Fadar Mulkin Amurka: Tattaunawa Da Iran Ta Yi Armashi
Published: 13th, April 2025 GMT
Fadar mulkin Amurka ta “White Hosue” ta bayyana cewa tattaunawar da aka yi a tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci da wakilin Donald Trump akan gabas ta tsakiya Steve Witkoff, ta hanyar shiga tsakanin kasar Oman, ta yi armashi.
Da marecen jiya Steve Witkoff ya bayyana cewa; shugaba Donald Trump ya ba shi umarnin ya yi duk abinda zai iya domin rage tazarar sabanin da ake da ita ta hanyar tattaunawa da diflomasiyya.
Bayanin na fadar mulkin Amurka ya kuma yaba wa kasar Oman wacce ta kasance mai masaukin baki na tattaunawar da aka yi wacce ba ta gaba da gaba ba ce a tsakanin Amurkan da kuma Iran.
Gabanin bayanin na fadar mulkin Amurkan, manzon musamman na shugaba Donald Trump, Steve Witkoff ya fada wa tashar talabijin din NBC cewa, ya yi tattaunawa mai matukar armashi da kuma amfani.
Tun a ranar Asabar da safe ne dai ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci ya isa birnin Mascut, inda ya gana da takwaransa na kasar Sayyid Hamad Bin Hamud al-Busa’idi, tare da mika masa bayanai da su ka kunshi mahangar Iran akan tattaunawar.
Ministan na harkokin wajen Oman ya zama mai shiga tsakanin kasashen biyu a tsawon lokacin tattaunawar. Bangarorin biyu sun yi musayar takardu har sau hudu.
A ranar Asabar mai zuwa ne dai za a ci gaba da tattaunawar daga inda aka tsaya a wani wurin da ba a kai ga ayyana shi ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta kori Wike, Fayose, Anyanwu da wasu
Jam’iyyar PDP ta kori Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, tsohon gwamnan Jihar Ekiti, Ayodele Fayose da tsohon sakataren jam’iyyar na ƙasa, Samuel Anyanwu.
PDP ta yanke wannan hukunci ne a babban taron jam’iyyar da ake gudanarwa a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.
Gwamnati, UNICEF da ’yan jarida sun haɗa don yaƙar cututtukan da aka manta da su a Gombe Sanusi II ne kaɗai halastaccen Sarki a Kano — KwankwasoTsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na yankin Kudu, Cif Olabode George ne, ya gabatar da ƙudirin korarsu, sannan Samaila Burga, shugaban PDP na Jihar Bauchi, ya mara masa baya.
A baya, tsagin jam’iyyar da ke goyon bayan Wike sun kai ƙara kotu don a hana gudanar da taron.
Amma PDP ta samu hukuncin da ya ba ta damar ci gaba da taron daga Kotun Ƙoli ta Jihar Oyo.
Kwana biyu kafin taron, Mao Ohuabunwa, Shugaban Majalisar Amintattu (BoT) na ɓangaren Wike, ya ce duk wanda ya tafi Ibadan don taron hutu ya je yi, domin doka ba za ta aminta da shi ba.
A cewarsa, Anyanwu ya riga ya fitar da sanarwar ɗage taron.
Ohuabunwa ya ce: “Mun zauna a matsayin kwamitin zartarwa na ƙasa na PDP, muka duba abubuwan da muka yi. Mun yadda da bin hukuncin kotu game da taron Ibadan. Don haka ba mu da hannu a taron.
“Ibadan wurin jama’a ne, mutane na iya zuwa don kowane abu amma ba don babban taro ba. Duk wanda ya tafi can da sunan taro ya ɗauki hakan a matsayin shaƙatawa kawai.
“Ba za mu amince da take haƙƙin kundin tsarin mulki da wasu mutanen ke yi da sunan babban taro ba.”
Muƙaddashin shugaban tsagin, Abdulrahman Muhammad, shi ma ya kira wakilansu da su guji zuwa taron.
Ya ce tsagin nasu zai ci gaba da haɗa kan mambobi a jihohi 36 da Abuja domin ƙarfafa jam’iyyar.
Muhammad ya ce: “Muna kiran dukkanin wakilai su guji zuwa taron Ibadan.”
A nasa jawabin, Wike ya gode wa mambobin jam’iyyar saboda yadda suke tsayawa wajen kare jam’iyyar a yankunansu.
Ya ce su a ɓangarensu za su ci gaba da bin doka kuma ba za su bari a tsoratar da su ba.
Wike, ya kuma ce ba zai taɓa yaudarar waɗanda ke goyon bayan kundin tsarin mulkin jam’iyyar ba.
Ya ce: “Ina farin ciki da yadda kuke nuna damuwa game da jam’iyyar a yankunanku. Zan ci gaba da goyon bayanku, ba zan yaudare ku ba.”