Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Gamsu da Gudanar da Aikin Tantance ‘Yan Fansho
Published: 8th, May 2025 GMT
Karamar Hukumar Birnin Kudu ta nuna gamsuwa da yadda aikin tantance yan fansho ya gudana a yankin.
Shugaban Karamar Hukumar, Dr Builder Muhammed Uba ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin jami’an gudanar da aikin tantance yan fanshon jim kadan da kammala aikin a sakatariyar Karamar hukumar.
Yace karamar hukumar ta gamsu matuka bisa yadda aikin ya gudana cikin kyakkyawan tsari mafi dacewa.
Alhaji Builder Muhammad Uba ya kuma yabawa hukumar asusun adashen gata na fansho kan yadda take biyan hakkokin ma’aikatan da suka yi ritaya akan lokaci ta hanyar basu hakkokin su.
Shima a nasa jawabin, Daraktan kudi da mulki na karamar hukumar, Malam Haruna Ibrahim Kwaimawa ya godewa Karamar Hukumar bisa karamci data nuna a lokacin aikin tantancewar tare da godewa yan fanshon yankin bisa hadin kai da suka bayar a lokacin aikin.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Yan Fansho
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasara A Yakin Duniya Na Biyu
Shugaban kasar Rasha Vladimit Putin ta tokwaransa na kasar China Xi Jinping sun tattauna a birnin Mosco a yau Alhamis, inda kasashen biyu suka kara dankon zuminci a tsakaninsu, da fatan zasu bukasa harkokin kasuwanci da ci gaba a tsakaninsu nan da shekara ta 2030.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa shugaba Xi Jinping ya je birnin Mosco ne don halattan bikin nasara da kasar Rasha ta samu kan sojojin Nazi a yankin duniya na biyu shekaru 80 da suka gabata.
Haduwar shugabannin kasashen biyu yana zuwa ne a dai-dai lojkacinda ake kara tada jijiyoyin wuta tsakanin su da kasashen yamma musamman Amurka.
Shuwagabannin biyu sun kara jaddada manufar su da samar da duniya mai kudubobi daban daban ba kasar Amurka kadai zata jujjuya duniyar kamar yadda ta ga dama ba.