Sojoji sun kama mutum 4 kan zargin ta’addanci a Taraba
Published: 8th, May 2025 GMT
Dakarun Birget na 6 na Sojin Najeriya da ke Jalingo Jihar Taraba sun cafke wasu mutane huɗu da ake zargin cewa ’yan ta’adda ne.
Kama waɗanda ake zargin ya biyo bayan wani samame da sojojin suka gudanar a ranar 7 ga Mayu, 2025 a Ƙaramar Hukumar Arɗo-Kola da ke jihar.
Kakakin Rundunar, Kyaftin Oni Olubodunde, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a garin Jalingo.
Ya bayyana cewa rundunar ta sami kiran gaggawa dangane da shigowar wasu mutane ɗauke da makamai a yankin.
’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — ZulumKyaftin Oni ya ƙara da cewa dakarun sun yi gaggawar kai ɗauki wurin, inda hakan ya kai ga kama mutanen huɗu, uku daga cikinsu na rike da makamai.
Ya ce makaman da aka ƙwato daga hannunsu sun haɗa da bindigogi uku, adduna guda 3, alburusai guda 42, wayoyin hannu guda 4 da katin shaidar ƙasa guda 1.
Binciken farko ya nuna cewa ana zargin wani mai mutum da kiran wadannan mutanen zuwa yankin, kuma ana ci gaba da bincike kan rawar da ya taka a lamarin.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu, sun sace mutum 8 a Kwara
’Yan bindiga sun kai hari wasu ƙauyuka na Patigi a Jihar Kwara, inda suka kashe wata mata mai juna biyu tare da wasu mutane.
Haka kuma sun yi garkuwa da mutane takwas tare da jikkata da dama.
Mawaki Davido ya ba matarsa kyautar motar miliyan 240 Tarihi da rayuwar Sheikh Abdulaziz Al-Sheikh (1943-2025)Shaidu sun ce maharan sun shiga ƙauyukan ne a babura, inda suka dinga harbi ba ƙaƙƙautawa wanda ya sa mazauna ƙauyukan suka gudu.
Ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Motokun, Egboro da Fanagun.
Wani mai suna James Ibrahim, ya ce: “Mun farka da safe muka ga mutane suna gudu daga Motokun bayan harin. An harbi wata mace wadda daga bisani ta rasu a asibitin Patigi.
“Sun kuma sace mutum takwas tare da yin awon gaba da babura da dama. Muna roƙon gwamnati ta taimake mu.”
Wani shugaban al’umma, Malam Mohammed, ya ƙara da cewa: “’Yan bindigar sun fara kai hari Motokun, daga nan suka nufi Egboro. Yawancin mazauna ƙauyukan sun tsere.
“Sun kashe wani malami da ya saba zuwa yin wa’azi, sannan suka sace mutanen da suke ganin za su iya karbar fansa a hannunsu.”
Harin ya tilasta wa magidanta da dama barin gidajensu, inda suka nemi mafaka a garuruwan da ke kusa da su.
Mazauna ƙauyukan sun ce suna rayuwa cikin tsoro saboda hare-haren da ke ƙara yawaita kullum.
Gwamnatin Jihar Kwara, ta yi alƙawarin ƙara tsaurara tsaro tare da buƙatar al’umma su fallasa masu bai wa ’yan bindiga bayanai.
Rundunar sa-kai da sojoji kuma sun ƙara tsaurara tsaro, duk da cewa jama’a sun koka cewa sau da yawa maharan na kai farmaki kafin a kai musu agaji.