Kokarin Da Iran Take A Tattaunawa Da Amurka Shi Ne Dage Mata Takunkuman Zaluncin Da Aka Dora Mata
Published: 15th, April 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Bagaei ya bayyana cewa kokari da JMI a tattaunawarta da kasar Amurka kan shirin Nukliyar kasar shi ne ganin an dauke mata takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata, ko amurka da dora mata..
Tashar talabjin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran yana fadar haka a jiya, Litinin a lokacinda yake jawabi gay an jaridu a ko wani mako.
Ya kuma kara da cewa degewa Iran wadanan takunkuman dole ne su kasance mataki na farko don ganin hanyar diblomasiyya ta yi aikinta. Kuma sai da haka ne ake iya fatan za’a cimma wani abu mai muhimmanci a wannan tattaunawar.
Banda haka kakakin ma’aikatar harkokin wajen JMI ya bayyana damuwarsa da yadda gwamnatin HKI take keta yarjeniyar da suka cimma da kasar Lebanon a cikin watannin da suka gabata. Y ace yahudawan suna keta yarjeniyar 1701 kamar ba’a samar da yarjeniyar ba.
A lokacinda aka tambayeshi dangane da takunkuman Bagaei ya ce, su da kansu ne yakamata su warware, wannan batun, don bai kamata sun a maganar tattaunwa sannan a dayan bangaren kuma suka kara takurawa wanda kuke tattaunawa da shi ba.
Yace Iran ta nuna hakukri da kuma diblomasiyya a cikin wannan al-amarin, kuma Amurka ce yakamata ta nuna cewa tana bukatar tattaunawar tare da daukar matakan da suka dace.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
Aƙalla mutum shida ne suka rasu, yayin da wasu 13 suka jikkata, bayan wata bas ɗauke da nakasassu ta yi hatsari a kan hanyar Lokoja zuwa Okene.
Waɗanda abin ya shafa suna komawa Okene ne bayan halartar bikin Ranar Nakasassu ta Duniya ta 2025 a Gidan Gwamnatin Jihar da ke Lokoja.
Jirgin fadar shugaban ƙasa ya ƙi sayuwa wata 5 bayan saka shi a kasuwa ’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a YobeAn garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa asibitoci daban-daban a jihar, inda suke ci gaba da samun kulawa.
Kwamishinan Harkokin Sadarwa na Jihar Kogi, Kingsley Femi Fanwo, ya ce wannan hatsari abun baƙin ciki ne ga gwamnati da jama’a.
Ya ce Gwamna Ahmed Usman Ododo ya umarci gwamnatin jihar da ta biya dukkanin kuɗin maganin waɗanda suka jikkata kuma ta tura jami’ai zuwa asibitoci don tallafa wa waɗanda abin ya shafa da iyalansu.
Fanwo ya ce: “Gwamnatin Jihar Kogi tana jimami sosai tare da iyalan waɗanda suka rasu guda shida, kuma za ta tallafa musu.”