’Yan Najeriya sun koka kan rashin ingancin shinkafar Gwamantin Tarayya
Published: 15th, April 2025 GMT
’Yan Najeriya da suka rabauta da sayen shinkafar kasar waje da Gwamnatin Tarayya ta karya farashinsa sun koka bisa rashin ingancin wata wadda ake sayarwa a Jihar Kogi.
Wadanda suka sayi rukunin farko na shinkafar sun yaba da ingancinta da dandanonta, wasu kuma na korafi a kan yanayi da kuma dandanon wadda suka samu daga wani kamfani daga wata kasar Asiya.
Wasu suka samu shinkafar mai matsala sun yi ikirarin samun kwari a cikinta kuma tana yin kumfa idan ana dafa ta, sa’annan idan ta nuna tana yin danko sosai, sabanin yadda aka san shinkafar kasar waje.
Wani dan kasuwar shinkafar cikin gida a Najeriya ya yi zargin rukunin shinkafar da ta samu matsalar ta jima a ajiye ne kafin a fito da ita, shi ya sa ingancin ya samu matsala.
Duk da samun koma baya: Najeriya ce kasa mafi arzikin danyen mai a Afirka —OPEC Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a KanoDon haka ya shawarci masu saya da su shanya ta a rana kuma su wanke ta sosai sa’annan su dan turara ta domin dawo da ingancinta.
A gefe guda kuma wadanda da suka amfana da wani rukuni na daban na shinkafar gwamnatin sun yaba da ingancinta ta fuskar dandano da kuma yanayi.
Kawo yanzu dai hukumomi ba su ce uffan game da korafin da jama’a ke yi kan wannan lamari ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati
এছাড়াও পড়ুন:
Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
Jami’in tafiyar da sha’anin Mulki a yankin Cape ya fada a jiya Laraba cewa; An sami karuwar wadanda su ka rasa rayukansu ya karu zuwa 49.
Shugaban tafiyar da sha’anin Mulki a yankin na garin Cape, Oscar Mobyan ya bayyana haka ne a wani taron manema labaru,kamar yadda kamfanin dillancin labarun Reuters ya nakalto.
Wasu yankuna na kasar ta Afirka Ta Kudu sun fuskanci saukar ruwa kamar da bakin kwarya, haka nan kuma saukar kankara, da hakan ya sa aka shiga cikin yanayin sanyi mai tsanani da kuma yankewar wutar lantarki a wasu yankunan.
Ambaliyar ruwan da aka samu a kusa da wata makaranta ya ja motar da take dauke da dalibai 13, da hakan ya yi sanadiyyar rasuwarsu. Tuni an tsamo gawawwakin dalibai shida,ana kuma ci gaba da neman sauran.
Sauyin yanayin duniya yaa shafi kasar Afirka Ta Kudu, ta yadda a cikin shekarun bayan nan ake yawan samu ambaliyar ruwa. A watan Aprilu na 2022 an yi mamakon ruwa guguwa mai karfi wacce ta ci rayukan kusan mutane 400.