Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
Published: 14th, April 2025 GMT
Sojojin kasar Yemen sun kakkabo jirgin yakin Amurka wanda ake sarrafashi daga nesa samfurin MQ-9 na 19 a jiya Lahadi da yamma a sararin samaniyar kasar.
Tashar talabijan ta Presstv daga nan Tehran ya bayyana cewa sojojin kasar ta Yemen sashen UAV wato masu kula da abinda ake kira ‘Drones’ sun bada sanarwan kakkabo jirgin yaki na Amurka ne a lokacinda yake tattara bayanai a wasu yankuna a sararin samaniyar kasar.
Masana sun bayyana cewa farashin ko wane jirgi yakin samfurin MQ-9 ya kai dalar Amurka miliyon $33, don haka ya zuwa yanzu kasar Amurka ta yi asarar dalar Amurka miliyon $600. Kafin haka dai sojojin Yemen bangaren makamai masu linzami sun bada sanarwan cilla makamai masu linzami samfurin Balistic guda biyu kan HKI, wanda ya kai ga rufe tashar jiragen sama na Bengerion a birnin Yafa (telaviv.) . Bugediya Yahyah Saree kakakin sojojin kasar ta Yemen ya bayyana cewa godiya ta tabbata ga All..saboda dukkan makaman sun cimma manufofin cillasu, wadanda suka hada da rufe tashar jiragen sama na Bengrion da tilastawa miliyoyin yahudawan sahyoniyya gudu zuwa wuraren buya.
Saree ya kammala da cewa, ayyukan soje a kan HKI da kuma Amurka zasu ci gaba har zuwa dakatar da yaki a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bukaci Mutanen Yemen Su Daina Kashe Juna
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Baghaei ya gargadi mutanen kasar Yemen daga kungiyoyi daban daban da su yi kokarin sasantawa a tsakaninsu, saboda ci gaba ta yakar juna yana taimakawa HKI ne kawau.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Baghaei ya na fadar haka a yau Lahadi a cikin wani bayanin da ya watsa a shafinda na X.
Ya kara da cewa a cikin yan makonnin da suka gabata yan bindiga wadanda suke samun goyon bayan saudia sun fara yaki da sojojin Gwamnatin Yemen a kudancin kasar mai arzikin man fetur da nufin tada hankali a kasar.
Wasu kafafen yada labarai suna maganar cewa kudancin kasar Yemen zata shelanta bellewarta daga arewacin kasar nan ba da dadewa ba.
Baghaei ya bayyana cewa dukkan wadan nan al-amura suna faruwa ne a cikin shirin HKI na sake tsara kasashen yammacin Asiya. Kuma shi yasa bata barin wata kasa daga kasashen yankin ta ci gaba da zaman lafiya ba.
Daga karshen ya bukaci kungiyoyi daban-daban a kasar ta Yemen su yi kokarin sasantawa a tsakaninsu kada su ci gaba da aiki wa yahudawa ta hanyar rarraba kansu da kuma zubar da jinanensu don amfanin yahudawa.
Yayi kira ga gwamnatin kasar Yemen ta yi kokarin sasantawa da sauran Kabilun kasar don dawo da zaman lafiya a kasar. Duk wanda bai son zaman lafiya shi ne wanda yake khidima wa makiyan kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Tayi Tir Da Hare-Haren Sydney Na Kasar Austaralia December 14, 2025 Sudan: Makaman ‘Drones’ Sun Kashe Ma’aikatan MDD 6 A Kadugli Na Kurdufan Ta Kudu December 14, 2025 Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD) December 14, 2025 َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja December 14, 2025 Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha December 14, 2025 Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan. December 14, 2025 Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai December 14, 2025 Ghana Ta Kori Wasu Yahudawa Guda 3 Don Mayar Da Martani December 14, 2025 Araghchi ya bukaci Amurka ta girmama al’ummar Iran da gwamnatinta December 14, 2025 Dan bindiga ya kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula a Siriya December 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci