Sojojin kasar Yemen sun kakkabo jirgin yakin Amurka wanda ake sarrafashi daga nesa samfurin MQ-9 na 19 a jiya Lahadi da yamma a sararin samaniyar kasar.

Tashar talabijan ta Presstv daga nan Tehran ya bayyana cewa sojojin kasar ta Yemen sashen UAV wato masu kula da abinda ake kira ‘Drones’ sun bada sanarwan kakkabo jirgin yaki na Amurka ne a lokacinda yake tattara bayanai a wasu yankuna a sararin samaniyar kasar.

Masana sun bayyana cewa farashin ko wane jirgi yakin samfurin MQ-9 ya kai dalar Amurka miliyon $33, don haka ya zuwa yanzu kasar Amurka ta yi asarar dalar Amurka miliyon $600.  Kafin haka dai sojojin Yemen bangaren makamai masu linzami sun bada sanarwan cilla makamai masu linzami samfurin Balistic  guda biyu kan HKI, wanda ya kai ga rufe tashar jiragen sama na Bengerion a birnin Yafa (telaviv.) . Bugediya Yahyah Saree kakakin sojojin kasar ta Yemen ya bayyana cewa godiya ta tabbata ga All..saboda dukkan makaman sun cimma manufofin cillasu, wadanda suka hada da rufe tashar jiragen sama na Bengrion da tilastawa miliyoyin yahudawan sahyoniyya gudu zuwa wuraren buya.

Saree ya kammala da cewa, ayyukan soje a kan HKI da kuma Amurka zasu ci gaba har zuwa dakatar da yaki a Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi

Gwamnatin Jihar Bauchi, ta ƙaryata zargin cewa Gwamna Bala Mohammed na shirin ficewa daga PDP zuwa jami’yyar PRP.

Jita-jitar ta samo asali ne bayan Sakataren jam’iyyar PRP na Bauchi, Hon. Wada Abdullahi, ya ce ba za su karɓi gwamnan zuwa jami’yyarsu ba.

Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky

Ya ce gwamnan bai cika ƙa’idojin da PRP ke buƙata ba a shugabancinsa a Bauchi.

Amma mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin yaɗa labarai, Mukhtar Gidado, ya ce gwamnan bai taɓa tunanin barin PDP ba.

Ya ce babu wata tattaunawa ko mataki da aka ɗauka na komawa PRP.

Gidado, ya ce gwamnan na aiki ne wajen ƙarfafa PDP kuma ya taɓa doke PRP a zaɓuka da suka gabata.

Ya ƙara da cewa Jihar Bauchi ta samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnan, musamman a ɓangaren tallafa wa jama’a, ababen more rayuwa, ci gaban ƙauyuka, da yawon buɗe ido.

Gwamnatin ta soki PRP kan yaɗa jita-jita marasa tushe.

Ya ce gwamnan na da ’yancin zaɓar makomarsa a harkokin siyasa, amma duk wata shawara da zai ɗauka ba za ta kasance bisa ƙarya ko jita-jita ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Amurka ta matsa lamba a kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan: Reuters