Aminiya:
2025-06-27@03:20:54 GMT

Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo

Published: 19th, April 2025 GMT

Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo ya bayyana cewa masu garkuwa da mutane da aka samu da laifi a jihar za su fuskanci hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Okpebholo ya bada tabbacin a shirye yake ya sanya hannu akan sammacin kisa na waɗanda aka yankewa hukunci a jihar idan kotu ta same su da laifi.

An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a Neja PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – Wike

Gwamna Okpebholo ya bayyana hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a garin Uromi, inda ya tattauna da shugabanni da ’yan uwa na yankin unguwar ’yan Arewa mazauna Esan.

“Ku tuna cewa Majalisar Dokokin Jihar Edo (EDHA) ta zartar da wani ƙudiri na gyara dokar hana garkuwa da mutane (da wasu dokoki da suke da alaƙa da na shekarar 2013)”.

Ƙudirin dokar ya tanadi hukuncin kisa ga masu garkuwa da mutane sannan kuma ya ba da umarnin ƙwacewa da rushe dukiyoyin da ake yin amfani da su wajen aikata laifukan.

A cewar gwamnan, gwamnatinsa ba za ta lamunci rashin tsaro, kisan gilla da kuma garkuwa da mutane ba.

“Na ɗauki batun rashin tsaro da muhimmanci kuma ba zan karkatar da ƙa’idar ba sai dai a yi amfani da su sosai, sabuwar dokar jihar ta ba mu damar rusa kadarorinsu da ƙwace musu filayensu.

“Za mu kawo masu garkuwa da mutane a gaban jama’a, mu kashe su domin mu nuna muhimmancinmu a kan dokokin da Majalisar Edo ta riga ta yi, ba zan ji tsoron sanya hannu a kai ba,” in ji shi.

Gwamnan ya yi kira ga kowa da kowa da su ba gwamnatinsa haɗin kai don tabbatar da tsaron jihar, yana mai cewa “tsaro aikin kowa ne ba na hukumomin tsaro kaɗai ba”.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnan jihar Edo Hukuncin rataya Masu Garkuwa da mutane Monday Okpebholo garkuwa da mutane masu garkuwa

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

Jiya Laraba 25 ga watan Yuni ne, a birnin Rome na kasar Italiya, aka kaddamar da gagarumin bikin nune-nunen kayan al’adu na murnar cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Italiya, karkashin hadin-gwiwar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, da ma’aikatar raya al’adu ta Italiya, da gidan adana kayan tarihi na wayin kan dan Adam na Italiya, da cibiyar koyon fasahohin zane-zane dake birnin Rome na Italiya, da kungiyar wasan kwallon kafar Italiya da sauransu.

Bikin na nuna nagartattun kayayyakin al’adu sama da dari biyu da shahararrun masu zane-zane, da magadan al’adun gargajiya da ba na kayayyaki ba, da sauran wasu masu aikin fasahohin al’adu na kasar Sin fiye da 100 suka yi, tare da kayayyakin al’adu masu daraja sama da 100 da aka adana a gidan adana kayan tarihi na wayin kan dan Adam na Italiya.

A wannan rana kuma, CMG ya shirya bikin musanyar al’adu na murnar cika shekaru 55 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Italiya a birnin Rome, inda aka kaddamar da “makon nuna fina-finan kasar Sin na shekara ta 2025 a Italiya”. (Murala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
  • Yadda aka kama mai garkuwa da mutane yana tsaka da cin kasuwar shanu a Neja
  • Gwamnatin Neja ta rufe Jami’ar IBB bayan ɓarkewar rikici
  • Mutane 4 Sun Mutu, 10 Sun Jikkata Yayin Da Wata Mota Ta Taka Bam A Borno
  • PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta
  • An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya
  • Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6
  • Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
  • Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta —Trump
  • Trump ta ce Iran da Isra’ila sun amince da tsagaita wuta bayan harin Iran kan sansanonin Amurka