HausaTv:
2025-09-17@23:11:45 GMT

Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran

Published: 13th, April 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Makiya suna cike da takaici da fushi kan ci gaban da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take samu

A yayin ganawarsa da manyan kwamandojin sojojin kasar Iran a yau Lahadi, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa; Ci gaban da Iran ta samu ya fusata da kuma kara takaicin masu mugun nufi kan lasar ta Iran.

Yana mai bayyana cewa, tabbas akwai rauni a fannonin da suka shafi tattalin arziki da ya kamata a magance.

Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya yi la’akari da cewa; Sojojin kasar suna matsayin kariya ta al’umma da kuma mafakar al’umma daga duk wani mai wuce gona da iri, sannan kuma ya jaddada wajibcin ci gaba da bunkasa shirye-shirye da kayan aiki da tsare-tsare don sauke wannan nauyi na kasa. Ya kara da cewa: Ci gaban da kasar ta samu ya fusata da kuma kara takaicin masu adawa da Iran, kuma ko shakka babu akwai raunin da ya faru a fannonin da suka shafi tattalin arziki da babu shakka akwai bukatar a magance shi. Jagoran ya bayyana shirye-shiryen kayan aikin sojojin a matsayin ma’ana inganta karfin makamansu da inganta tsarin su da kuma yadda suke rayuwa. Ya kara da cewa, “Bugu da ƙari, shirye-shiryen kayan aiki, shirye-shirye ne na gudanar da tsare-tsare – wato imani da manufa da sako da kuma tabbatar da halaccin hanyar – wadanda suke da matukar muhimmanci, kuma akwai ƙoƙari na makiya na neman murguda su.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: shirye shirye

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno

Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.

Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala

A cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.

“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).

“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.

Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato