HausaTv:
2025-12-01@02:56:47 GMT

Ministan Harkokin Noma Na Kasar Iran Ya Kama Hanya Zuwa Kasar Brazil

Published: 15th, April 2025 GMT

Ministan harkokin noma na JMI Ghulan Reza Noori Ghezelji ya jagoranci wata tawagar jami’an gwamnatin kasar zuwa kasar Brazil don halattan taron ministocin noma na kungiyar BRICS da kuma tattauna al-amura masu muhimmanci wadanda suka shafi ayyukan noma a duniya.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gwamnatin JMI ta fara aiki a matsayin mamba a kungiyar raya tattalin arziki na kasashen BRICS, wacce ta zama cikekken maba a farkon wannan shekara.

Ta fara aiki tare da sauran kasashen kungiyar wadanda suka kafa ta, wato Brazil, Rasha, India, China,da kuma Afirka ta kudu..

Halattar wannan taron ba kawai zai kara karfin JMI a cikin kungiyar BRICS ba, sai dai zai kara inganta matsayin kasar a fagen noma da abinda ya shafi noma a duniya. Taron  na Brazil zai maida hankali kan aminci samun abinci ga yan kasashen kungiyar da kasuwancinsa a duniya. Da kuma hanyoyin samar da samar da kudade don ayyukan noma duniya.

Daga karshe taron na Brazil zai bayyana jadawalin ayyukan kungiyar dangane da noma a shekara ta 2025.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya sake aike wa Majalisar Dattawa ƙarin sunayen mutum 32 domin tantance su a matsayin jakadu.

Sunayen sun haɗa da manyan mutane kamar tsohon shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Femi Fani-Kayode, da Reno Omokri.

Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe

An raba sunayen zuwa kashi biyu; na farko yana ɗauke da sunan mutum 15 waɗanda suke da gogewar aikin jakadanci da kuma waɗanda ba su gogewar aikin jakadanci mutim 17.

Wasu daga cikin fitattu da suka shiga jerin sun haɗa da tsofaffin gwamnonin kamar Ifeanyi Ugwuanyi da Victor Okezie Ikpeazu, matan tsofaffin gwamnoni kamar Angela Adebayo da Florence Ajimobi, da kuma Sanata Jimoh Ibrahim.

Bayan tantancewa, za a tura jakadun zuwa ƙasashe irin su China, Indiya, Kanada, UAE, Afrika ta Kudu, da Kenya.

Sauran wuraren sun haɗa da manyan cibiyoyi na ƙasa da ƙasa kamar Majalisar Ɗinkin Duniya (UN), UNESCO, da Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).

Za a bayyana inda za a tura kowane, bayan Majalisar Dattawa ta tantance su.

A makon da ya gabata ne, Tinubu ya tura sunayen mutum uku da ake sa ran tura su Amurka, Birtaniya ko Faransa.

Shugaban ya ce za a sake fitar da ƙarin sunayen jakadu nan ba da jimawa ba.

Wannan mataki na cikin shirin Tinubu na karfafa hulɗar diflomasiyya ta hannun ƙwararru da gogaggun mutane don wakiltar Najeriya a ƙasashen waje.

Ana sa ran Majalisar Dattawa za ta fara tantance su cikin makonni masu zuwa, kafin su kama aiki.

Masu sharhi kan sha’anin siyasa suna ganin waɗanda aka zaɓo ƙwararru ne kuma za su taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasar gida da waje.

Da dama na ganin cewa waɗannan naɗe-naɗen za su iya taka rawa wajen tsara sabuwar hanyar hulɗa da ƙasashen waje da manufofin diflomasiyyar Najeriya a nan gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An yi gangami a fadin duniya a zagayowar ranar Falasdinu
  • Hizbullah Ta Bukaci Shugaban Cocin Katolika Na Duniya Yayi Tir Da Hare-haren Isra’ila
  • Iran: Kalaman Da Trump Yayi Na Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venuzuwela Ya Sabama Doka.
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32
  • Iran Ta Kakkabo Jiragen Yakin HKI Fiye Da 196 A Yakin Kwanaki 12
  • Iran Za ta Kauracewa taron fasalta kasashen da za su halarci  gasar cin kofin duniya na shekara ta 2026
  • Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko
  • China Ta Gargadi Amurka Akan Batun Yakar Kasar Venezuela
  • Kungiyar ‘Yan’uwa Musulmi Ta Soki Shirin Donald Trump Na Bayyanata A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka