Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayana labarummu na yau zai yi magana dangane da ‘Mahangar Jumhuriyar Musulunci na Iran ta yadda za’a kai ga fahintar juna a tattaunawanta da kasar Amurka da suke yi wanda ni tahir amin zan karanta.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi a wata tattaunawa ta wayar tarho da tokwaransa na kungiyar tarayyar turai wato Kaja Kallas, ya bayyana mata yadda bangarorin Amurka da Iran za su kai ga cimma yarjeniya dangane da shirin makamashin nukliya na kasarsa.

Ministan ya kara da cewa tun kimani shekaru 20 da suka gabata ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran bangaren tattaunawa dangane da shirin nukliyar kasar ta zaman lafiya. Kuma batun shirin nukliyar kasar Iran tana daga cikin ayyuka masu muhimmanci wadanda ma’aikatar harkokin wajen ta aiwatar a cikin wannan lokacin.

Kasashen ya mamma karkashin jagorancin Amurka suka dorawa kasar Iran takumkuman tattalin arziki masu yawa, saboda hana JMI amfani da hakkinta na amfani da fasahar makamashin nukliya, da sunan wai iran tana shirin gina makaman Nukliya.

Don biyan wannan bukatarsu wadannan azzaluman kasashe suka sanya mafi yawan mutanen kasar Iran cikin matsaloli na rayuwa daban-daban. Amma jami’an gwamnatin JMI  don tabbatarwa duniya da kuma wadannan kasashe kan cewa ba ta da wani shiri na mallakar makaman nukliya, ta bude tattaunawa da wadannan kasashe na tsawon shekaru biyu, har sai da bangarorin biyu daga ciki har da Amutka, suka cimma yarjeniya ta ganin JMI ta amfana da fasaha da kuma makamashin nukliya wanda yarjenyar NPT ta amincewa ko wace kasa a duniya ta yi amfani da shi. Wannan ya kaiga samar da yarjeniyar JCPOA a shekara 2015.  

Inda JMI ta aiwatar da dukkan alkawulan da ta dauka a cikin yarjeniyar. Banda haka hukumar makamashin nukliya ta duniya IAEA ta bada rahoto har 16 kan cewa shirin makamashin nukliya na kasar Iran bai karkata daga yarjeniyar JCPOA ba,

Ana cikin wannan halin ne sai shugaban kasar Amurka mai ci ya hau kan kujerar shugabancin kasar Amurka, ya kuma fidda Amurka daga cikin yarjeniyar a shekara ta 2018, tare da dalilin cewa yarjeniyar bata yi masa ba.

Sai dai a dole JMI ta sake dawowa kan teburin tattaunawa dangane da shirin ta na makamashin nukliya. Sannan ta kara yawan takunkuman tattalin arzikin da ta dorawa JMI, don tursasa mata ta yi abinda take bukata. Banda haka ta sha alwashin sai ta maida cikinin danyen man fetur na JMI a kasuwar duniya ya zama sifir.

Amma bukatar kasar Amurka a lokacin bata ga rana ba har wata gwamnati ta maye gurbinta, sannan a dayan bangaren kasashen turai wadanda tare da su aka kulla yarjeniyar JCPOA a shekara ta 2015 suma sun saba alkawalunsu a wannan yarjeniyar suka ci gaba da dorawa JMI takunkuman tattalin arziki ba iyaka. Wadanda duk wanda ya nazarcesu zai fahinci cewa suna son faduwar gwamnatin JMI ne. Amma har yanzun basu ga hakan ya auku ba. Kuma da yardar All…ba zasu taba gani ba.

Don haka bayan ficewar Trump daga yarjeniytar JCPOA da kuma sabawa sauran kasashen Turai alkawulan da suka dauka a yarjeniyar,  yarjeniyar ta zama babu wani amfani da JMI.

Amma bayan da Donal Trump ya sake komawa Fadar white House a farkon wanan shekara ta 2025 ya sake da ta wannan maganar sannan ya farfado da dukkan takunkuman tattalin arzikin da ya dorawa JMI a shugabancinsa na farko sannan yana kara wasu, daga lokaci zuwa lokaci. A wannan karon har da baraza na farwa kasar da yaki idan ta ki amincewa da sake tattauna shirin nukliyar kasar.

Ganin cewa JMI ta san cewa Amurka musamman Donal Trump ba mai cika alkawali ne ba, sai ta zabi tattaunawa ba kai tsaye ba da ita, saboda yaki zabi ne na karshe.

Don haka aka gudanar da zagaye na farko na tattaunawar a ranar 5 ga watan Afrilun da ya gabata a birnin Mascat na kasar Omman, sannan zagaye na biyu da na uku a ranar 12 da kuma 19 na watan Afrilu a biranen Roma da maskat, amma sai aka dage zaman a 4, wanda yaka mata a gudanar da ita a ranar 26 ga watan a birnin Roma.

