Amurka, Ki Fahimci Cewa “Girma Da Arziki Ke Sa A Ja Bajimin Sa Da Zaren Abawa”
Published: 15th, April 2025 GMT
Ban da haka, Wang ya ce matakan kasar Amurka sun karya ka’idojin kungiyar WTO na rashin nuna bambanci, da takaita karbar haraji, kana suna girgiza tsarin tattalin arzikin duniya, da tushen tsarin cinikayya da ya shafi bangarori daban daban. Ganin haka ya sa kasar Sin daukar matakan ramuwar gayya kan kasar Amurka, don kare halaltacciyar moriyar kai, gami da neman tabbatar da adalci a duniya.
Da ma shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya gabatar da jerin zafafan matakan tattalin arziki ne don neman daidaita matsalolin da kasar Amurka ke fuskanta. Sai dai ra’ayinsa na dora “Amurka ta zama gaba da komai” na tarnake masa damar samun biyan bukata.
Raymond Thomas Dalio, shahararren mai kula da sha’anin hada-hadar kudi ne, wanda ya kafa kamfanin Bridgewater Associates, ya tattauna tare da ‘yan jarida a kwanan baya, inda ya fayyace matsalolin da kasar Amurka ke fuskanta a fannin tattalin arziki, kamar su: dimbin bashin da ake binta, da rashin karfin samar da kayayyakin da take bukata, da dai sauransu. A cewarsa, Amurka ta riga ta tsunduma cikin mawuyacin hali na cin bashi da kashe kudi fiye da kima a kai a kai, lamarin da ya haddasa rushewar tsarin kudi da siyasa na duniya, da kawo karshen zamanin tilasta zama karkashin jagorancin kasar Amurka. Kana mista Dalio ya ce yanzu haka, Amurka na neman daidaita matsalolin da take fuskanta ta hanyar ta da rikici a duniya, da karin matsin lamba ga sauran kasashe, lamarin da a cewarsa zai iya haifar da sakamako mafi muni, da kawo tafiyar hawainiya ga tattalin arzikinta.
Hausawa kan ce “Girma da arziki ke sa a ja sa da zaren abawa.” Sai dai a nata bangare, kasar Amurka ta tsaya kan daukar matakan radin kai, da matsawa da cin zarafin sauran kasashe, duk da cewa tana bukatar samun taimako daga saura wajen daidaita matsalar da take fuskanta, inda kuma sam ba zai yiwu ta samu biyan bukata ta wannan turbar ba.
A karshe dai za a lalubo dabara kamar yadda minsta Wang Wentao ya fada, “nemo bakin zaren wareware matsala ta hanyar shawarwari, bisa tushen girmama juna, da zaman daidaito”, matukar ana son warware matsalar.
Muna fatan ganin kasar Amurka ta zama mai sanin ya kamata, da wajabta wa kanta iya sauraron shawara, da daukar mataki mafi dacewa. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bada sanarwan rufe zirga zirgan jiragen sama kwata-kwata a kan sararin samaniyar kasar Venezuel daga yau, a cikin shirinsa na fara mamayar kasar.
Tashar talabijan ta Al-Mayadeen ta kasar Lebanon ta nakalto Trump yana fadar haka a shafinsa na sadarwa True Social. Ya kuma bayyana cewa wannan sako ne ga dukkan kamfanonin jiragen sama da matuka jiragen sama.
Trump ya aika da wannan sakon ne bayanda kasashen Espaniya da Potigal suka bukaci dukkan kamfanonin jiragen sama na kasar da su daina wucewa ta sararin samaniyar kasar Venezuela.
Shugaban ya kara da cewa, sojojinsa a shirye suke su shiga farautar masu safarar miyagun kwayoyi a kasar ta Venezuela, a aikin sojojin kasa a cikin yan kwanaki masu zuwa.
A cikin watan satumban da ya gabata jiragen yakin Amurka sun bude wuta kan kwale-kwale sun fi 10 a tashoshin jiragen ruwa na Venezuela inda mutane kimani 80 suka rasa rayukansu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kamfanin Kera Jiragen Sama Na Airbus Ya Bukaci A Dawo Da Jiragen Sama Samfrin A320 Saboda Gyara November 29, 2025 An Kammala Gasar ‘Rayan’ Na AI Ta Kasa Da Kasa A Nan Tehran November 29, 2025 Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya November 29, 2025 MDD ta yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan kisan gillar da aka yi wa Falasdinawa November 29, 2025 Lebanon ta shigar da kara ga Kwamitin Tsaro bayan Isra’ila ta Gina katanga a Yankinta November 29, 2025 AU ta dakatar da Guinea-Bissau daga zama mamba a cikinta bayan juyin mulkin sojoji November 29, 2025 Najeriya : An yi jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi November 29, 2025 Larijani: Da’awar lalata karfin nukiliyar Iran wauta ce November 29, 2025 Babban banki Najeriya Ya Tura Dala Miliyan 50 Don Ƙarfafa Kasuwar Musayar Kudade November 29, 2025 Iran Da Kasashen Larabawa Sun Yi Tir Da Hare-Haren Isra’ila A Kan Kasar Siriya November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci