HausaTv:
2025-11-05@17:53:01 GMT

Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran

Published: 13th, April 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Makiya suna cike da takaici da fushi kan ci gaban da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take samu

A yayin ganawarsa da manyan kwamandojin sojojin kasar Iran a yau Lahadi, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa; Ci gaban da Iran ta samu ya fusata da kuma kara takaicin masu mugun nufi kan lasar ta Iran.

Yana mai bayyana cewa, tabbas akwai rauni a fannonin da suka shafi tattalin arziki da ya kamata a magance.

Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya yi la’akari da cewa; Sojojin kasar suna matsayin kariya ta al’umma da kuma mafakar al’umma daga duk wani mai wuce gona da iri, sannan kuma ya jaddada wajibcin ci gaba da bunkasa shirye-shirye da kayan aiki da tsare-tsare don sauke wannan nauyi na kasa. Ya kara da cewa: Ci gaban da kasar ta samu ya fusata da kuma kara takaicin masu adawa da Iran, kuma ko shakka babu akwai raunin da ya faru a fannonin da suka shafi tattalin arziki da babu shakka akwai bukatar a magance shi. Jagoran ya bayyana shirye-shiryen kayan aikin sojojin a matsayin ma’ana inganta karfin makamansu da inganta tsarin su da kuma yadda suke rayuwa. Ya kara da cewa, “Bugu da ƙari, shirye-shiryen kayan aiki, shirye-shirye ne na gudanar da tsare-tsare – wato imani da manufa da sako da kuma tabbatar da halaccin hanyar – wadanda suke da matukar muhimmanci, kuma akwai ƙoƙari na makiya na neman murguda su.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: shirye shirye

এছাড়াও পড়ুন:

Uba Sani Ya Kaddamar Da Gidaje 100 Ga Waɗanda Rikici Ya Shafa A Jihar

Gwamnatin Kaduna Da Hadin Gwiwar UINL Da FHFL Sun Gina Gidaje 100 Ga Mutanen Da Rikici Ya Raba Da Muhallans

Daga Abdullahi Shettima

Gwamnatin Jihar Kaduna tare da haɗin gwiwar kamfanin Ummi International Nigeria Ltd (UINL) da Family Homes Funds Ltd (FHFL), bisa tallafin Ma’aikatar Tsare-tsare da Kasafin Kuɗi ta Tarayyar Najeriya, sun kammala ginin gidaje 100 domin mutanen da rikici ya raba da muhallansu da kuma marasa galihu a cikin jihar.

Wannan aiki ya gudana ne a yankin Rigachikun, inda kamfanin Ummi International Nigeria Ltd ya bayar da fili, yayin da Gwamnatin Kaduna, Family Homes Funds, da Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsare suka ɗauki nauyin ginin gidajen gaba ɗaya.

A yayin ƙaddamar da ginin da kuma miƙa ma waɗanda za su zauna, Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayyana cewa aikin ya samo asali ne daga kudirin gwamnatinsa na taimaka wa waɗanda suka rasa matsuguninsu sakamakon rikice-rikice, tare da dawo musu da martabar rayuwa.

Gwamna Uba Sani ya ce wannan aiki yana cikin shirin gwamnatin jihar na inganta walwalar marasa galihu da tabbatar da ci gaban da ya shafi kowa a fadin jihar.

A nasa jawabin, Ministan Ma’aikatar Tsare-tsare da Kasafin Kuɗi, Sanata Atiku Bagudu, ya yabawa wannan haɗin gwiwa tare da tabbatar da cewa ma’aikatar za ta ci gaba da yin aiki tare da kamfanoni masu zaman kansu da kungiyoyin agaji domin cimma burin ci gaba mai ɗorewa.

Ita kuma tsohuwar Ministar Mata ta Tarayyar Najeriya, Dame Pauline Tallen, ta bayyana ginin a matsayin wani muhimmin aiki na alheri wanda zai taimaka wajen farfaɗo da rayuwar zawarawa, marayu da sauran masu buƙata a cikin al’umma.

A nata bangaren, Dr. Umma Sani (Zinariyar Gabasawar Zazzau), shugabar kamfanin Ummi International Nigeria Ltd, ta bayyana cewa gidauniyarta ta dade tana gudanar da irin wannan aiki na samar da matsuguni ga zawarawa da marayu domin inganta rayuwar su kamar sauran jama’a.

Ta kuma gode wa Gwamna Uba Sani bisa cikakkiyar gudunmawar da ya bayar wajen ganin an samu wannan nasara, tare da bayyana shi a matsayin shugaba mai kishin al’umma da tausayi.

Haka kuma Ambasada Dr. Fatima Mohammed Goni, shugabar Global Business Network Initiative (GBNI), ta bayyana Dr. Umma Sani a matsayin abin koyi ga mata a Najeriya, la’akari da yadda ta ke aiwatar da ayyukan jin kai don tallafa wa mabukata.

Ta kuma yi kira ga wadanda suka amfana da gidajen da su kula da su da kyau, domin tabbatar da dorewar manufar da aka samar da su saboda ta alheri ce ta gaskiya.

Taron ƙaddamarwar ya gudana ne a yau Litinin, inda ya sami halartar manyan baki, jami’an gwamnati, da wakilan kungiyoyi masu zaman kansu daga sassa daban-daban na Jihar Kaduna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zan ci gaba da siyasa har ƙarshen rayuwata – Shekarau
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Farmaki Ga Wani Dan Majalisa A Jihar Niger
  • Ayatollah Khamenei: Rikici Tsakanin Iran da Amurka na asasi
  • Khatibzadeh: Shirin Nukiliya na Iran ya fi bayyana a duniya
  • Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya
  • Karuwanci da zubar da cikin ’yan mata ’yan gudun hijira ya karu a Maiduguri
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yayi Maraba Da Kalaman Da Hukumar IAEA Ta yi Kan Shirin Nukuliyarta
  • Uba Sani Ya Kaddamar Da Gidaje 100 Ga Waɗanda Rikici Ya Shafa A Jihar
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Da Tasirin Shirin NG-CARES A Jihar Jigawa
  • Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso