Hukumar jindadin Alhazai ta jihar jigawa ta gudanar da taro da shugabanin shiyya shiyya da kuma jami’an alhazai na kananan Hukumomi Jihar 27 a shelkwatar hukumar dake Dutse gabannin fara jigailar maniyatan aikin hajjin bana.

A lokacin da yake jawabi, Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmed Umar labbo ya ce taron yana da muhimmanci kasancewar aiki yayi nisa na fara jigilar maniyata zuwa kasa mai tsarki.

Yana mai cewar, hukumar ta kammala duk wani shiri ga maniyyata domin fara jigilar su zuwa kasa mai tsarki.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar, a lokacin taron da suka gudanar da jami’an sun rabawa shugabanin shiyya-shiyya da jami’an su dukkanin kayayyakin maniyyata da dukkan sauran muhimman abubuwa daya dace.

Game da batun biza kuwa, Labbo yace an kammala yiwa maniyatan biza wadda daga yanzu zuwa kowane lokaci za’a sanar da maniyyatan zuwa sansanin alhazai domin jigilar su zuwa kasa mai tsarki.

A sabili da haka nema, Ahmed Labbo ya bukaci shugabanin shiyya-shiyya da suyi takatsantsan da kayayyakin maniyyata saboda mahimmacin sa.

Darekta Janar na hukumar, ya kuma godewa gwamnatin Jihar bisa tanadin dukkanin Muhimman abubuwa da suka kamata a filin jirgin saman kasa da kasa na Muhammadu Sunusi dake birnin Dutse domin fara jigailar maniyyatan a dan kankanin lokaci.

Kazalika, yace Gwamna Umar Namadi yasha alwashin ci gaba da kyautata jin dadin maniyyatan bana tun daga nan gida Najejriya har zuwa kasa Mai tsarki.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taro zuwa kasa mai tsarki

এছাড়াও পড়ুন:

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tattalin Arziki Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho November 7, 2025 Tattalin Arziki Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria October 25, 2025 Tattalin Arziki Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life October 25, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar Trump: Ya kamata shugabannin Najeriya su farka daga bacci — Bishop Kukah
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock
  • Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026
  • A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu
  • Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho