Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
Published: 14th, April 2025 GMT
Sojojin kasar Yemen sun kakkabo jirgin yakin Amurka wanda ake sarrafashi daga nesa samfurin MQ-9 na 19 a jiya Lahadi da yamma a sararin samaniyar kasar.
Tashar talabijan ta Presstv daga nan Tehran ya bayyana cewa sojojin kasar ta Yemen sashen UAV wato masu kula da abinda ake kira ‘Drones’ sun bada sanarwan kakkabo jirgin yaki na Amurka ne a lokacinda yake tattara bayanai a wasu yankuna a sararin samaniyar kasar.
Masana sun bayyana cewa farashin ko wane jirgi yakin samfurin MQ-9 ya kai dalar Amurka miliyon $33, don haka ya zuwa yanzu kasar Amurka ta yi asarar dalar Amurka miliyon $600. Kafin haka dai sojojin Yemen bangaren makamai masu linzami sun bada sanarwan cilla makamai masu linzami samfurin Balistic guda biyu kan HKI, wanda ya kai ga rufe tashar jiragen sama na Bengerion a birnin Yafa (telaviv.) . Bugediya Yahyah Saree kakakin sojojin kasar ta Yemen ya bayyana cewa godiya ta tabbata ga All..saboda dukkan makaman sun cimma manufofin cillasu, wadanda suka hada da rufe tashar jiragen sama na Bengrion da tilastawa miliyoyin yahudawan sahyoniyya gudu zuwa wuraren buya.
Saree ya kammala da cewa, ayyukan soje a kan HKI da kuma Amurka zasu ci gaba har zuwa dakatar da yaki a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wang Yi Ya Ce Kasar Sin Za Ta Magance Cin Zarafin Da Amurka Ke Yi Ita Kadai
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana cewa, kasar Sin za ta ci gaba da magance cin zarafin da Amurka ke yi ita kadai, ba wai kawai don kare hakki da moriyarta ba, har ma da kiyaye moriyar kasashen duniya. Ya bayyana hakan ne a jiya Jumma’a yayin ganawarsa da takwaransa na kasar Tajikistan Sirojiddin Muhriddin.
Ministocin harkokin wajen kasashen biyu sun yi musayar ra’ayoyi kan batutuwan da suka shafi harajin kwastam yayin da suka hadu a birnin Almaty domin halartar taron ministocin harkokin wajen kasashen tsakiyar Asiya da kasar Sin karo na shida.
Wang, ya nanata cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da dukkan bangarori domin tabbatar da gudanar da kasuwanci cikin ‘yanci, da nuna adawa da kariyar cinikayya, da kare daidaito da adalci a duniya.
Yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Uzbekistan Bakhtiyor Saidov, duk dai a wannan ranar, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da kasashe masu ra’ayi iri daya, wajen kiyaye damawa da kowa da kowa, da kare daidaito da adalci, da kuma nuna adawa da kariyar cinikayya. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp