Kasashen duniya sun damu da rikici tsakanin Indiya da Pakistan
Published: 7th, May 2025 GMT
Kasashen duniya na ci gaba da nuna matukar damuwa game da rikicin da ya barke tsakanin Pakistan da Indiya.
Iran na daga cikn jerin kasashen da a baya bayan nan suka nuna damuwa.
Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Iran ta fitar ta ce “Jamhuriyar Musulunci ta bayyana matukar damuwarta kan yadda takun saka tsakanin Indiya da Pakistan ke ci gaba da ruruwa.
Iran ta ce a matsayinta na kasa mai iyaka da Pakistan wacce kuma ke da kyakkyawar alaka da Indiya, ta yi tayin shiga tsakani a rikicin tun cikin watan Maris.
Kasar Turkiyya ma ta yi gargadin game da rikicin.
Inda a wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ta yi Allah wadai da hare-haren da ake kai wa fararen hula da kayayyakin more rayuwa.
A nata bangaren gwamnatin Jamus ta yi kira da a dakile duk wani tashin hankali da kuma kare fararen hula.
Moscow ta yi kira ga kasashen Indiya da Pakistan da su yi taka-tsan-tsan.
Inda ta bukaci bangarorin da su yi taka-tsantsan don kaucewa tabarbarewar lamarin.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin tarayya ki amince damu a matakin ƙasa – Bijilanti
Kwamandan Ƙungiyar sa kai ta Vigilante Group of Nigeria (VGN) reshen Jihar Kaduna, Abdulwahab Muhammed ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta amince da Ƙungiyar a matakin ƙasa ta hanyar sanya hannu a kan ƙudurin da aka gabatar.
A cewar ƙungiyar bisa la’akari da irin rawar da take takawa wajen daƙile ayyukan miyagu da samar da tsaro a sassan ƙasar nan.
An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai Ma’aikacin jinya ya kashe marasa lafiya 10 saboda aiki ya masa yawaYa ce lokaci ya yi da gwamnati za ta sa hannu kan kudurin amincewa da kungiyar domin kasancewa cikin jerin hukumomin tsaro na kasa, la’akari da irin jajircewar da suke nunawa musamman a Jihar Kaduna.
Abdulwahab ya bayyana hakan ne yayin taron ƙarin girma da ƙungiyar ta shirya ga wasu jami’anta a Ƙaramar hukumar Jama’a, inda kuma aka karrama wasu fitattun mutane da ke ba da gudunmawa wajen tallafa wa ayyukan tsaro.
Kwamandan ya ce, suna da kyakkyawar fahimta da haɗin kai da sauran jami’an tsaro, inda suke miƙa waɗanda suka kama ga ’yan sanda don gudanar da bincike da yin hukunci bisa doka. Ya roƙi gwamnatin jihar Kaduna da ta ƙara tallafa musu da kayan aiki domin sauƙaƙa gudanar da ayyukansu.
Shi ma Shugaban karamar hukumar Jama’a Peter Tanko Dogara wanda sakataren Ƙaramar hukumar Jama’a, Dakta Shehu Usman Danbala ya wakilta, ya yaba da ƙoƙarin ƙungiyar wajen tabbatar da tsaro a matakin sa kai, tare da kiran al’umma da su riƙa basu cikakken goyon baya.