Ministan Harkokin Noma Na Kasar Iran Ya Kama Hanya Zuwa Kasar Brazil
Published: 15th, April 2025 GMT
Ministan harkokin noma na JMI Ghulan Reza Noori Ghezelji ya jagoranci wata tawagar jami’an gwamnatin kasar zuwa kasar Brazil don halattan taron ministocin noma na kungiyar BRICS da kuma tattauna al-amura masu muhimmanci wadanda suka shafi ayyukan noma a duniya.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gwamnatin JMI ta fara aiki a matsayin mamba a kungiyar raya tattalin arziki na kasashen BRICS, wacce ta zama cikekken maba a farkon wannan shekara.
Ta fara aiki tare da sauran kasashen kungiyar wadanda suka kafa ta, wato Brazil, Rasha, India, China,da kuma Afirka ta kudu..
Halattar wannan taron ba kawai zai kara karfin JMI a cikin kungiyar BRICS ba, sai dai zai kara inganta matsayin kasar a fagen noma da abinda ya shafi noma a duniya. Taron na Brazil zai maida hankali kan aminci samun abinci ga yan kasashen kungiyar da kasuwancinsa a duniya. Da kuma hanyoyin samar da samar da kudade don ayyukan noma duniya.
Daga karshe taron na Brazil zai bayyana jadawalin ayyukan kungiyar dangane da noma a shekara ta 2025.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa
Kasar Sin ta bukaci Japan da ta daina yi wa masu fafutukar neman “‘Yancin kan Taiwan”, ingiza mai kantu ruwa, kamar yadda mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Guo Jiakun ya bayyana a yau Laraba.
An ruwaito cewa, gwamnatin Japan a ranar Talata ta ba da wata lambar girmamawa ga tsohon “wakilin Taiwan a Japan” Hsieh Chang-ting.
A martanin da ya mayar game da hakan a wani taron manema labarai, mai magana da yawun ma’aikatar Guo Jiakun ya ce, kasar Sin tana matukar adawa da matakin gwamnatin Japan na ba da lambar girmamawa ga wadanda ke fafutukar “‘yancin kai na Taiwan” kuma yin hakan wani babban kuskure ne da bangaren Japan ke yunkurin tafkawa kan batun da ya shafi yankin Taiwan na kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA