Ban da haka, Wang ya ce matakan kasar Amurka sun karya ka’idojin kungiyar WTO na rashin nuna bambanci, da takaita karbar haraji, kana suna girgiza tsarin tattalin arzikin duniya, da tushen tsarin cinikayya da ya shafi bangarori daban daban. Ganin haka ya sa kasar Sin daukar matakan ramuwar gayya kan kasar Amurka, don kare halaltacciyar moriyar kai, gami da neman tabbatar da adalci a duniya.

 

Da ma shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya gabatar da jerin zafafan matakan tattalin arziki ne don neman daidaita matsalolin da kasar Amurka ke fuskanta. Sai dai ra’ayinsa na dora “Amurka ta zama gaba da komai” na tarnake masa damar samun biyan bukata.

 

Raymond Thomas Dalio, shahararren mai kula da sha’anin hada-hadar kudi ne, wanda ya kafa kamfanin Bridgewater Associates, ya tattauna tare da ‘yan jarida a kwanan baya, inda ya fayyace matsalolin da kasar Amurka ke fuskanta a fannin tattalin arziki, kamar su: dimbin bashin da ake binta, da rashin karfin samar da kayayyakin da take bukata, da dai sauransu. A cewarsa, Amurka ta riga ta tsunduma cikin mawuyacin hali na cin bashi da kashe kudi fiye da kima a kai a kai, lamarin da ya haddasa rushewar tsarin kudi da siyasa na duniya, da kawo karshen zamanin tilasta zama karkashin jagorancin kasar Amurka. Kana mista Dalio ya ce yanzu haka, Amurka na neman daidaita matsalolin da take fuskanta ta hanyar ta da rikici a duniya, da karin matsin lamba ga sauran kasashe, lamarin da a cewarsa zai iya haifar da sakamako mafi muni, da kawo tafiyar hawainiya ga tattalin arzikinta.

 

Hausawa kan ce “Girma da arziki ke sa a ja sa da zaren abawa.” Sai dai a nata bangare, kasar Amurka ta tsaya kan daukar matakan radin kai, da matsawa da cin zarafin sauran kasashe, duk da cewa tana bukatar samun taimako daga saura wajen daidaita matsalar da take fuskanta, inda kuma sam ba zai yiwu ta samu biyan bukata ta wannan turbar ba.

 

A karshe dai za a lalubo dabara kamar yadda minsta Wang Wentao ya fada, “nemo bakin zaren wareware matsala ta hanyar shawarwari, bisa tushen girmama juna, da zaman daidaito”, matukar ana son warware matsalar.

 

Muna fatan ganin kasar Amurka ta zama mai sanin ya kamata, da wajabta wa kanta iya sauraron shawara, da daukar mataki mafi dacewa. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka

Wani matashi mai shekaru 27, Chukwuebuka Eweni, ya shiga hannun ’yan sanda a birnin New Orleans na ƙasar Amurka, kan zargin kashe mahaifinsa har lahira tare da jikkata ’yan uwansa mata guda biyu a gidansu da ke unguwar Pebble.

Mahaifin matashin malami ne a fannin kimiyyar kwamfuta a Jami’ar Southern ta New Orleans.

Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — Akpabio Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16

Iyayen matashin waɗanda asalin ’yan Najeriya ne, sun bayyana lamarin a matsayin abin mamaki da ban tsoro.

Sun shaida cewar Chukwuebuka na fama rashin lafiyar ƙwaƙwalwa amma bai taɓa aikata wani mummunan abu ba.

Rahotanni sun nuna cewa ɗaya daga cikin ’yan matan da aka jikkata an sallame ta daga asibiti, yayin da ɗayar ke kwance tana samun kumawar likitoci.

Rundunar ’yan sandan New Orleans ta tabbatar cewa Chukwuebuka yana hannu kuma ana duba lafiyarsa, kafin kammala bincike.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:59 na daren ranar 11 ga watan Nuwamba, 2025.

’Yan sanda sun samu kiran agajin gaggawa, inda suka garzaya gidan da lamarin ya auku suka tarar da mahaifin matashin kwance cikin jini, sannan wasu biyu sun ji rauni.

Yanzu dai ana tuhumar Chukwuebuka da laifuka biyu da suka shafi kashe mahaifinsa da kuma ƙoƙarin kashe ’yan uwansa mata guda biyu.

Ofishin Korer na Orleans Parish, zai bayyana musabbabin rasuwar mahaifin matashin bayan kammala binciken gawar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95
  • Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka
  • Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30
  • An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur
  • Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki
  • Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho
  • Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka