Gwamnatin Amurka ta sanar da cewa: Ba ta neman tada tashin hankali tsakaninta da Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Samuel Werberg ya bayyana cewa: Kasarsa ba ta neman kara ruruta wutar rikici da Iran, yana mai jaddada cewa har yanzu kofar diflomasiyya a bude take, duk kuwa da kakkausar murya da Amurka ta yi na kin amincewa Iran ta mallaki makamin nukiliya.

Werberg ya kara da cewa; Za su ci gaba da riko da siyasar matsin lamba da nufin dakatar da ci gaba a shirin nukiliyar Iran.

Kakakin na Amurka ya bayyana cewa, “Dole ne Iran ta nuna kyakkyawar niyyarta kafin ta yi magana kan duk wata nasara da za a samu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi)

Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya tabbatar da cewa har yanzu Amurka ba ta nuna sha’awarta ta shiga “tattaunawa mai ma’ana ba,” yana mai sake nanata cewa dole ne Washington ta fara amincewa da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya na zaman lafiya a karkashin Yarjejeniyar hana yaduwar Makaman Nukiliya ta (NPT).

A wata hira ta musamman da aka yi da kamfanin dillancin labarai na Japan Kyodo a ranar Asabar, ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa an kaiwa cibiyoyin nukiliya na Jamhuriyar Musuluncihari da bama-bamai, wanda ya lalata su sosai” a lokacin harin Isra’ila da Amurka a watan Yuni.

Araghchi ya jaddada cewa wadannan hare-haren sun kasance “wataƙila mafi girman keta dokokin kasa da kasa” da aka taba yi wa wata cibiya da Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) ke sa ido a kai.

Ministan harkokin wajen na Iran ya ce Jamhuriyar Musulunci da IAEA sun cimma yarjejeniya a birnin Alkahira a farkon wannan shekarar da zata duba wuraren da suka lalata.

Duk da haka, wannan tsari ya shiga cikin matsala lokacin da Amurka da kasashen Turai uku da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar nukiliya ta 2015 suka nemi a dawo da takunkumin da Majalisar Tsaron Majalisar Dinkin Duniya ta sanya wa Iran a baya.

Babban jami’in diflomasiyyar Iran ya kara da cewa babbar matsalar ita ce rashin amincewar Washington da ‘yancin Iran na mallakr fasahar nukiliya ta zaman lafiya, gami da wadatarwa, a karkashin NPT.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hamas : ‘’Babu batun kwance damarar makamai matuƙar Isra’ila ta ci gaba da mamaya’’ December 7, 2025 Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila December 7, 2025 Masar : ba za mu bari a yi amfani da iyakar Rafah ba don korar Falasdinawa December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168 December 7, 2025 Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167 December 7, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 166 December 7, 2025 Rwanda Da Amurka Sun Rattaba Hannu Kan Tallafin Dalar Amurka Miliyon $228 Na Kiwon Lafiya December 7, 2025 Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba December 7, 2025 Iran Ta Gargadi Kasashen Larabawa Dangane Da Tsibiran Kasar Guda Uku A cikin Tekun Farisa December 7, 2025 Hamas Tace Zata Mikawa Gwamnatin Falasdinawa Makamanta Idan An Kawo Karshen Mamaya December 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dole ne Amurka ta amince da ‘yancin Iran na samar da makamashin nukiliya cikin lumana (Araghchi)
  • Iran : sabbin dabarun tsaron Amurka cimma maradun Isra’ila
  • Amurka: Mun Yi Kokarin Kifar Da Gwamnatin JMI Har Sau Biyu Ba Tare Da Samun Nasara Ba
  • Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu
  • Gwamnatin Iraki Ta Kore Saninta Da Shigar Da Sunayen Hizbullah Da “Ansarullah” A Cikin Na ‘Yan Ta’adda
  • Limamin Tehran:  Idan Abokan Gaba Su Ka  Sake Yin Kuskure Akan Iran Za Su Sake Cin Kasa
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC
  • Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
  • Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania