Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kasim, ya bayyana cewa mutanen kasar Lebanon zasu ci gaba da gwagwarmaya da HKI wacce ta ke mamaye da wasu kasashen larabawan yankin har zuwa nasara.

Tashar talabijibn ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Sheik Kasim yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar ta kafar bidiyo a taron da aka fara gudanarwa a yau a makarantar Darushafia dake birnin Qom.

Taron na Qom yana Magana dangane da “Makarantun Hauza a Qum, Juyin juya halin musulunci a Iran da kuma Gwagwarmaya’.

Sheik Kasim ya kara da cewa mutanen kasar Lebanon sun fara gwagwarmaya ne bayan gwamnatin HKI ta mamaye kasarsu, sannan bayan sun sami jagoranci da tunanin Imam Khumaini (q) wanda ya kafa JMI. Yace tunanin Imam Khumaini Q ne ya taiamakawa mutanen kasar Lwabanon suka kai inada suka kai. Kuma alkawalin All…Gaskiya ce, nasara tana zuwa ga musulmin yankin da kuma duniya gaba daya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Bukaci Kasashen Turai Su Shiga Tattaunawar Nukliya Da Take Yi Da Amurka

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaaei ya bukaci kasashen turai da su shiga a dama da su kan tattaunawa dangane da shirin nukliyar kasar Iran na zaman lafiya. Ya kuma jaddada cewa Iran tana turjiya ga dukkan tunanin Amurka na wargaza shirin Nukliyar kasar Iran kwata-kwata.

Baghaei ya kara da cewa duk da cewa Iran a shirye take a ci gaba da tattaunawa kan shirin makamashin nukliyar kasar, da sake farfado da yarjeniyar JCPOA ta shekara ta 2015 amma kuma ba zata taba barin hakkinta na mallakar fasahar nukliya da luma sarrafashi a hanyoyin da yarjeniyar NPT ta amince da su ba.

Kuma da alamun tattaunawar tsakanin Amurka da Iran ya daki dutse, saboda sun sami sabani a kan wasu al-amura wadanda basu shafi Nukliya ba, don haka ne aka fasa taron roma wanda yakamata a gudanar a ranar asabar da ta gabata. Batun cewa Mike Waltz mai bawa shugaban kasar Amurka shawara kan tsaro yana son cusawa gwamnatin Amurka ra’ayin Benyamin Natanyahu firai ministan HKI a tattaunawar Amurka da Iran, ya ce, wannan al-amari ne na cikin gida ga gwamnatin Amurka, amma abinda ya shafi Iran shi ne menene Amurka zata gabatar a kan teburin tattaunawa da ita.

Don haka ne Iran take bukatar kasashen Turai su shigo a dama da su a cikin wannan tattaunawar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasara A Yakin Duniya Na Biyu
  • Hukumar Alhazan Jigawa Ta Shirya Taro da Shugabannin Alhazai na Kananan Hukumomi
  • Iran Ta Yi Tsokaci Kan Jita-Jitar Da Ake Yadawa Cewa: Shugaban Kasar Iran Zai Gana Da Shugaban Amurka
  • Gwamnatin Siriya Tana Neman Tattaunawa Da Gwamnatin Mamayar Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-hassam Al-Mujtaba (a) 119
  • Kungiyar Ansarullahi Ta Yemen Ta Sanar Da Cewa Ayyukan Yemen Na Tallafawa Gaza Ba Zai Tsayawa Ba
  • Iran Ta Bukaci Kasashen Turai Su Shiga Tattaunawar Nukliya Da Take Yi Da Amurka
  • NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya?
  • NAJERIYA A YAU: Me Yake Kai ‘Yan Gwagwarmaya Shiga Tasku A Najeriya?