Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Taron Musayar Al’adu Tsakanin Sin Da Rasha
Published: 8th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Sin, Xi Jinping ya aike da wasikar taya murna ga taron musayar al’adu da cudanyar al’umma da aka shirya domin murnar cika shekaru 80 da samun nasarar yakin turjiya da jama’ar kasar Sin suka yi a kan zaluncin Japan da kuma kazamin yakin ceton kasa na tsohuwar tarayyar Soviet.
A cikin sakon nasa, Xi ya yi nuni da cewa, shekaru 80 da suka gabata, al’ummomin kasar Sin da na kasar Rasha sun bayar da gudummawa mai tarihi da ba za a taba mantawa da ita ba wajen samun nasarar yaki da zaluncin danniya a duniya, tare da kulla kakkarfar alaka da ba za a iya kassarawa ba ta hanyar sadaukar da jini, wadda ta kafa tubulin raya dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu a matakin koli.
Ya kara da cewa, a yau, bayan shekaru 80 da afkuwar hakan, sakamakon kokarin hadin gwiwa, dangantakar da ke tsakanin Sin da Rasha na kara habaka tare da sabon kuzari, inda ta zama wani sabon nau’in zumuncin kasa da kasa abin koyi a tsakanin manyan kasashe.
Shugaban na kasar Sin ya kuma bayyana cewa, yana fatan kafofin watsa labaru na kasashen biyu za su hada karfi da karfe don ci gaba da yin aiki tare a bisa manufa guda, da gudanar da kasaitacciyar musayar al’adu da cudanyar jama’a da ke hade zukatan al’umma wuri guda, ta yadda za a kara matsa kaimi ga karfafa fahimtar juna da kauna da zumunci a tsakanin jama’ar kasashen biyu, da kara inganta cikakkiyar dangantakar Sin da Rasha ta fuskar tsare-tsaren ci gaba a sabon zamani, da bayar da sabbin dimbin gudummawa ga gina al’umma mai makoma guda ga daukacin bil’adama. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Tabbatar Da Adalci Ga Falasdinawa Wajen Maido Da Hakkinsu Na Kasa
Dangane da halin da ake ciki game da rikicin Falasdinu da Isra’ila, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana a yau Litinin 22 ga wata cewa, karfin soja ba zai iya samar da zaman lafiya ba, kuma tashin hankali ba zai iya samar da tsaro ba. Kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da kasashen duniya wajen ci gaba da jajircewa a kan tsagaita bude wuta da kawo karshen yakin da ake yi a zirin Gaza, da kuma matukar nuna goyon baya ga tabbatar da adalci ga al’ummar Falasdinawa wajen maido da hakkinsu na kasa, da kuma kara azamar warware matsalar Falasdinu tun da wuri ta hanyar samar da cikakkiyar mafita, mai adalci da kuma dorewa.
Guo Jiakun ya ce, kawo karshen rikicin cikin hanzari da samar da dawwamammen zaman lafiya, shi ne babban burin al’ummar Falasdinu da Isra’ila da kuma yankin Gabas ta Tsakiya, kuma wannan aiki ne na gaggawa da ke gaban kasashen duniya. Kasar Sin ta yi imanin cewa, a halin da ake ciki yanzu, ya zama tilas a karfafa tsagaita bude wuta a zirin Gaza, tare da daukar matakin gaggawa domin rage radadin bala’in jin kai a yankin.
Ya ci gaba da cewa, ya kamata kasashen da ke da tasiri na musamman a kan Isra’ila su sauke nauyin da ke wuyansu. Dole ne a aiwatar da ka’idar barin “Falasdinawa su mulki Falasdinu” bisa turbar gaskiya, kuma dole ne a kiyaye hakkin kasar Falasdinu kan batutuwan da suka shafi shugabanci bayan yaki da kuma shirye-shiryen sake gina kasar. Kazalika, a cewarsa, dole ne a ci gaba da bibiyar shawarar “kafa kasashe biyu” ba tare da kakkautawa ba, da samar da karin fahimtar juna da cimma matsaya tsakanin kasa da kasa da kuma yin watsi da duk wani mataki na bangare guda da zai iya yin kafar ungulu a kan “kafuwar kasashe biyu”. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp