Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo
Published: 19th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo ya bayyana cewa masu garkuwa da mutane da aka samu da laifi a jihar za su fuskanci hukuncin kisa ta hanyar rataya.
Okpebholo ya bada tabbacin a shirye yake ya sanya hannu akan sammacin kisa na waɗanda aka yankewa hukunci a jihar idan kotu ta same su da laifi.
An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a Neja PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – WikeGwamna Okpebholo ya bayyana hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a garin Uromi, inda ya tattauna da shugabanni da ’yan uwa na yankin unguwar ’yan Arewa mazauna Esan.
“Ku tuna cewa Majalisar Dokokin Jihar Edo (EDHA) ta zartar da wani ƙudiri na gyara dokar hana garkuwa da mutane (da wasu dokoki da suke da alaƙa da na shekarar 2013)”.
Ƙudirin dokar ya tanadi hukuncin kisa ga masu garkuwa da mutane sannan kuma ya ba da umarnin ƙwacewa da rushe dukiyoyin da ake yin amfani da su wajen aikata laifukan.
A cewar gwamnan, gwamnatinsa ba za ta lamunci rashin tsaro, kisan gilla da kuma garkuwa da mutane ba.
“Na ɗauki batun rashin tsaro da muhimmanci kuma ba zan karkatar da ƙa’idar ba sai dai a yi amfani da su sosai, sabuwar dokar jihar ta ba mu damar rusa kadarorinsu da ƙwace musu filayensu.
“Za mu kawo masu garkuwa da mutane a gaban jama’a, mu kashe su domin mu nuna muhimmancinmu a kan dokokin da Majalisar Edo ta riga ta yi, ba zan ji tsoron sanya hannu a kai ba,” in ji shi.
Gwamnan ya yi kira ga kowa da kowa da su ba gwamnatinsa haɗin kai don tabbatar da tsaron jihar, yana mai cewa “tsaro aikin kowa ne ba na hukumomin tsaro kaɗai ba”.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnan jihar Edo Hukuncin rataya Masu Garkuwa da mutane Monday Okpebholo garkuwa da mutane masu garkuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya shawarci matasan da ake ribatarsu a matsayin ’yan daban siyasa da suka tuba da su guji tashin hankali, yana tabbatar musu da shirye-shiryen gwamnatinsa na gyara tarbiyarsu tare da mayar da su cikin al’umma.
Gwamnan ya yi wannan alkawari ne a taron wuni ɗaya da aka gudanar tare da shugabannin rukunan ’yan daban da suka tuba a ƙarƙashin Shirin Safe Corridor.
Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a JigawaGwamnan, wanda Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Waiya, ya wakilta, ya ce: “Ba za a sake ɗaukar makami da sunan fadan siyasa ko wasu munanan dabi’u ba.
“Za mu gyara muku tarbiya, mu tabbatar kun samu ababen yi da suka dace domin samun abun dogaro da kai. Za mu karɓe ku ɗaya bayan ɗaya, mu gyara ku, mu tura ku inda kuka fi dacewa.”
Waiya ya bayyana cewa wasu daga cikin tubabbun mutanen da aka yi wa rajista a baya a cikin shirin sun riga sun rasu, inda gwamnati za ta sake gudanar da sabon aikin tantancewa domin sabunta bayanai.
Ya jaddada cewa wannan shiri ba na siyasa ba ne, yana mai cewa manufarsa ita ce kawar da matsalar ‘yan daba da sauran munanan halaye a jihar.
“Mutane da dama masu shekarunku suna yin abubuwa masu kyau. Mun fahimci cewa ba ku ci moriyar wasu shirye-shirye na tallafi ba a baya, amma yanzu mun tsaya tsayin daka domin ku,” in ji shi.
Sauran masu jawabi a yayin taron sun haɗa da Kwamandan Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) na Kano, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar, da sauran masu ruwa da tsaki wajen yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi a Kano.