Gwamnatin Amurka ta sanar da cewa: Ba ta neman tada tashin hankali tsakaninta da Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Samuel Werberg ya bayyana cewa: Kasarsa ba ta neman kara ruruta wutar rikici da Iran, yana mai jaddada cewa har yanzu kofar diflomasiyya a bude take, duk kuwa da kakkausar murya da Amurka ta yi na kin amincewa Iran ta mallaki makamin nukiliya.

Werberg ya kara da cewa; Za su ci gaba da riko da siyasar matsin lamba da nufin dakatar da ci gaba a shirin nukiliyar Iran.

Kakakin na Amurka ya bayyana cewa, “Dole ne Iran ta nuna kyakkyawar niyyarta kafin ta yi magana kan duk wata nasara da za a samu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba

Shugaban hukumar makamashin Nukliya na kasar Iran Mohammad Islami ya bayyana cewa, kasar zata ci gaba a fannonin ilmi guda 6 na fasahar nukliya wato Fission, Fussion, Lasers, fasahar Quantum, da kuma Plasma duk tare da barazanar yaki, ko na siyasa ko kuma yakin kwakwalwan da makiya suke wa kasar.

Yace, matsayin  JMI a bayyana yake, kan cewa ba zata daina aikin ci gaba a fannonin ilmin makamashin nukliya don samun ci gaba a bangarorin kiwon lafiya da magunguna ba da wasu bangarorin ci gaba ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Islami yana fadar haka, a wani bukin kaddamar wasu sabbin kayakin aikin wadanda aka samar a cikin gida wadanda suka hada da ‘Plasma-Based drug synthesis da kuma wani sabon na’ura na jinyar gulando da fasahar Plasma jets.

A ranar 22 ga watan yunin da ya gabata ne gwamnatin kasar Amurka ta kaddamar da hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar Iran dake Fordo, Natanz da kuma Esfahan da kawo karshen shirin a kasar, sannan ta yi haka ne a dai dai lokacinda Iran take tattaunawa da ita.

Muhammad Islami ya karada cewa kasar Iran zata ci gaba wajen bunkasa ilmin masu amfani ga kasar ba tare da wata matsala ba, ya ce, luguden wuta a kan cibiyoyin nukliyar kasar ba zasu tsada wannan ci gaban ba, haka ma yaki da takurawa ta tattalin arziki, siyasa da sauransu.

Yace mutanen kasar Iran ba zasu ci gaba da zama masu sayan ilmi daga waje ba. Musamman ilmomi masu muhimmanci ga ci gaban mutanemmu a wannan zamanin.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026 December 12, 2025  Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi Akan Doron Ruwa December 12, 2025 Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi da dama December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu   December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • MDD ta amince da wani kuduri da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agaji a Gaza   
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince da Sama da Naira Biliyan 2.6 Domin Aikin Hajjin 2026
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Yadda za ku cike neman aikin dan sandan Najeriya na 2025/2026