Hukumar jindadin Alhazai ta jihar jigawa ta gudanar da taro da shugabanin shiyya shiyya da kuma jami’an alhazai na kananan Hukumomi Jihar 27 a shelkwatar hukumar dake Dutse gabannin fara jigailar maniyatan aikin hajjin bana.

A lokacin da yake jawabi, Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmed Umar labbo ya ce taron yana da muhimmanci kasancewar aiki yayi nisa na fara jigilar maniyata zuwa kasa mai tsarki.

Yana mai cewar, hukumar ta kammala duk wani shiri ga maniyyata domin fara jigilar su zuwa kasa mai tsarki.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar, a lokacin taron da suka gudanar da jami’an sun rabawa shugabanin shiyya-shiyya da jami’an su dukkanin kayayyakin maniyyata da dukkan sauran muhimman abubuwa daya dace.

Game da batun biza kuwa, Labbo yace an kammala yiwa maniyatan biza wadda daga yanzu zuwa kowane lokaci za’a sanar da maniyyatan zuwa sansanin alhazai domin jigilar su zuwa kasa mai tsarki.

A sabili da haka nema, Ahmed Labbo ya bukaci shugabanin shiyya-shiyya da suyi takatsantsan da kayayyakin maniyyata saboda mahimmacin sa.

Darekta Janar na hukumar, ya kuma godewa gwamnatin Jihar bisa tanadin dukkanin Muhimman abubuwa da suka kamata a filin jirgin saman kasa da kasa na Muhammadu Sunusi dake birnin Dutse domin fara jigailar maniyyatan a dan kankanin lokaci.

Kazalika, yace Gwamna Umar Namadi yasha alwashin ci gaba da kyautata jin dadin maniyyatan bana tun daga nan gida Najejriya har zuwa kasa Mai tsarki.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taro zuwa kasa mai tsarki

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Gamsu da Gudanar da Aikin Tantance ‘Yan Fansho

 

Karamar Hukumar Birnin Kudu ta nuna gamsuwa da yadda aikin tantance yan fansho ya gudana a yankin.

Shugaban Karamar Hukumar, Dr Builder Muhammed Uba ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin jami’an gudanar da aikin tantance yan fanshon jim kadan da kammala aikin a sakatariyar Karamar hukumar.

Yace karamar hukumar ta gamsu matuka bisa yadda aikin ya gudana cikin kyakkyawan tsari mafi dacewa.

Alhaji Builder Muhammad Uba ya kuma yabawa hukumar asusun adashen gata na fansho kan yadda take biyan hakkokin ma’aikatan da suka yi ritaya akan lokaci ta hanyar basu hakkokin su.

Shima a nasa jawabin, Daraktan kudi da mulki na karamar hukumar, Malam Haruna Ibrahim Kwaimawa ya godewa Karamar Hukumar bisa karamci data nuna a lokacin aikin tantancewar tare da godewa yan fanshon yankin bisa hadin kai da suka bayar a lokacin aikin.

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ya Ce Gwagwarmaya Zata Ci Gaba Har Zuwa Nasara
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Gamsu da Gudanar da Aikin Tantance ‘Yan Fansho
  • An Fara Gabatar Da Shirin “Kalaman Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Rasha
  • Ma’aikatar Yaɗa Labarai Ta Fara Bitar Ayyuka Na Tsakiyar Wa’adi
  • An Tabbatar Da Ficewar Sanata Sumaila Daga NNPP Zuwa APC A Majalisa
  • Jigawa Ta Kaddamar Da Kwamitin Likitocin Da Su Duba Lafiyar Mahajjatan Bana A Saudiyya
  • An kashe mutum 6 a sabon hari a Filato
  • Hajj 2025: Maniyyatan Kaduna za su fara tashi ranar 14 ga watan Mayu
  • Aikin Hajjin 2025 Ya Fara A Hukumance Yayin Da Tawagar NAHCON Ta Musamman Ta Tashi Zuwa Makkah