Aminiya:
2025-09-17@21:51:02 GMT

An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna

Published: 9th, May 2025 GMT

Wata kotun majistare da ke titin Ibrahim Taiwo a Kaduna ta gurfanar da wasu mutane 10 da suka haɗa da kaka, bisa laifin yi wa wata yarinya ’yar shekara 16 fyaɗe a ƙauyen Likoro da ke ƙaramar hukumar Kudan ta jihar.

An ruwaito cewa wanda ake zargi mutum na 11 na hannu a lokacin da shari’ar ta taso, ranar Alhamis.

An zaɓi Robert Prevost sabon fafaroma Ficewar ’Yan Majalisa 3 a PDP: Raɗɗa ya halarci zauren Majalisar Wakilai

Waɗanda ake zargin, a cewar rahoton farko da aka samu, sun ce wacce aka yi wa fyaɗen an yi ta aikat fyaɗen a lokuta daban-daban ta hanyar yaudara da kuma lallashinta ta zuwa wurarensu daban-daban inda suke da masaniya game da ita.

Lamarin ya haifar da samun ciki kuma wadda aka yi fyaɗen ta haifi ɗa namiji watanni huɗu da suka wuce.

Ɗan sanda mai gabatar da ƙara, Insfekta Yakubu I. Lemu, ya ce matakin ya saɓawa sashe na 257 na kundin laifuffuka na Jihar Kaduna.

Ya ce, “A cewar rahoton farko da aka samu a ranar 27 ga watan Oktoba, 2024 da ƙarfe 6:30 na yamma, wani Usman Yusuf ya ruwaito cewa ya gano cewa ƙanwarsa Fatima Maikanti na ɗauke da juna biyu na wata shida, ya ce a lokacin da aka tambaye ta, ta bayyana cewa a wurare daban-daban, a lokuta daban-daban waɗanda ake zargin sun yi ta lalata da ita ne, sun kai ta wurare daban-daban a ƙauyen inda ta samu juna biyu, hakan ya sa ta haifi yaro.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fyade

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

Ya ce ya sayi layin wayar ne daga hannun wani Audu, ɗan kungiyar Vikings wanda ya tsere yanzu.

A wani lamari kuma, ‘yansanda sun kama wasu mutum huɗu da suka shiga gonar wani mutum a Lapai Gwari, inda suka saci kifi da darajar kuɗinsu ta kai Naira 750,000.

Babban wanda ake zargi, Hussaini Garba, ya amsa laifi tare da bayyana Ahmed Yusuf, Ibrahim Musa da Abdulazeez Bawa a matsayin mutanen da suke sayen kifin idan ya sato.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta