Sojojin kasar Yemen sun kakkabo jirgin yakin Amurka wanda ake sarrafashi daga nesa samfurin MQ-9 na 19 a jiya Lahadi da yamma a sararin samaniyar kasar.

Tashar talabijan ta Presstv daga nan Tehran ya bayyana cewa sojojin kasar ta Yemen sashen UAV wato masu kula da abinda ake kira ‘Drones’ sun bada sanarwan kakkabo jirgin yaki na Amurka ne a lokacinda yake tattara bayanai a wasu yankuna a sararin samaniyar kasar.

Masana sun bayyana cewa farashin ko wane jirgi yakin samfurin MQ-9 ya kai dalar Amurka miliyon $33, don haka ya zuwa yanzu kasar Amurka ta yi asarar dalar Amurka miliyon $600.  Kafin haka dai sojojin Yemen bangaren makamai masu linzami sun bada sanarwan cilla makamai masu linzami samfurin Balistic  guda biyu kan HKI, wanda ya kai ga rufe tashar jiragen sama na Bengerion a birnin Yafa (telaviv.) . Bugediya Yahyah Saree kakakin sojojin kasar ta Yemen ya bayyana cewa godiya ta tabbata ga All..saboda dukkan makaman sun cimma manufofin cillasu, wadanda suka hada da rufe tashar jiragen sama na Bengrion da tilastawa miliyoyin yahudawan sahyoniyya gudu zuwa wuraren buya.

Saree ya kammala da cewa, ayyukan soje a kan HKI da kuma Amurka zasu ci gaba har zuwa dakatar da yaki a Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Petro: Man fetur shine burin Amurka a Venezuela ba yaki da fataucin kwayoyi ba

Yayin da ayyukan sojin Amurka ke karuwa a yankin Caribbean da Pasifik, shugaban kasar Colombia Gustavo Petro ya zargi gwamnatin Trump da yin amfani da matsin lamba kan kasar Venezuela da sunan yaki da fataucin muggan kwayoyi a matsayin hujjar samun damar shiga kasar don mamaye  albarkatun man fetur da Allah ya huwace wa kasar.

Man fetur shine tushen al’amarin, Petro ya fadawa CNN a cikin wata hira ta musamman, yana mai cewa Venezuela ita ce kasar da tafi kowace kasa yawan danyen ma a duniya.

“Saboda haka, wannan batun baki dayansa a kan man fetur ne. Na yi imani cewa (Shugaban Amurka Donald Trump) na tunanin yadda zai samu mai a kasar Venezuela ne ba batun dimokiradiyya ko yaki da fataucin miyagun ƙwayoyi ba ne, “in ji shi.

Petro ya bayar da hujjar cewa man fetur na Venezuela ya kasance a sahun gaba game da manufofin Amurka. Ya bayyana cewa kadan ne kawai na cinikin magunguna a duniya ke bi ta kasar Venezuela kuma ba a daukar kasar a matsayin babbar mai samar da su.

A ranar Talata, Petro ya zargi Amurka da yunkurin dawo da wani sabon mulkin mallaka a kan kasashen latin.

Da yake mayar da martani, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Amurka ya ce gwamnatin Trump za ta ci gaba da ayyukanta na yaki da muggan kwayoyi a yankin Caribbean da kuma jajircewarta na kare Amurkawa daga abin da ya kira mummunar gubar gwamnatin Maduro.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tarayyar Afirka ta yi Allah wadai da juyin mulkin a Guinea-Bissau November 28, 2025 Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi November 27, 2025 Iran ta yi tir da Australiya kan alakanta IRGC, da mai tallafawa ta’addanci November 27, 2025 Ramaphosa ya soki Trump kan hana shi halartar taron G20 na badi November 27, 2025 ECOWAS ta yi Allah wadai da juyin mulki a Guinea Bissau November 27, 2025 Faransa, Jamus, Italiya, da Burtaniya sun yi tir da “karuwar rikici” a yammacin kogon jodan November 27, 2025 Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci November 27, 2025 Palasdinawa Sun Karbi Gawawwakin Shahidai 15 Daga ‘Yan Mamaya November 27, 2025 Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon  Dake Takawa Makiya Birki November 27, 2025 Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump zai haramta wa ’yan Najeriya da wasu ƙasashe zuwa Amurka
  • Jagoran : Amurka Tasha Kashi A Yakin Kwanaki 12 Duk Da Manyan Makamai Na Zaman Da Take Da Su.
  • Isra’ila Na Barazanar Sake Shiga Wani Sabon Yaki Da Kasar Lebanon
  • Petro: Man fetur shine burin Amurka a Venezuela ba yaki da fataucin kwayoyi ba
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Sojojin Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar  Guinea Bissau
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Uganda: An Kama Fiye Da ‘Yan Hamayyar Siyasa 300 A Lokacin Yakin Neman Zabe
  • An haramta cin naman Kare da Kyanwa a Indonesia