Ban da haka, Wang ya ce matakan kasar Amurka sun karya ka’idojin kungiyar WTO na rashin nuna bambanci, da takaita karbar haraji, kana suna girgiza tsarin tattalin arzikin duniya, da tushen tsarin cinikayya da ya shafi bangarori daban daban. Ganin haka ya sa kasar Sin daukar matakan ramuwar gayya kan kasar Amurka, don kare halaltacciyar moriyar kai, gami da neman tabbatar da adalci a duniya.

 

Da ma shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya gabatar da jerin zafafan matakan tattalin arziki ne don neman daidaita matsalolin da kasar Amurka ke fuskanta. Sai dai ra’ayinsa na dora “Amurka ta zama gaba da komai” na tarnake masa damar samun biyan bukata.

 

Raymond Thomas Dalio, shahararren mai kula da sha’anin hada-hadar kudi ne, wanda ya kafa kamfanin Bridgewater Associates, ya tattauna tare da ‘yan jarida a kwanan baya, inda ya fayyace matsalolin da kasar Amurka ke fuskanta a fannin tattalin arziki, kamar su: dimbin bashin da ake binta, da rashin karfin samar da kayayyakin da take bukata, da dai sauransu. A cewarsa, Amurka ta riga ta tsunduma cikin mawuyacin hali na cin bashi da kashe kudi fiye da kima a kai a kai, lamarin da ya haddasa rushewar tsarin kudi da siyasa na duniya, da kawo karshen zamanin tilasta zama karkashin jagorancin kasar Amurka. Kana mista Dalio ya ce yanzu haka, Amurka na neman daidaita matsalolin da take fuskanta ta hanyar ta da rikici a duniya, da karin matsin lamba ga sauran kasashe, lamarin da a cewarsa zai iya haifar da sakamako mafi muni, da kawo tafiyar hawainiya ga tattalin arzikinta.

 

Hausawa kan ce “Girma da arziki ke sa a ja sa da zaren abawa.” Sai dai a nata bangare, kasar Amurka ta tsaya kan daukar matakan radin kai, da matsawa da cin zarafin sauran kasashe, duk da cewa tana bukatar samun taimako daga saura wajen daidaita matsalar da take fuskanta, inda kuma sam ba zai yiwu ta samu biyan bukata ta wannan turbar ba.

 

A karshe dai za a lalubo dabara kamar yadda minsta Wang Wentao ya fada, “nemo bakin zaren wareware matsala ta hanyar shawarwari, bisa tushen girmama juna, da zaman daidaito”, matukar ana son warware matsalar.

 

Muna fatan ganin kasar Amurka ta zama mai sanin ya kamata, da wajabta wa kanta iya sauraron shawara, da daukar mataki mafi dacewa. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasar Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya

Gwamnatin kasar Rwanda ta rattaba hannu a kan yarjeniya na dalar Amurka miliyon $228 a karkashin sabon tsarin taimako na gwamnatin kasar Amurka.

Shafin yanar gizo na labarai Africa News ya bayyana cewa tallafin zai taimakawa kasar Rwanda ta kyautata harkokin kiwon lafiya a kasar ta Rwanda a yayinda tallafin kudaden zai ci gaba a sabon tsarin da gwamnatin Amurka ta fitar don tallafawa kasashen kawayenta.

Tun ran Jumma’a ne aka bada labarin kulla wannan yarjeniyar, bayanda shugaba Paul Kagame na kasar Rwanda ya rattaba hannu kan wata yarjeniya ta zaman lafiya tsakaninsa da shugaban kasar Kongo Felix tsetsekedi don kawo karshen yaki a gabacin kasar Kongo wanda kasar ta Amurka ta jagoranta.

Karkashin wannan yarjeniyar dai Amurka zata kashe dalar Amurka miliyon $158 kan kyautata kiwon lafiya a kasar Rwanda ta hanyar yakar cututtuka masu yaduwa wadanda suka hada da HIV da Malaria. Da kuma kyautata tsarin shirin ko ta kwana na bullar cututtuka masu hatsari.

Sannan Kigali zata kara dalar Amurka miliyon $70 a cikin harkokin kiwon lafiya a kasar don bayyana kekyawar anniyarta a cikin shirin kyautata kiwon lafiya a kasar.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri December 7, 2025 Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21 December 7, 2025 Afirka Ta Kudu: An Kashe Mutane 11 A Wani Bude Wuta Na Kan Mai Uwa Da Wabi December 7, 2025  Dubban Mutane Suna Guduwa Daga  Gabashin DRC Saboda Barkewar Sabon Fada December 7, 2025 Mutane Biyar Ne Suka Mutu A Wata Musayar Wuta Tsakanin Sojojin Afghanistan Da Pakistan December 6, 2025 Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurumin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi December 6, 2025   Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • MِِِِDD:  Kisan Kare Dangin Da Isra’ila Ta yi A Gaza Shi Ne Farko Da Yafi Jan Hankalin duniya
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Yi Ganawar Sirri da Gwamnonin Jihohi Shidda
  • IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
  •  Macron Na Faransa Ya Yi Wa Najeriya Alkawalin Taimakawa Akan Matsalolin Tsaro
  • Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka  Teke Fuskanta
  • Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  • Venezuela: Ba Mu Tsoron Kaudin Amurka Na Wuce Gona Da Iri
  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21