HausaTv:
2025-05-08@00:53:20 GMT

Kasashen duniya sun damu da rikici tsakanin Indiya da Pakistan

Published: 7th, May 2025 GMT

Kasashen duniya na ci gaba da nuna matukar damuwa game da rikicin da ya barke tsakanin Pakistan da Indiya.

Iran na daga cikn jerin kasashen da a baya bayan nan suka nuna damuwa.

Sanarwar da ma’aikatar harkokin wajen Iran ta fitar ta ce “Jamhuriyar Musulunci ta bayyana matukar damuwarta kan yadda takun saka tsakanin Indiya da Pakistan ke ci gaba da ruruwa.

Iran ta ce a matsayinta na kasa mai iyaka da Pakistan wacce kuma ke da kyakkyawar alaka da Indiya, ta yi tayin shiga tsakani a rikicin tun cikin watan Maris.

Kasar Turkiyya ma ta yi gargadin game da rikicin.

Inda a wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen kasar ta fitar ta yi Allah wadai da hare-haren da ake kai wa fararen hula da kayayyakin more rayuwa.

A nata bangaren gwamnatin Jamus ta yi kira da a dakile duk wani tashin hankali da kuma kare fararen hula.

Moscow ta yi kira ga kasashen Indiya da Pakistan da su yi taka-tsan-tsan.

Inda ta bukaci bangarorin da su yi taka-tsantsan don kaucewa tabarbarewar lamarin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Kotun Duniya Ta Wanke HDL Akan Zargin Kisan Kiyashi A Sudan

Kotun duniya ta yi watsi da karar da Sudan ta kai Hadaddiyar Daular Larabawa tana mai zarginta da hannu a kisan kiyashin da aka yi wa al’ummar wannan kasa.

A yau Litinin ne kotun duniyar ta yi watsi da karar ta Sudan, tana mai wanke Hadaddiyar Daular Larabawa.

Ita dai Sudan ta zargi Hadaddiyar Daular Larabawar da cewa ta hada baki da dakarun kai daukin gaggaawa wajen yi wa mutanen yankin Darfur kisan kiyashi.

A nata gefen Hadaddiyar Daular Larabawan ta ki amincewa da tuhumar da Sudan ta yi mata  tana mai siffata ta da cewa; Farfaganda ce, kuma Sudan din ta yi hakan ne domin kawar da hankulan duniya daga kan laifukan da sojoji suke aikatawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo
  • Yaƙi ya ɓarke tsakanin Indiya da Pakistan
  • Kasar Indiya Ta Yi Luguden Makamai Masu Linzami Kan Kasar Pakistan
  • Aragchi Ya Ce Hanyar Diblomasiyya Ce Kadai Hanar Warware Matsalar Shirin Nukliyar Iran
  • Iran Ta Bukaci Kasashen Turai Su Shiga Tattaunawar Nukliya Da Take Yi Da Amurka
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Sha Alwashin Mayar Da Martani Cikin Gaggawa Kan Duk Wani Hari Kan Kasarta
  • Sharhin bayan Labarai: Ci Gaban Harkokin Kasuwanci Tsakanin Iran Da Kasashen Waje Duk Tare Da Takunkuman Kasashen Yamma
  •  Kotun Duniya Ta Wanke HDL Akan Zargin Kisan Kiyashi A Sudan
  • Iran ta watsi da zargin Isra’ila da Amurka cewa ta na da hannu a harin ramuwar gayya na Yemen