Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Bagaei ya bayyana cewa kokari da JMI a tattaunawarta da kasar Amurka kan shirin Nukliyar kasar shi ne ganin an dauke  mata takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata,  ko amurka da dora mata..

Tashar talabjin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran yana fadar haka a jiya, Litinin a lokacinda yake jawabi gay an jaridu a ko wani mako.

Bagaei har ‘ila yau ya tabo al-amuran da suka shafi yankin kudancin Asiya da kuma karya yarjeniyar tsagaita wutan da HKI ta yi a Gaza.

Ya kuma kara da cewa degewa Iran wadanan takunkuman dole ne su kasance mataki na farko don ganin hanyar diblomasiyya ta yi aikinta. Kuma sai da haka ne ake iya fatan za’a cimma wani abu mai muhimmanci a wannan tattaunawar.

Banda haka kakakin ma’aikatar harkokin wajen JMI ya bayyana damuwarsa da yadda gwamnatin HKI take keta yarjeniyar da suka  cimma da kasar Lebanon a cikin watannin da suka gabata. Y ace yahudawan suna keta yarjeniyar 1701 kamar ba’a samar da yarjeniyar ba.

A lokacinda aka tambayeshi dangane da takunkuman Bagaei ya ce, su da kansu ne yakamata su warware, wannan batun, don bai kamata sun a maganar tattaunwa sannan a dayan bangaren kuma suka kara takurawa wanda kuke tattaunawa da shi ba.

Yace Iran ta nuna hakukri da kuma diblomasiyya a cikin wannan al-amarin, kuma Amurka ce yakamata ta nuna cewa tana bukatar tattaunawar tare da daukar matakan da suka dace.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Fira Ministan Pakistan Tare Da Tattaunawa Kan Harin Da Iran Ta Fsukanta

Shugaban kasar Iran ya gana da fira ministan kasar Pakistan

Shugaban kasar Masoud Pezehkian ya gana da fira                             ministan Pakistan Shehbaz Sharif a gefen zaman taron kungiyar hadin kan tattalin arziki ta ECO da Jamhuriyar Azabaijan ta karbi bakunci.

Fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif ya yaba da irin rawar da shugaban kasar Iran ya taka a lokacin da yahudawan sahayuniyya suka kai wa Iran hari tare da tabbatar da goyon bayan Pakistan ga Iran da kuma hada kai da hadin gwiwa da Iran don samar da zaman lafiya a yankin.

Sanarwar da ofishin fira ministan Pakistan ya fitar ta ce: shugaba Masoud Pezehkian ya gana da fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif a gefen zaman taron kungiyar hadin kan tattalin arziki ta ECO da Jamhuriyar Azarbaijan ta dauki nauyi.

Shugaban kasar ta Iran ya isa birnin Khankandi na jamhuriyar Azarbaijan ne a yau Juma’a a domin halartar taron koli na kungiyar hadin kan tattalin arziki ta ECO karo na 17.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba
  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Fira Ministan Pakistan Tare Da Tattaunawa Kan Harin Da Iran Ta Fsukanta
  • “ADC za ta fuskanci matsala wajen zaɓen wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa”
  • Amurka Ta Kakabawa JMI Sabbin Takunkuman Tattalin A Jiya Alhamis
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
  • Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu