Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Bagaei ya bayyana cewa kokari da JMI a tattaunawarta da kasar Amurka kan shirin Nukliyar kasar shi ne ganin an dauke  mata takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata,  ko amurka da dora mata..

Tashar talabjin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran yana fadar haka a jiya, Litinin a lokacinda yake jawabi gay an jaridu a ko wani mako.

Bagaei har ‘ila yau ya tabo al-amuran da suka shafi yankin kudancin Asiya da kuma karya yarjeniyar tsagaita wutan da HKI ta yi a Gaza.

Ya kuma kara da cewa degewa Iran wadanan takunkuman dole ne su kasance mataki na farko don ganin hanyar diblomasiyya ta yi aikinta. Kuma sai da haka ne ake iya fatan za’a cimma wani abu mai muhimmanci a wannan tattaunawar.

Banda haka kakakin ma’aikatar harkokin wajen JMI ya bayyana damuwarsa da yadda gwamnatin HKI take keta yarjeniyar da suka  cimma da kasar Lebanon a cikin watannin da suka gabata. Y ace yahudawan suna keta yarjeniyar 1701 kamar ba’a samar da yarjeniyar ba.

A lokacinda aka tambayeshi dangane da takunkuman Bagaei ya ce, su da kansu ne yakamata su warware, wannan batun, don bai kamata sun a maganar tattaunwa sannan a dayan bangaren kuma suka kara takurawa wanda kuke tattaunawa da shi ba.

Yace Iran ta nuna hakukri da kuma diblomasiyya a cikin wannan al-amarin, kuma Amurka ce yakamata ta nuna cewa tana bukatar tattaunawar tare da daukar matakan da suka dace.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta gayyaci Yusuf Datti Baba-Ahmed, tsohon abokin takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar Labour a zaben 2023 tare da Peter Obi.

DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed ne a daren Juma’a bisa zargin ci gaba da bayyana ra’ayoyi da take ganin na iya tayar da hankali a Najeriya.

Wata majiyar tsaro ta ce DSS ta daɗe tana bibiyar kalaman Baba-Ahmed a kafafen yada labarai, musamman kan iƙirarin da ya yi na cewa akwai “rikicin kundin tsarin mulki” a Najeriya.

A cewar majiyar, “Kwanan nan Datti Baba-Ahmed ya bayyana a talabijin inda ya zargi kotuna da rundunar sojoji da rashin hana rantsar da Shugaba Bola Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima. Har ma ya yi nuni da cewa rantsar da Tinubu ta bai wa sojoji damar cin mutuncin mutane.

Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali CAF ta ƙara yawan ’yan wasan ƙasashe zuwa 28 a gasar nahiyar Afrika

Ta ƙara da cewa irin waɗannan kalamai na iya haifar da tashin hankali a ƙasar, musamman a irin wannan yanayin siyasa da ake ciki.

Ta ce, “Abin damuwa ne ganin yadda irin wannan magana ta janyo rikice-rikice a wasu ƙasashe kamar Guinea-Bissau. Hukumar tsaro tana ɗaukar wannan da muhimmanci, ba don siyasa ba, sai don kare zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.”

A cewar majiyar, DSS ta yi wannan gayyata ne bisa ƙa’ida, saboda kalaman Datti Baba-Ahmed da suka yi kama da raina ƙoƙarin gwamnati wajen inganta tsaro a matsayin “wasa” na iya tayar da hankalin jama’a da kuma rage amincewa da hukumomin ƙasa.

Ta ce, “Wannan gayyatar ba hukunci ba ne, amma matakin kariya ne domin fayyace niyya, da manufar kalamansa a muhallinsu, da kuma hana fitowar labarai da za su iya haifar da rikici ba tare da an yi niyya ba.”

Har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoto, DSS ba ta fitar da wata sanarwa ba, haka kuma Datti Baba-Ahmed bai ce komai a hukumance kan gayyatar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran
  • Shugaban venuzuwela Ya Gargadi Amurka Game Da Kokarin Da Take yi Na Karbe Ikon Kula Da Rijiyoyin Mai Na Kasar
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran.
  • Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
  • Najeriya :  Sojoji sun kubutar da yan mata 12 da mayakan ISWAP
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Yadda ’yan mata ke kufancewa da kasuwancin fara a Kano
  • DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankali
  • Iran Za ta Kauracewa taron fasalta kasashen da za su halarci  gasar cin kofin duniya na shekara ta 2026