Amurka, Ki Fahimci Cewa “Girma Da Arziki Ke Sa A Ja Bajimin Sa Da Zaren Abawa”
Published: 15th, April 2025 GMT
Ban da haka, Wang ya ce matakan kasar Amurka sun karya ka’idojin kungiyar WTO na rashin nuna bambanci, da takaita karbar haraji, kana suna girgiza tsarin tattalin arzikin duniya, da tushen tsarin cinikayya da ya shafi bangarori daban daban. Ganin haka ya sa kasar Sin daukar matakan ramuwar gayya kan kasar Amurka, don kare halaltacciyar moriyar kai, gami da neman tabbatar da adalci a duniya.
Da ma shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya gabatar da jerin zafafan matakan tattalin arziki ne don neman daidaita matsalolin da kasar Amurka ke fuskanta. Sai dai ra’ayinsa na dora “Amurka ta zama gaba da komai” na tarnake masa damar samun biyan bukata.
Raymond Thomas Dalio, shahararren mai kula da sha’anin hada-hadar kudi ne, wanda ya kafa kamfanin Bridgewater Associates, ya tattauna tare da ‘yan jarida a kwanan baya, inda ya fayyace matsalolin da kasar Amurka ke fuskanta a fannin tattalin arziki, kamar su: dimbin bashin da ake binta, da rashin karfin samar da kayayyakin da take bukata, da dai sauransu. A cewarsa, Amurka ta riga ta tsunduma cikin mawuyacin hali na cin bashi da kashe kudi fiye da kima a kai a kai, lamarin da ya haddasa rushewar tsarin kudi da siyasa na duniya, da kawo karshen zamanin tilasta zama karkashin jagorancin kasar Amurka. Kana mista Dalio ya ce yanzu haka, Amurka na neman daidaita matsalolin da take fuskanta ta hanyar ta da rikici a duniya, da karin matsin lamba ga sauran kasashe, lamarin da a cewarsa zai iya haifar da sakamako mafi muni, da kawo tafiyar hawainiya ga tattalin arzikinta.
Hausawa kan ce “Girma da arziki ke sa a ja sa da zaren abawa.” Sai dai a nata bangare, kasar Amurka ta tsaya kan daukar matakan radin kai, da matsawa da cin zarafin sauran kasashe, duk da cewa tana bukatar samun taimako daga saura wajen daidaita matsalar da take fuskanta, inda kuma sam ba zai yiwu ta samu biyan bukata ta wannan turbar ba.
A karshe dai za a lalubo dabara kamar yadda minsta Wang Wentao ya fada, “nemo bakin zaren wareware matsala ta hanyar shawarwari, bisa tushen girmama juna, da zaman daidaito”, matukar ana son warware matsalar.
Muna fatan ganin kasar Amurka ta zama mai sanin ya kamata, da wajabta wa kanta iya sauraron shawara, da daukar mataki mafi dacewa. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan
Ma’aikatar raya al’adu da yawon bude ido ta kasar Sin ta fitar da sanarwa a jiya Lahadi, wadda ke kira ga al’ummunta da su yi taka-tsantsan a kwanakin nan wajen zuwa yawon bude ido kasar Japan.
Game da hakan, masani a kwalejin bincike ta Nomura Takahide Kiuchi, ya bayyana a jiyan cewa, raguwar yawan Sinawa masu zuwa yawon bude ido Japan, zai haifar da raguwar GDPn kasar ta Japan da kashi 0.36%, kana hasashen yawan asarar tattalin arziki da hakan zai haifar zai kai JYE tiriliyan 2.2, kwatankwachin kudin Sin yuan biliyan 101.6.
Bayanai sun nuna cewa, kasar Sin ce babbar abokiyar ciniki mafi girma ta Japan, kasa ta biyu mafi girma wajen fitar da kayayyaki zuwa kasar, kana babban tushen shigar da kayayyaki zuwa kasar. A shekarar 2024, jimillar darajar ciniki tsakanin Sin da Japan ta kai dalar Amurka biliyan 308.3, inda yawan kudin da Sin ta kashe wajen shigo da kayayyaki daga Japan ya kai dalar Amurka biliyan 156.25.
Kididdigar hukuma mai kula da yawon bude ido ta Japan, ta nuna cewa jimillar kudin da masu yawon bude ido na Sin suka kashe a Japan a shekarar 2024 ya haura na al’ummun sauran kasashen duniya.
Manyan ’yan siyasa, da masana masu fashin baki, da kafafen watsa labarai na yankin Taiwan, sun yi Allah wadai da kalaman tayar da husuma na firaministar Japan Sanae Takaichi dangane da yankin Taiwan na Sin, suna masu bayyana kalaman nata a matsayin wadanda suka illata moriyar al’ummun Taiwan, wato mazauna yankin dake fatan wanzuwar zaman lafiya da daidaito a daukacin mashigin Taiwan.
Da yake tsokaci kan hakan, tsohon shugaban jam’iyyar Kuomintang a yankin Taiwan Ma Ying-jeou, ya ce batutuwan da suka shafi bangarori biyu na mashigin Taiwan ba sa bukatar tsoma bakin sassan waje, yana mai jaddada cewa al’ummunsu ne kadai ke da alhakin warware su. Jami’in ya kara da cewa, Sinawa na bangarorin mashigin Taiwan biyu na da basira, da ikon warware sabaninsu cikin lumana.
Shi ma a nasa tsokaci, mawallafin mujallar “Observer” Chi Hsing, cewa ya yi, a yayin mamayar dakarun Japan, al’ummun Taiwan ba su taba dakatar da nuna turjiyarsu ba. Don haka duk wani mai kaunar adalci dake Taiwan zai yi tir da kalaman na firaminista Takaichi.
Hsieh Chih-chuan, mai fashin baki kan batutuwan siyasar Taiwan, ya ce kalaman na Takaichi sun sabawa ainihin tarihi da dokokin kasa da kasa. Daga nan sai ya gargadi ’yan aware masu rajin neman ’yancin kan Taiwan, da kada su yaudari kansu bisa kalaman na Takaichi. Domin kuwa ba makawa Sin za ta kasance kasa daya dunkulalliya.(Saminu Alhassan、Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA