HausaTv:
2025-12-14@03:56:25 GMT

Fadar Mulkin Amurka: Tattaunawa Da Iran Ta Yi Armashi

Published: 13th, April 2025 GMT

Fadar mulkin Amurka ta “White Hosue” ta bayyana cewa tattaunawar da aka yi a tsakanin ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci  da wakilin Donald Trump akan gabas ta tsakiya Steve Witkoff, ta hanyar shiga tsakanin kasar Oman, ta yi armashi.

Da marecen jiya Steve Witkoff ya bayyana cewa; shugaba Donald Trump ya ba shi umarnin ya yi duk abinda zai iya domin rage tazarar sabanin da ake da ita ta hanyar tattaunawa da diflomasiyya.

Bayanin na fadar mulkin Amurka ya kuma yaba wa kasar Oman wacce ta kasance mai masaukin baki na tattaunawar da aka yi wacce ba ta gaba da gaba ba ce a tsakanin Amurkan da kuma Iran.

Gabanin bayanin na fadar mulkin Amurkan, manzon musamman na shugaba Donald Trump, Steve Witkoff ya fada wa tashar talabijin din NBC cewa, ya yi tattaunawa mai matukar armashi da kuma amfani.

Tun a ranar Asabar da safe ne dai ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci ya isa birnin Mascut, inda ya gana da takwaransa na kasar Sayyid Hamad Bin Hamud al-Busa’idi, tare da mika masa bayanai da su ka kunshi mahangar Iran akan tattaunawar.

Ministan na harkokin wajen Oman ya zama mai shiga tsakanin kasashen biyu a tsawon lokacin tattaunawar. Bangarorin biyu sun yi musayar takardu har sau hudu.

A ranar Asabar mai zuwa ne dai za a ci gaba da tattaunawar daga inda aka tsaya a wani wurin da ba a kai ga ayyana shi ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya

Amurka ta kama wani katafaren jirgin ruwan dakon man Najeriya kan zargin safarar ɗanyen mai na sata.

Jami’an tsaron Amurka sun kama jirgin mai suna Super Tanker, mai lamba 9304667, ne, bayan sun gano cewa ya yi basaja, inda ya maƙala tutar wata kasa daban maimakon ta Najeriya yayin shigarsa ruwan Amurka.

Wannan ya haifar da shakku kan sahihancin jirgin da ma wadanda ke tafiyar da shi. Daga bisani kuma aka gano cewa ba ya cikin tsarin jiragen da ake tsammani a hukumance.

Hukumomin Amurka sun ƙaddamar da bincike kan jirgin, wanda ake hasashen zai bankaɗo badaƙalar safarar man sata da fataucin miyagun ƙwayoyi da ayyukan ’yan fashin teku da ke shafar ƙasashe da dama.

An shafe shekaru ana magana ba kan matsalar yawan satar ɗanyen mai ayankin Neja Delta mai arzikin mai ya zame wa al’umma tamkar tamkar masifa.

Bayanan kama jirgin

Jirgin mallakin wani babban ɗan kasuwa a Najeriya mai kamfanin Thomarose Global Ventures, yanzu haka yana tsare a hannun jami’an tsaron Amurka.

Bayanan farko sun nuna cewa an fara gudanar da bincike kan alakar jirgin da safarar muggan ƙwayoyi da kuma harkokin barayin kan teku, musamman a zirin Tekun Gunea da ke addabar kasashe da dama, ciki har da Najeriya, Kamaru, Sao Tome da Ghana.

Alƙaluman da aka fitar a watan Nuwamba, shekarar 2025, sun nuna cewa Najeriya ta yi asarar kimanin dala biliyan 300 sakamakon satar ɗanyen mai a ciki da wajen kasar.

Wannan satar mai ba wai kawai tana jawo asarar kudi ba, har ma tana barin baya da kurar gurbata muhalli, lamarin da ke ci gaba da kassara yankin mai arzikin mai na Niger Delta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa
  • DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Amince Ya Ziyarci Beirut
  • Islami: Yaki Ba Zai Hana Iran Ci Gaba A Shirinta Na Makamashin Nukliya Ba
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama
  • Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan