Hukumar jindadin Alhazai ta jihar jigawa ta gudanar da taro da shugabanin shiyya shiyya da kuma jami’an alhazai na kananan Hukumomi Jihar 27 a shelkwatar hukumar dake Dutse gabannin fara jigailar maniyatan aikin hajjin bana.

A lokacin da yake jawabi, Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmed Umar labbo ya ce taron yana da muhimmanci kasancewar aiki yayi nisa na fara jigilar maniyata zuwa kasa mai tsarki.

Yana mai cewar, hukumar ta kammala duk wani shiri ga maniyyata domin fara jigilar su zuwa kasa mai tsarki.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kara da cewar, a lokacin taron da suka gudanar da jami’an sun rabawa shugabanin shiyya-shiyya da jami’an su dukkanin kayayyakin maniyyata da dukkan sauran muhimman abubuwa daya dace.

Game da batun biza kuwa, Labbo yace an kammala yiwa maniyatan biza wadda daga yanzu zuwa kowane lokaci za’a sanar da maniyyatan zuwa sansanin alhazai domin jigilar su zuwa kasa mai tsarki.

A sabili da haka nema, Ahmed Labbo ya bukaci shugabanin shiyya-shiyya da suyi takatsantsan da kayayyakin maniyyata saboda mahimmacin sa.

Darekta Janar na hukumar, ya kuma godewa gwamnatin Jihar bisa tanadin dukkanin Muhimman abubuwa da suka kamata a filin jirgin saman kasa da kasa na Muhammadu Sunusi dake birnin Dutse domin fara jigailar maniyyatan a dan kankanin lokaci.

Kazalika, yace Gwamna Umar Namadi yasha alwashin ci gaba da kyautata jin dadin maniyyatan bana tun daga nan gida Najejriya har zuwa kasa Mai tsarki.

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taro zuwa kasa mai tsarki

এছাড়াও পড়ুন:

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

Daga ranar 18 zuwa 21 ga watan nan bisa agogon Rasha, an gudanar da dandalin tattaunawa tattalin arziki na kasa da kasa na St. Petersburg karo na 28 a kasar ta Rasha. Yayin taron, an sake gayyatar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG don halartar dandalin a matsayin abokin huldar yada labarai.

CMG, ya gina wani wurin baje koli mai zaman kansa a cikin wurin taron, da kafa dakin nuna shirye-shirye, da yin hira da manyan baki, kuma ya ba da rahotanni game da dandalin a cikin harsuna da yawa.

Ban da wannan kuma, a yankin baje kolin, an nuna sabon sakamakon aikace-aikacen fasahohin zamani na AI, wanda CMG ya yi nazari da kansa, da gabatar da shirye-shiryen CMG masu inganci da kuma kayayyakin al’adun kasa da kasa da ya kera da kansa, ya kuma jawo hankulan baki ‘yan siyasa da ’yan kasuwa da wakilan kafofin watsa labaru na kasashe daban-daban da suka halarci dandalin, inda suka tsaya tare da ziyartar dakin da ya kafa.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 2 sun mutu a ƙoƙarin ciro waya daga masai a Kano
  • Mutum 2 sun mutum a ƙoƙarin ciro wata daga masai a Kano
  • Hajji 2025: Kashi Na Farko Na Alhazan Abuja Sun Dawo Gida Nijeriya
  • CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 
  • Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
  • Ɗan ƙunar baƙin wake ya kashe mutum 10 da bam a Borno
  • Duk Da Jihohin Nijeriya Sun Fara Biyan Mafi Ƙarancin Albashi Na 70,000, Ana Ci Gaba Da Fuskantar Matsin Rayuwa
  • Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya