An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna
Published: 9th, May 2025 GMT
Wata kotun majistare da ke titin Ibrahim Taiwo a Kaduna ta gurfanar da wasu mutane 10 da suka haɗa da kaka, bisa laifin yi wa wata yarinya ’yar shekara 16 fyaɗe a ƙauyen Likoro da ke ƙaramar hukumar Kudan ta jihar.
An ruwaito cewa wanda ake zargi mutum na 11 na hannu a lokacin da shari’ar ta taso, ranar Alhamis.
Waɗanda ake zargin, a cewar rahoton farko da aka samu, sun ce wacce aka yi wa fyaɗen an yi ta aikat fyaɗen a lokuta daban-daban ta hanyar yaudara da kuma lallashinta ta zuwa wurarensu daban-daban inda suke da masaniya game da ita.
Lamarin ya haifar da samun ciki kuma wadda aka yi fyaɗen ta haifi ɗa namiji watanni huɗu da suka wuce.
Ɗan sanda mai gabatar da ƙara, Insfekta Yakubu I. Lemu, ya ce matakin ya saɓawa sashe na 257 na kundin laifuffuka na Jihar Kaduna.
Ya ce, “A cewar rahoton farko da aka samu a ranar 27 ga watan Oktoba, 2024 da ƙarfe 6:30 na yamma, wani Usman Yusuf ya ruwaito cewa ya gano cewa ƙanwarsa Fatima Maikanti na ɗauke da juna biyu na wata shida, ya ce a lokacin da aka tambaye ta, ta bayyana cewa a wurare daban-daban, a lokuta daban-daban waɗanda ake zargin sun yi ta lalata da ita ne, sun kai ta wurare daban-daban a ƙauyen inda ta samu juna biyu, hakan ya sa ta haifi yaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Fyade
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya A Filato
Tsohon ɗan takarar gwamna ƙarƙashin jam’iyyar CPC ta shuɗe a Jihar Kaduna, Alhaji Haruna Sa’eid Kajuru, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta gudanar da cikakken bincike kan kisan da aka yi wa wasu mazauna Zariya da suka je dauren aure a Jihar Filato kwanan nan.
Alhaji Kajuru ya yi wannan kira ne a lokacin da ya kai ziyara ta jaje ga iyalan waɗanda suka rasa ‘yan uwansu a Zaria, inda ya nuna alhini da ta’aziyya ga dangin waɗanda wannan al’amari ya shafa.
Tsohon Akanta Janar na Jihar Kaduna, Alhaji Haruna Kajuru, ya yi Allah-wadai da kisan, yana mai jaddada cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi na kashe wani ɗan ƙasa.
Ya ce dole ne a kama masu hannu a kisan kuma a gurfanar da su a gaban shari’a domin hakan ya zama izina ga sauran mutane.
“Kundin tsarin mulki bai amince da kisan wani ɗan ƙasa ba. Dole ne mu tsaya tsayin daka wajen ganin an tabbatar da doka da oda a kasa,” in ji shi.
Alhaji Haruna Sa’eid Kajuru, wanda shi ne tsohon ɗan takarar gwamna na CPC a Jihar Kaduna, ya kuma yi kira ga gwamnatocin tarayya da na Jihar Kaduna su tallafa wa iyalan da abin ya shafa, domin rage musu raɗaɗin rashin ‘yan uwa da masu ciyar da su.
Kazalika, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su ci gaba da zauna lafiya da juna, yana mai cewa zaman lafiya da haɗin kai su ne ginshiƙan ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’umma.
Kisan da aka yi a Jihar Filato ya janyo tashin hankali da kiraye-kiraye daga sassa daban-daban na ƙasa kan buƙatar ƙara tsaro da tabbatar da adalci a cikin al’ummomin da abin ya shafa.
Rel: Adamu Yusuf