Aminiya:
2025-08-07@13:22:57 GMT

Sojoji sun kama mutum 4 kan zargin ta’addanci a Taraba

Published: 8th, May 2025 GMT

Dakarun Birget na 6 na Sojin Najeriya da ke Jalingo Jihar Taraba sun cafke wasu mutane huɗu da ake zargin cewa ’yan ta’adda ne.

Kama waɗanda ake zargin ya biyo bayan wani samame da sojojin  suka gudanar a ranar 7 ga Mayu, 2025 a Ƙaramar Hukumar Arɗo-Kola da ke jihar.

Kakakin Rundunar, Kyaftin Oni Olubodunde, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a garin Jalingo.

Ya bayyana cewa rundunar ta sami kiran gaggawa dangane da shigowar wasu mutane ɗauke da makamai a yankin.

’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum

Kyaftin Oni ya ƙara da cewa dakarun sun yi gaggawar kai ɗauki wurin, inda hakan ya kai ga kama mutanen huɗu, uku daga cikinsu na rike da makamai.

Ya ce makaman da aka ƙwato daga hannunsu sun haɗa da bindigogi uku, adduna guda 3, alburusai guda 42, wayoyin hannu guda 4 da katin shaidar ƙasa guda 1.

Binciken farko ya nuna cewa ana zargin wani mai mutum da kiran wadannan mutanen zuwa yankin, kuma ana ci gaba da bincike kan rawar da ya taka a lamarin.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa

Dakarun sojin Nijeriya sun hallaka aƙalla ’yan ta’adda 17 na ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP a wasu hare-haren kwantan bauna da suka kai a jihohin Borno da Adamawa a tsakanin ranakun 23 ga Yuli zuwa 2 ga Agustan 2025.

Kyaftin Reuben Kovangiya, Daraktan Yaɗa Labarai na Rundunar Sojin Kasa ta Nijeriya, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniya An soka wa jami’in Sibil Difens wuka har lahira a Jigawa

Ya bayyana cewa sojojin ƙarƙashin rundunar Operation Hadin Kai sun kai hare-haren ne a ƙananan hukumomin Bama, Konduga, Gwoza, Magumeri, da Biu a Jihar Borno, da kuma Michika da ke Jihar Adamawa.

A cewarsa, an kuma gano ababen fashewa 14 da ’yan ta’addan suka dasa a wurare daban-daban wadanda dakarun suka samu nasarar tarwatsa su.

“Ayyukan sun haifar da gagarumar nasara ga rundunar, inda muka hallaka mayaƙan, kuma muka ƙwato makamai da kayan yaƙi daban-daban da suke amfani da su wajen kai hare-hare,” in ji Kyaftin Kovangiya.

Kyaftin Kovangiya ya ce wannan nasara na zuwa ne bayan bincike da leƙen asiri da aka gudanar tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro da sauran hukumomin ƙasa.

Ko da yake ana samun ci gaba a fagen yaki da ta’addanci a Arewa maso Gabas, amma har yanzu matsalar tsaro na ci gaba da addabar sassan ƙasar, musamman a jihohin Zamfara, Katsina da wasu yankunan Borno, inda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da kai hare-hare kan fararen hula da dakarun.

Rahotanni sun nuna cewa, hare-haren ‘yan ta’adda na haifar da ƙalubale ga abinci da zaman lafiyar jama’a, musamman ga manoma da ke fuskantar barazanar kisa ko biyan haraji kafin su iya zuwa gonakinsu.

A wasu yankunan, ’yan bindiga na tilasta wa mutane biyan kuɗin kafin su shiga gona, lamarin da ke hana dubun dubatar fararen hula gudanar da harkokin noma, wanda hakan na ƙara tsananta matsin tattalin arziki da yunwa a yankunan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama bama-baman da aka boye a cikin kayan gwangwan a Kaduna
  • Mutanen Kasar Lebanon Suna Tsoron HKI Zata Shiga Kasar Daga Kasar Siriya
  • Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
  • Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Taraba
  • Ambaliya ta lalata kauyuka 3 a Sakkwato
  • Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
  • Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a Katsina
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa
  • An Zargin Akantan jihar Nasarawa Da Shiga Harkokin Siyasa