Fadar Mulkin Amurka: Tattaunawa Da Iran Ta Yi Armashi
Published: 13th, April 2025 GMT
Fadar mulkin Amurka ta “White Hosue” ta bayyana cewa tattaunawar da aka yi a tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci da wakilin Donald Trump akan gabas ta tsakiya Steve Witkoff, ta hanyar shiga tsakanin kasar Oman, ta yi armashi.
Da marecen jiya Steve Witkoff ya bayyana cewa; shugaba Donald Trump ya ba shi umarnin ya yi duk abinda zai iya domin rage tazarar sabanin da ake da ita ta hanyar tattaunawa da diflomasiyya.
Bayanin na fadar mulkin Amurka ya kuma yaba wa kasar Oman wacce ta kasance mai masaukin baki na tattaunawar da aka yi wacce ba ta gaba da gaba ba ce a tsakanin Amurkan da kuma Iran.
Gabanin bayanin na fadar mulkin Amurkan, manzon musamman na shugaba Donald Trump, Steve Witkoff ya fada wa tashar talabijin din NBC cewa, ya yi tattaunawa mai matukar armashi da kuma amfani.
Tun a ranar Asabar da safe ne dai ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci ya isa birnin Mascut, inda ya gana da takwaransa na kasar Sayyid Hamad Bin Hamud al-Busa’idi, tare da mika masa bayanai da su ka kunshi mahangar Iran akan tattaunawar.
Ministan na harkokin wajen Oman ya zama mai shiga tsakanin kasashen biyu a tsawon lokacin tattaunawar. Bangarorin biyu sun yi musayar takardu har sau hudu.
A ranar Asabar mai zuwa ne dai za a ci gaba da tattaunawar daga inda aka tsaya a wani wurin da ba a kai ga ayyana shi ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa
Aƙalla mutum shida ne suka jikkata bayan da wani rikici ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyen Kangire da ke Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa.
Ishak Ibrahim Fanini, mai taimaka wa shugaban Ƙaramar Hukumar Birnin Kudu, Muhammad Uba, ya tabbatar da faruwar lamarin a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook.
Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano DSS ta gayyaci Datti Baba-Ahmed kan zargin kalaman tayar da hankaliA cewarsa, an zargi makiyaya da shigar da dabbobinsu cikin gonakinsu wasu manoma.
Wannan ya haddasa faɗa tsakanin manoma da makiyayan.
Ya ƙara da cewa shugaban Ƙaramar Hukumar ya gudanar da taron sulhu tsakanin ɓangarorin biyu, inda ya gargaɗi su kan tayar da rikici a yankin.
Wannan sabon rikici ya faru makonni kaɗan bayan irin wannan ya auku a watan Oktoba, inda mutane uku suka mutu sakamakon rikicin manoma da makiyaya a Ƙaramar Hukumar Birniwa.
Rikicin manoma da makiyaya ya zama babban matsala a Jigawa da sauran yankunan Arewa.
Masana sun ce wannan rikici na yawan faruwa ne saboda matsalolin muhalli, tsadar rayuwa.
Sun bayyana cewa sauyin yanayi da yaɗuwar hamada a Arewacin Sahel sun tilasta wa makiyaya da dama yin ƙaura don ciyar da dabbobnsu.
Sai dai shigarsu yankunan da ake noma a Jigawa, ya haifar da rikici saboda lalata gonaki.