Amma dan dan tsakanin nan sai muka fara jin maganganu daga jami’an gwamnatin kasar Amurka na cewa manufarsu ita ce hana JMI sarrafa makamashin nukliya kwatw-kwata, al-hali a zaman tattaunawa guda uku da aka gudanar Amuka bata kawo wannan batun ba. Amma an ji Trump da sakataren harkokin wajensa Rubio suna maganar hana JMI mu’amala da makamashin nukaliya kwata-kwata ne.

Sai dai wannan ketare jan layi ne, ga JMI, don ba zata taba amincewa da hakan ba, ko da za ta ga shiga yaki ne da wadannan kasashe.

Sayyid Abbas Aragchi ya fadawa Kajal Kallas jami’a mai kula da al-amuran harkokin waje na tarayyar Turai kan cewa bangarorin biyu zasu kai ga fahintar juna ne kawai idan dayan baranagren bai gabatar da wani abu wanda ya tabbatar da dayan bangaren ba zai taba amincewa ba. Ko kuma wani abu wanda ba zai taba yiyuwa ba.

Ya kammala da cewa Iran tana da tarjuba na saba alkalin Amurka, don haka idan ta kuskra da shigar da wani abu wanda ta san cewa JMI ba zata amince ba, ba inda tattaunawar zai je.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: makamashin nukliya kasar Amurka a yarjeniyar

এছাড়াও পড়ুন:

2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’

Fadar Shugaban Kasa ta ce shugaba Bola Tinubu zai zabi wanda zai yi masa takarar mataimaki a zaben 2027 a hukumance ne kawai bayan a kammala babban taron jam’iyyar APC a 2026.

Kakakin shugaban, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawarsa da jaridar Daily Trust a ranar Alhamis.

Da yake martani kan dalilin da ya sa fadar shugaban ta yi shiru kan zargin cewa Tinubu na son canza mataimaki a 2027 musamman la’akari da yadda ’yan jam’iyyar ke ta nuna goyon bayansu ga shugaban shi kadai, Onanuga ya ce hakan ba gaskiya ba ne.

Nan da mako biyu za mu yanke shawara kan shigar wa Isra’ila yaƙi — Trump Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya

A cewarsa, “Lokacin da na karanta labarin, na karyata shi saboda ba shi da tushe. A tsarin shugaba mai cikakken iko da Najeriya ke bi, dan takarar shugaban kasa ake fara zaba, shi kuma sai ya zabi wanda zai yi masa mataimaki. Abin da ya faru ke nan a lokacin Buhari – an fara zabensa, sai daga baya shi kuma ya dauki mataimaki. Ba a yin duka biyun a lokaci daya.

“Da zarar INEC ta fitar da jadawalin zabuka, jam’iyya za ta shirya babban taronta, idan aka sake tsayar da shugaban kasa, shi kuma zai zabi mataimakinsa,” in ji Onanuga.

Kazalika, ya kuma yi fatali da tarihin da ake daukowa cewa sau biyu tinubu yana canza mataimaka lokacin da ya yi Gwamna a jihar Legas daga 1999 zuwa 2007, cewa irin haka za ta faru da Kashim Shettima a 2027.

Ya kuma ce jita-jitar da ake yadawa a kan yiwuwar canza Shettima tun ma kafin a fara nuna amincewa da sake takarar Tinubu ba ta da tushe.

Ya ce, “Ba ni da masaniya a kan duk wani sabani tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa. Iya abin da na sani shi ne akwai kyakkyawar fahimtar juna da alakar aiki mai kyau a tsakaninsu. Duk maganganun da ake yadawa ba su da maraba da na teburin mai shayi. Mutane na ta fadara maganganun rashin kan gado cewa wai Seyi Tinubu ne ma mataimakin shugaban kasa. Wannan shashanci ne.

“A wannan kasar, mukamin mataimaka ko na gwamna ko na shugaban kasa ba a raba su da ’yan tsegungumin mutane. Ko da ana zaune lafiya babu wata matsala, makunsantansu sai sun kirkiri husuma da labaran karya. Amma iya abin da na sani shi ne babu matsala tsakanin Tinubu da Shettima.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi
  • Sin Ta Yi Matukar Allah Wadai Da Hare-Haren Da Amurka Ta Kaiwa Iran
  • Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
  • Amurka ta ƙaddamar da hare-hare kan Iran
  • ’Yan Najeriya da suka maƙale a Isra’ila na neman ɗauki
  • Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia
  • Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka
  • Yin sulhu da ’yan bindiga dabara ce ba gazawa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Katolika ta horar da shugabannin al’umma da na addini kan zaman lafiya
  • 2027: ‘Sai bayan babban taron APC Tinubu zai bayyana wanda za su yi takara tare’