Sai dai, rikice-rikicen cikin gida da matsalolin tsaro da tattalin arziƙi sun sa gwamnatin ke ci gaba da yin gyare-gyare don samar da hanyoyin da za su ba ta kariya da cikakken iko kan harkokin leƙen asiri da tsaro.

Wannan mataki yana iya nuni da cewa Nijar na ƙoƙarin zama mai dogaro da kai a fannin tsaro, ko kuma tana neman ƙawancen da zai fi dacewa da manufofinta na cikin gida da waje.

Duk da haka, ƙwararru na ganin cewa hakan na iya janyo sabon matsin lamba daga ƙasashen duniya da ƙungiyoyin yanki kamar ECOWAS.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Bayanan Sirri ECOWAS Nijar Rasha Turkiyya Yarjejeniya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa

Gwamnatin Tarayya ta ce ƙofofinta buɗe suke ta sayar da dukkan matatun manta na Warri, Fatakwal da Kaduna ga ’yan kasuwa domin ƙarfafa gasa a fannin tace mai a Najeriya.

Mai ba Shugaban ƙasa Bola Tinubu shawara kan harkokin makamashi, Olu Verheijen ce ta bayyana hakan a wata hira da Bloomberg TV a gefen taron makamashi na ADIPEC da aka gudanar a Abu Dhabi, Hadaddiyar Daular Larabawa, ranar Talata.

Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir

Verheijen ta ce wannan mataki na daga cikin shawarwarin da ake dubawa don inganta harkar man fetur a Najeriya.

“Daya daga cikin matakan da za a iya la’akari da su kenan, musamman idan aka samu wanda yaje da kwarewa da kuma jarin da zai iya sayen su,” in ji ta.

Ta ce matatun man da a baya suka dade suna aiki a ƙarƙashin tallafin gwamnati, yanzu sun sami kishiyoyi bayan cire tallafin man fetur.

“Yanzu da muka cire tallafin, mun kawar da duk wani tarnaki da ke cikin wannan kasuwar ta man fetur,” kamar yadda ta fada.

A watan Oktoba, Kamfanin Man Fetur na Najeriya (NNPCL) Limited ya sanar da fara cikakken bincike na fasaha da kasuwanci kan matatun mai guda hudu da gwamnati ke da su.

Tun a watan Yuli, Shugaban kamfanin Group, Bayo Ojulari, ya ce aikin gyaran matatun ya ɗan samu tsaiko, yana mai cewa kamfanin na fatan kammala sake duba su kafin ƙarshen shekara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Goyi Bayan Matakin shari’ar Turkiyya Kan Neman kama Masu Take Hakkin Bil’Adama A Isra’ila
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Yadda Duniya Ta Fara Wayewa Tun Daga Zamanin Annabi Nuhu (AS) Har Manzon Allah (SAW) Ya Zo Ya Cika Komai (2)
  • Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar
  • Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • An Kama ‘Yan Jarida 3 A Nijar Bi Sa Tuhumar  Fitar Da Bayanai Na Hukuma