APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo
Published: 7th, May 2025 GMT
Ya ce, “Na koma jam’iyyar APC ne domin in ci gaba da samun ribar kujerar kakakin majalisar domin ci gaban mazaba ta.
“A gare ni, sauya sheka ba batun jam’iyya ba ne, illa don ci gaban mazaba ta, a matsayina na mai wakiltar mutane na, idan na jefar da wannan matsayi saboda jam’iyya, matsayin da zai bunkasa ci gaban yankina, hakan na nufin ban shirya yi wa jama’a aiki ba.
“’Yan uwana na majalisa, ina so in sanar da wannan majalisa a hukumance cewa, kakakin majalisar, Rt. Hon. Blessing Agbebaku, ya koma APC,” inji shi.
Agbebaku ya bayyana cewa ‘yan mazabar sa na goyon bayan matakin da ya dauka, inda ya ce “akwai ayyukan ci gaba a mazabar Owan ta Yamma wanda Gwamna Monday Okpebolo ya kaddamar.”
Ya kara da cewa, “Don haka, sauya sheka na ba wai don wata manufa ta kashin kai ba ce, sai dai sadaukar da kai ga wadanda suka zabe ni, muradin al’ummata ne gaba a don da izininsu nake zaune anan yau,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
Shugaban ya kuma yaba bisa gudunmawar da kwararrun matasa ke samar wa, musamman masu yiwa kasa hidima da ke yin aikin yiwa kasa hidama, a Hukumar ta NPA.
Ya danganta su a matsayin matasan gobe da za su samar da sauyi wajen ci gaba da bunkasa fannin tattalin azrki na Teku da kuma ga daukacin tattalin arzikin kasar nan.
An kirkiro da wannan ranar ta NMD ce, a shekarar 2014 wadda kuma aka kaddamar da ita a kasar Ingila a shekarar 2016, wadda kuma ake gudnar da bikin zagoywar ranar, a duk ranar 27 na watan Okutobar kowacce shekara.
Kazalika, gudanar da bkin wannan ranar, ta yi daidai da cimma muradun karni, na Majalisar Dinkin Duniya.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA