Kokarin Da Iran Take A Tattaunawa Da Amurka Shi Ne Dage Mata Takunkuman Zaluncin Da Aka Dora Mata
Published: 15th, April 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Bagaei ya bayyana cewa kokari da JMI a tattaunawarta da kasar Amurka kan shirin Nukliyar kasar shi ne ganin an dauke mata takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata, ko amurka da dora mata..
Tashar talabjin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran yana fadar haka a jiya, Litinin a lokacinda yake jawabi gay an jaridu a ko wani mako.
Ya kuma kara da cewa degewa Iran wadanan takunkuman dole ne su kasance mataki na farko don ganin hanyar diblomasiyya ta yi aikinta. Kuma sai da haka ne ake iya fatan za’a cimma wani abu mai muhimmanci a wannan tattaunawar.
Banda haka kakakin ma’aikatar harkokin wajen JMI ya bayyana damuwarsa da yadda gwamnatin HKI take keta yarjeniyar da suka cimma da kasar Lebanon a cikin watannin da suka gabata. Y ace yahudawan suna keta yarjeniyar 1701 kamar ba’a samar da yarjeniyar ba.
A lokacinda aka tambayeshi dangane da takunkuman Bagaei ya ce, su da kansu ne yakamata su warware, wannan batun, don bai kamata sun a maganar tattaunwa sannan a dayan bangaren kuma suka kara takurawa wanda kuke tattaunawa da shi ba.
Yace Iran ta nuna hakukri da kuma diblomasiyya a cikin wannan al-amarin, kuma Amurka ce yakamata ta nuna cewa tana bukatar tattaunawar tare da daukar matakan da suka dace.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi
Sheikh Ahmad Gumi ya yi martani kan kiraye-kirayen da ake yi na kama shi, inda ya ce masu yin kiran na yi ne domin kawar da rawar da yake takawa wajen magance matsalar ’yan bindiga a Arewa.
Gumi, ya ce duk ganawar da yake yi da ’yan bindiga yana yi ne domin samar da zaman lafiya, kuma hukumomin tsaro sun san da komai.
Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — AkpabioMaganar ta sake fitowa fili ne bayan da ya sake jaddada cewa tattaunawa hanya ce da za ta iya kawo ƙarshen tashin hankali a karkara.
A cikin dogon saƙon da ya wallafa a Facebook a ranar Lahadi, Gumi ya soki masu cewa ya kamata a kama shi saboda ya ganawar da ya yi da shugabannin ’yan bindiga.
Ya bayyana kiran a matsayin don rai la’akari da irin ƙoƙarin da ya yi a baya domin daƙile matsalar tsaro a Arewa.
Ya ce ba shi niyyar goyon bayan masu laifi; kawai yana ƙoƙari rage tashin hankali da kuma shawo kan ’yan bindiga su miƙa wuya.
Gumi, ya ce ya yi muhimmin zama da mahara a Janairun 2021 a dajin Sabon Garin Yadi da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.
Kuma ya ce tare da Kwamishinan ’Yan Sandan Kaduna ya je a lokacin d aka yi ganawar, wanda ya wakilci Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa.
Ya ce taron ya samu halartar ’yan bindiga da shugabanninsu sama da 600, kuma sun yi alƙawarin daina kai hare-hare idan gwamnati ta samar musu da wasu muhimman abubuwa.
“Na je dajin Sabon Garin Yadi tare da Kwamishinan ’Yan Sandan Kaduna.”
“Wannan zama ɓangare ne na aikin samar da zaman lafiya, inda muka yi wa ’yan bindiga sama da 600 da shugabanninsu wa’azi, suka kuma amince za su ajiye makamai idan gwamnati ta samar musu da tsaro da ingantaccen rayuwa,” in ji shi.
Gumi, ya ce duk abin da ya yi bisa ƙa’ida ya yi sa, kuma hukumomi sun san da komai.
Ya ce maimakon mutane su kai su soke shi, kamata ya yi su tambayi dalilin da ya sa gwamnati ba ta yi buƙatun ’yan bindiga ba.
Sheikh Gumi ya kuma tambayi dalilin da ya sa wasu ke son a kama shi, alhali manufarsa ita ce kawo ƙarshen tashin hankali a Najeriya.
“To me zai sa kama ni? Domin na yi kira su ajiye makamai… ko saboda na faɗakar da al’umma game da labarin ’yan bindiga?”.
Gumi ya zargi masu sukarsa da nuna wariya, inda ya tunatar da su cewa kundin tsarin mulki ya bai wa kowa damar faɗin albarkacin bakinsa.
“Shin faɗin ra’ayi ba haƙƙinmu ba ne na kundin tsarin mulki ba? Shin kira da suke yi na a kama ni ba nuna son rai ba ne kuma zai iya haifar da tashin hankali?”.
Ya bayyana cewa buƙatun ’yan bindigar suka nema waɗanda suka haɗa da ababen more rayuwa, kariya daga kame ba bisa ƙa’ida ba, da hanankai musu hari ba idan sun miƙa wuya.
Ya ce babu ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan da aka aiwatar, wanda hakan ya wargatsa tattaunawar.
Gumi, ya ce kamata ya yi mutane su mayar da hankali kan mafita a aikace, ba zagi da fushi ba.