HausaTv:
2025-07-26@03:28:53 GMT

Kasar Sudan Ta Yanke Huldar Jakadancinta Da Kasar Hadaddiyar Daular Larabawa

Published: 7th, May 2025 GMT

Kasar Sudan ta yanke huldar jakadancinta da kasar Hadaddiyar Daulart Larabawa tana mai ayyana UAE a matsayin ‘kasa mai cin zali’

Kamfanin dillancin labaran Sudan (SUNA) ya watsa rahoton cewa: Kwamitin tsaro da kula da matakan tsaron kasar Sudan ya sanar a cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Talata cewa: Sudan ta yanke huldar diflomasiyya da kasar Hadaddiyar Daular Larabawa da kuma kiran hanzarta dawowar ma’aikatan ofishin jakadancin Sudan gida daga Abu Dhabi.

Kwamitin tsaro da kula da matakan tsaron Sudan ya bayyana cewa: Fiye da shekaru biyu, daukacin duniya take bibiyar laifuffukan wuce gona da iri kan kasar Sudan, da tabbatar da tsaron yankunanta, da tsaron ‘yan kasarta daga hadaddiyar daular Larabawa ta hanyar wakiliyarta na cikin gida, ‘yan ta’adda, masu tayar da kayar baya na kungiyar Rapid Support Forces ta dakarun kai daukin gaggawa, kuma masu goyon bayan siyasarsu.

Ya kara da cewa: “Lokacin da Hadaddiyar Daular Larabawa ta tabbatar da rushewar wakilayarta na cikin gida, wanda sojojin Sudan suka fatattake su, sai Hadaddiyar Daular Larabawar ta kara ba da goyon bayanta tare da bayar da karin karfinta wajen baiwa ‘yan tawayen makamai na zamani.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Hadaddiyar Daular Larabawa kasar Sudan

এছাড়াও পড়ুন:

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

A ranar Alhamis 24 ga watan nan ne aka tantance tare da amincewa da biranen kasar Sin guda tara a matsayin biranen dausayi na kasa da kasa, yayin bude taron bangarorin da suka kulla yarjejeniyar Ramsar kan filayen dausayi karo na 15 (COP15), da aka gudanar a birnin shakatawa na Victoria Falls na kasar Zimbabwe, inda hakan ya kara adadin wadannan biranen a kasar Sin zuwa 22.

Sabbin biranen tara da aka amince da su sun hada da Chongming na Shanghai, da Dali na lardin Yunnan, da Fuzhou na lardin Fujian, da Hangzhou na lardin Zhejiang, da Jiujiang na lardin Jiangxi, da birnin Lhasa na jihar Xizang mai cin gashin kanta, da Suzhou na lardin Jiangsu, da Wenzhou na lardin Zhejiang, da kuma Yueyang da ke lardin Hunan.

Magajin garin birnin Kasane na kasar Botswana, Johane Chenjekwa, ya yaba wa kasar Sin bisa yadda ta inganta aikin kiyaye filin dausayi, yana mai cewa, Afirka za ta iya cin gajiyar hadin gwiwa da kasar Sin wajen kula da filin dausayi.

Ya kara da cewa, “Za mu sa lura mu ga abun da za mu iya koya daga gare su yayin da muke hulda da juna. Su ma suna da muradin koyon yadda muke gudanar da abubuwa a nan, don haka ana samun babbar kwarewa idan ana cudanya da juna.” (Abdulrazaq Yahuza jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa
  • An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
  • ‘Yan Tawayen Sudan Ta Kungiyar Rapid Support Forces Sun Kashe Mutane 27 A Yammacin Jihar Kordofan Ta Kasar Sudan
  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Iran Tace Tawagar Kwararru Daga Hukumar IAEA Zata Ziyarci Kasar Nan Ba Da Dadewa Ba
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta