Aminiya:
2025-05-08@16:20:04 GMT

Sojoji sun kama mutum 4 kan zargin ta’addanci a Taraba

Published: 8th, May 2025 GMT

Dakarun Birget na 6 na Sojin Najeriya da ke Jalingo Jihar Taraba sun cafke wasu mutane huɗu da ake zargin cewa ’yan ta’adda ne.

Kama waɗanda ake zargin ya biyo bayan wani samame da sojojin  suka gudanar a ranar 7 ga Mayu, 2025 a Ƙaramar Hukumar Arɗo-Kola da ke jihar.

Kakakin Rundunar, Kyaftin Oni Olubodunde, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a garin Jalingo.

Ya bayyana cewa rundunar ta sami kiran gaggawa dangane da shigowar wasu mutane ɗauke da makamai a yankin.

’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum

Kyaftin Oni ya ƙara da cewa dakarun sun yi gaggawar kai ɗauki wurin, inda hakan ya kai ga kama mutanen huɗu, uku daga cikinsu na rike da makamai.

Ya ce makaman da aka ƙwato daga hannunsu sun haɗa da bindigogi uku, adduna guda 3, alburusai guda 42, wayoyin hannu guda 4 da katin shaidar ƙasa guda 1.

Binciken farko ya nuna cewa ana zargin wani mai mutum da kiran wadannan mutanen zuwa yankin, kuma ana ci gaba da bincike kan rawar da ya taka a lamarin.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan fashi sun kashe magidanci a Kano

Ana fargabar cewa wasu da ake zargin ’yan fashi ne sun kashe wani magidanci a  unguwar Ɗanbare da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano.

Bayanai sun ce waɗanda ake zargin sun kashe magidancin ne da adda, bayan sun shiga gidansa da yake zaune domin sata da asuba.

To sai dai mazauna unguwar sun bayyana wa Aminiya cewa sun samu nasarar kama wanda suke zargin shugaban ’yan fashin ne, sun kuma miƙa shi ofishin ’yan sanda na Ɗorayi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama mutum 6 da ake zargi kan garkuwa da mutane
  • A yi amfani da fasahar zamani don yaƙar ta’addanci – Ganduje
  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 4, Sun Kwato Makamai A Taraba
  • An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
  • Matashi ya kashe mahaifinsa da adda a Jigawa
  • EFCC Ta Kama Matashi A Kaduna Bisa Zargin Wulaƙanta Naira A Bidiyon Barkwanci
  • Wata mata ta auri maza biyu a lokaci guda a Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa
  • ’Yan fashi sun kashe magidanci a Kano