HausaTv:
2025-12-13@03:34:31 GMT

Fadar Mulkin Amurka: Tattaunawa Da Iran Ta Yi Armashi

Published: 13th, April 2025 GMT

Fadar mulkin Amurka ta “White Hosue” ta bayyana cewa tattaunawar da aka yi a tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci  da wakilin Donald Trump akan gabas ta tsakiya Steve Witkoff, ta hanyar shiga tsakanin kasar Oman, ta yi armashi.

Da marecen jiya Steve Witkoff ya bayyana cewa; shugaba Donald Trump ya ba shi umarnin ya yi duk abinda zai iya domin rage tazarar sabanin da ake da ita ta hanyar tattaunawa da diflomasiyya.

Bayanin na fadar mulkin Amurka ya kuma yaba wa kasar Oman wacce ta kasance mai masaukin baki na tattaunawar da aka yi wacce ba ta gaba da gaba ba ce a tsakanin Amurkan da kuma Iran.

Gabanin bayanin na fadar mulkin Amurkan, manzon musamman na shugaba Donald Trump, Steve Witkoff ya fada wa tashar talabijin din NBC cewa, ya yi tattaunawa mai matukar armashi da kuma amfani.

Tun a ranar Asabar da safe ne dai ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci ya isa birnin Mascut, inda ya gana da takwaransa na kasar Sayyid Hamad Bin Hamud al-Busa’idi, tare da mika masa bayanai da su ka kunshi mahangar Iran akan tattaunawar.

Ministan na harkokin wajen Oman ya zama mai shiga tsakanin kasashen biyu a tsawon lokacin tattaunawar. Bangarorin biyu sun yi musayar takardu har sau hudu.

A ranar Asabar mai zuwa ne dai za a ci gaba da tattaunawar daga inda aka tsaya a wani wurin da ba a kai ga ayyana shi ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan

Gwamnatin kasar Iran ta yi kakkausar suka ga kasashen duniya wadanda suka rage yawan kudaden da suke bayarwa don tallafawa yan gudun hijira daga kasar Afganisatan a cikin kasar Iran.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto jakadan kasar Iran a MDD Amir Saeed Iravani yana fadar haka a jawabinda ya gabatar a taron kwamitin tsaro na MDD dangane da kasar ta Afganistan a jiya Laraba.

Iravani ya kara da cewa a halin yanzun Iran tana ci gaba da daukar bakwncin yan gudun hijiran Afganisatan fiye da miliyon 6 wanda ya hada da da shi da shansu da karatun yayansu da kuma tallafin da gwamnatin kasar take bayarwa na gidajen zamansu da ruwa da wutan lanatarki. Wanda a halin yanzu tana kashe akalla dalar Amurka billion $1o don yin hakan.

Kafin haka dai kwamitin tsaro na majalisar ya tsaida shawarar rage kashe 65% na kudaden da take bawa kasar Iran dangane da yan gudun hijiran Afganistan fiye da miliyon 6 da suke zama a kasar a shekara mai zuwa wato 2026.

Iravani ya musanta zancen tsohon jakafan Amurka a Zalmay Khalilzad wanda ke cewa ai Iran ta kore mafi yawan yan gudun hijiran Afganisatan a kasar. Ya ce wadanda Iran ta kora sune wadanda suka  shiga kasar ba tare da takardun shaida ba. Wannan kuma an amince da shi a ko ina a duniya.  

Iravani ya bayyana cewa, wannan matakin ya sabawa al-kawalin da kasashen duniya suka dauka na daukan nauyin yan gudun hijira a duniya. Ba zasu bar nauyin a kan kasa guda ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5  December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi AkanDoron Ruwa
  • Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama
  • Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan
  • Amurka ta matsa lamba a kan kotun ICC don janye bincike kan yakin  Gaza da Afghanistan: Reuters
  • Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran