Ministan Harkokin Noma Na Kasar Iran Ya Kama Hanya Zuwa Kasar Brazil
Published: 15th, April 2025 GMT
Ministan harkokin noma na JMI Ghulan Reza Noori Ghezelji ya jagoranci wata tawagar jami’an gwamnatin kasar zuwa kasar Brazil don halattan taron ministocin noma na kungiyar BRICS da kuma tattauna al-amura masu muhimmanci wadanda suka shafi ayyukan noma a duniya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gwamnatin JMI ta fara aiki a matsayin mamba a kungiyar raya tattalin arziki na kasashen BRICS, wacce ta zama cikekken maba a farkon wannan shekara.
Ta fara aiki tare da sauran kasashen kungiyar wadanda suka kafa ta, wato Brazil, Rasha, India, China,da kuma Afirka ta kudu..
Halattar wannan taron ba kawai zai kara karfin JMI a cikin kungiyar BRICS ba, sai dai zai kara inganta matsayin kasar a fagen noma da abinda ya shafi noma a duniya. Taron na Brazil zai maida hankali kan aminci samun abinci ga yan kasashen kungiyar da kasuwancinsa a duniya. Da kuma hanyoyin samar da samar da kudade don ayyukan noma duniya.
Daga karshe taron na Brazil zai bayyana jadawalin ayyukan kungiyar dangane da noma a shekara ta 2025.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
Dakarun kare juyin juya halin musulunci na kasar Iran ya bayyana cewa makamai masu linzamu na dakarun sun fada kan matatar man fetur na Haifa a HKI har sau biyu a yakin kwanaki 12 da ta fafata da Iran a cikin watan Yunin wannan shekara.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Burgediya Janar Ali Mohammad Naeini kakakin dakarun ya na fadar haka a jiya Lahadi a wani taro, ya kuma kara da cewa makaman har’ila yau sun kashe jami’an hukumar leken asirin HKI MOSAD har 36 a wani hari kan ginin hukumar a cikin yakin.
Naeini, ya kara da cewa HKI ta yi kuskuren lissafi a lokacinda ta farwa kasar Iran da yaki a cikin watan Yunin da ya gabata, tare da tsammanin cewa JMI ba zata iya maida martani ba, saboda rauni, don an kashe manya-manyan kwamandojin sojojin kasar sannan ba zata iya amfani da makamanta na kare dangi ba.
A ranar 13 ga watan Yuni na wannan shekara ne HKI tare da Amurka suka farwa kasar Iran da yaki, da nufin kifar da gwamnatin kasar da kuma kawo karshen shirinta na makamashin nukliya kwata-kwata. Saboda haka ne jiragen yakin Amurka samfurin B2 suka kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin Nukliya na kasar dake Fordo, Natanz da kuma Esfahan.
Naeni ya cewa Iran ta cilla makamai masu linzami har 14 kan sansanin sojojin Amurka mafi girma na Al-Udaid da ke kasar Qatar, sannan yace bisa lissafin Amurkawa kan su sun kashe dalar Amurka miliyon 111 wajen bibiyan inda makaman iran zasu fada.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace December 8, 2025 Iraki Ta Musanta Cewa Ta Tushe Asusun Hizbullah Da Ansarallah December 8, 2025 Sabon Fada Ya Barke A Tsakanin Thailand Da Cambodia December 8, 2025 Iran Ta Yi Allawadai Da Kisan Fararen Hula A Kasar Sudan December 8, 2025 Macron Na Faransa Ya Yi Wa Najeriya Alkawalin Taimakawa Akan Matsalolin Tsaro December 8, 2025 Rasha Ta Yi Maraba Da Cire Sunanta A Matsayin ” Barazanar Da Amurka Teke Fuskanta December 8, 2025 Majid Majidi Na Iran Ya Sami Kyauyar Girmamawa Daga Cibiyar Fina-finai Na “Eurasia Dake Kasar Rasha December 8, 2025 Benin : Har yanzu Shugaba Patrice Talon ne a kan mulkin_fadar shugaban kasa December 7, 2025 Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi) December 7, 2025 Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci