Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
Published: 14th, April 2025 GMT
Wani babban jami’in Diblomasiyya na kasar Iran ya bada sanarwan cewa zagaye na biyu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka za’a gudanar da shi ne a kasashen Turai a ranar 19 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2025.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin ministan harkokin waje na JMI kan al-amuran da suka shafi siysa Majid Takht-Ravabchi yana fadar haka a jiya Lahadi a lokacinda yake gabatarwa Majalisar dokokin kasar Iran rahoto kan taron tawagar Amurka da kuma JMI a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.
Jami’in diblomasiyyar ya kara da cewa, a tattaunawar da ba kai tsaye ba tsakanin kasashen biyu a ranar Asabar da ta gabata yayin kokarin gano, wuri guda wanda zasu iya tsayawa a kansa don gina tattaunawar a kansa. Takht-Ravanchi ya nakalto tawagar gwamnatin Amurka na cewa da gaske suke a tattaunawar, kuma basa neman yaki da kasar Iran, banda haka a shirye suke su saurari korafe korafe gwamnatin JMI. A ranar Asabar da ta gabace ministan harkokin wajen kasar Amurka da wakilin kasar Amurka a harkokin gabas ta tsakiya Steve Witkoff suka gudanar da zagaye na farko a tsakanin kasashen biyu a birnin Mascat na kasar Omman. Tashar talabijin ta Al-Manar ta kasar Lebanon ta nakalto shafin yanar gizo na larabarai na Axion na fadar cewa taro nag aba zai kasance a birni Roma na kasar Italiya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Ta Kai Wa Sojojin MDD Hari A Kasar Lebanon
Tankar yakin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta bude wuta akan dakarun zaman lafiya na MDD dake kudancin Lebanon
Dakarun zaman lafiyar na MDD dake kudancin Lebanon (UNIFiL) sun sanar da cewa tankar yakin “Isra’ila” ta buder wuta akansu, da hakan ya tilasta musu guduwa zuwa inda za su buya.
Rundunar ta “UNIFIL” ta kuma bayyana abinda ya faru da cewa keta kudurin MDD ne mail amba 1701, tare da yin kira ga “Isra’ila’ da ta dakatar da abinda take yi.
Wannan dai ba shi ne karon farko ba da dakarun zaman lafiyar na MDD suke keta kudurin MDD ta hanyar kai hare-hare da kuma yin kutse a cikin yankunan dake kan iyaka.
A ranar 27 ga watan Oktoba ma dai rundunar ta MDD ta sanar da cewa ta harbo wani jirgin sama maras matuki na Haramtacciyar Kasar Isra’ila da ya rika shawagi akan sojojinta masu sintiri da zummar kai musu hari. Haka nan kuma a waccan ranar wani jirgin saman maras matuki na “Isra’ila” ya jefa bom a kusa da dakarun a garin Kafar-kalla.
A baya a ranar 12 ga watan Oktoba wani jirgin na “Isra’ila” da ya jefa bom, ya jikkata daya daga cikin dakarun zaman lafiyar na MDD.
An kafa rundunar UNFEL ne dai a 1978 bayan da sojojin Haramtacicyar Kasar Isra’ila su ka kutsa cikin kudancin Lebanon, an kuma karfafa ayyukan rundunar a 2006 da fitar da kuduri 1701. Da akwai sojoji 10,000 akarkashin wannan rundunar domin sa ido akan dakatar da yaki daga Isra’ila da kuma karfafa sojojin Lebanon a kudancin tafkin “Litani”.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya November 16, 2025 Kasar Afghanistan Na Kokarin Karkata Akalar Kasuwancinta Zuwa Iran November 16, 2025 Kanada Ta Tsare Tsohon Wakilin Majalisar Dinkin Duniya Mai Bincike Kan Laifukan Yakin Israila. November 16, 2025 Zarfi: HKI Ce Kawai Take Ayyana Nukiliya Ba Bisa Kaida Ba A Yammacin Asiya. November 16, 2025 Shugaban kasar venuzuwela Yayi Tir Da Atisayan Soji Da Trinidad and Tobago Ke yi. November 16, 2025 IRGC ta kama wani jirgin ruwan dakon mai a gabar tekun kudancin Makran November 16, 2025 Iran : sojojin Amurka a yankin Caribbean barazana ne ga zaman lafiya November 16, 2025 Lebanon za ta kai karar Isra’ila a MDD kan gina Katanga a iyakarta November 16, 2025 AU ta sake watsi da ikirarin Trump cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya November 16, 2025 Falasdinu ta yi wasan sada zumunci a Spain November 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci