APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo
Published: 7th, May 2025 GMT
Ya ce, “Na koma jam’iyyar APC ne domin in ci gaba da samun ribar kujerar kakakin majalisar domin ci gaban mazaba ta.
“A gare ni, sauya sheka ba batun jam’iyya ba ne, illa don ci gaban mazaba ta, a matsayina na mai wakiltar mutane na, idan na jefar da wannan matsayi saboda jam’iyya, matsayin da zai bunkasa ci gaban yankina, hakan na nufin ban shirya yi wa jama’a aiki ba.
“’Yan uwana na majalisa, ina so in sanar da wannan majalisa a hukumance cewa, kakakin majalisar, Rt. Hon. Blessing Agbebaku, ya koma APC,” inji shi.
Agbebaku ya bayyana cewa ‘yan mazabar sa na goyon bayan matakin da ya dauka, inda ya ce “akwai ayyukan ci gaba a mazabar Owan ta Yamma wanda Gwamna Monday Okpebolo ya kaddamar.”
Ya kara da cewa, “Don haka, sauya sheka na ba wai don wata manufa ta kashin kai ba ce, sai dai sadaukar da kai ga wadanda suka zabe ni, muradin al’ummata ne gaba a don da izininsu nake zaune anan yau,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai
Majalisar Wakilai ta bayyana cewa ta amince da duk wasu tsare-tsare da dabarun karɓo rancen kuɗaɗe na Shugaba Bola Tinubu, bisa la’akari da ƙoƙarin da yake yi na farfaɗo da tattalin arziki da kuma rage talauci a ƙasar nan.
Shugaban Majalisar, Abbas Tajudeen ne ya bayyana hakan a yayin da yake jawabi ranar Litinin, a taron shekara-shekara karo na takwas kan bitar kasafin kuɗaɗe na majalisun dokokin nahiyyar Afirka (African Network of Parliamentary Budget Offices) da ke gudana a Abuja.
Sarkin Ruman Katsina ya rasu Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a NejaAbbas ya ƙaryata raɗe-raɗin cewa majalisar ta ƙi amincewa da tsare-tsaren karɓo rance na shugaban ƙasar, inda ya ce zantuka ne marasa tushe da aka ƙirƙira da manufa ta yaudara.
A cewarsa, “kwanan nan, an yi wa jawabin da Shugaban Masu Rinjaye na majalisar ya gabatar a taron majalisun dokoki na Afirka (West African Parliamentary Conference, WAPC) mummunar fassara, har aka rika yi wa majalisar kuskuren fahimta cewar ba ta goyon bayan tsare-tsare da dabarun rancen gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Wannan kuskuren fahimta ne, kuma ba gaskiya ba ce.”
Abbas ya jaddada cewa Majalisar Dokokin Tarayya baki ɗaya, sun amince cewa rance mai tsari cike da kulawa hanya ce da ake amfani da ita wajen gina muhimman ababen more rayuwa, ƙarfafa ci gaban tattalin arziki, da kuma tallafa wa marasa galihu.
Ya bayyana cewa, a ƙarƙashin jagorancin Tinubu, ana karkatar da kuɗaɗen rancen ne zuwa manyan ayyuka da suka haɗa da wutar lantarki, sufuri da noma, waɗanda za su ƙara inganta hanyoyin tattara kuɗaɗen shiga.
Abbas ya kuma tabbatar da cewa duk wani bashi za a karɓo shi ne cikin hikima da kuma tsare-tsaren rance na ƙasar na matsakaicin lokaci da wanda sun dace da duk wasu ƙa’idoji a fadin duniya.
Kazalika, ya jaddada muhimmancin kafa Ofishin Kasafin Kuɗi da Bincike na Majalisa (NABRO) domin yin bincike mai zaman kansa kan batutuwan rance, karɓo bashi da kuma manufofin kuɗi.
Sai dai shugaban majalisar ya yi gargaɗin cewa duk da yake karɓo rancen wajibi ne, amma buƙatar rufe ɓarakar sata da fitar da kuɗaɗen haramun ita ma babban lamari ne da ya zama tilas.
Ya bayyana cewa Najeriya na asarar kusan dala biliyan 18 duk shekara ta hanyar cin hanci da zamba da kuma halasta kuɗaɗen haramun — adadin da ya kai kusan kashi 3.8% na GDP.
Abbas ya ce haɗa rance mai tsari da kuma tsauraran matakan sa ido da yaƙi da cin hanci shi ne zai tabbatar da makomar tattalin arzikin Najeriya.