Iran Ta Ce Ana Yin Nazari Kan Lokacin Gudanar Da Zagaye Na Hudu Na Shawarwari Tsakanin Iran Da Amurka
Published: 7th, May 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa; Ana nazarin lokacin gudanar da zagaye na huɗu na shawarwari tsakanin Iran da Amurka
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya sanar da cewa: Ana nazari kan lokacin gudanar da zagaye na gaba na tattaunawar Iran da Amurka wand aba na kai tsaye ba, kuma mai shiga tsakani na Oman zai sanar da karin bayani da zarar an tantance lokaci da wurin da za a yi.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya shaidawa kamfanin dillancin labaran kasar Iran cewa: Ana duban lokacin da za’a gudanar da zagaye na gaba na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka.
Baqa’i ya kara da cewa: Mai shiga tsakani na Oman zai sanar da bayanai dangane da haka da zarar an tantance lokaci da wuri.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Har yanzu ba a sanya ranar karshe da za a gudanar da shawarwarin na gaba ba, amma ana duban shawarar da Oman ta gabatar na gudanar da tattaunawar a farkon mako mai zuwa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Kakakin ma aikatar harkokin wajen Iran Iran da Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Muna shawartar Trump kada ya shiga yaƙin Iran da Isra’ila — Birtaniya
Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya buƙaci Donald Trump kada ya ɗauki matakin soji kan Iran, yana mai kiran da a biyo wa lamarin ta hanyar lalama.
Mista Starmer ya ce akwai “mummunan hatsarin bazuwar” yaƙin, inda ya yi kira ga duka ɓangarorin sun rungumi sulhu.
Ba zai yiwu mu bar Khamenei a raye ba — Isra’ila Hisbah ta lalata katan 243 na barasa da wasu kayan maye a YobeYa ƙara da cewa a baya an samu “jerin tattauna masu yawa da Amurka, kuma ina ganin wannan ita ce hanyar warware matsalar.”
Kalaman nasa na zuwa ne yayin da sakataren harkokin wajensa, David Lammy ke shirin ganawa da takwaransa na Amurka, Marco Rubio kan yadda za a taƙaita bazuwar yaƙin.
Da maraicen yau Alhamis ne kuma Mista Lammy da Mista Rubio suka gana domin tattauna halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya.
Su ma shugabannin China da na Rasha sun yi Alla-wadai da hare-haren Isra’ila kan Iran tare da kiran a tsagaita wuta.
Shugaba Xi Jinping da Vladimir Putin sun tattauna ta waya inda suka nuna goyon-bayan amfani da hanyoyin diflomasiya wajen shawo kan rikicin.
Ministan Harkokin Wajen Iran, Abbas Aragchi zai tattauna da takwarorinsa na Faransa da Jamus da Birtaniya a Geneva a gobe Juma’a.