Aminiya:
2025-04-30@19:08:24 GMT

Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro

Published: 13th, April 2025 GMT

Wata mata mai suna Jennifer Castro ta shigar da ƙarar kamfanin jiragen sama na GOL da wata fasinja a kotu bisa wani faifan bidiyo aka wallafa da yake nuna matar ta ki barin kujerarta da ke kusa da taga saboda wani yaro da yake kuka.

Matar ’yar ƙasar Brazil da ta ƙi barin kujerar kusa da taga saboda wani yaro mai kuka ta shigar da ƙara a kotu.

Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato

Jennifer Castro, mai shekara 29 na daukar matakin shari’a a kan kamfanin jiragin sama na GOl da kuma fasinjar da ta ɗauki bidiyonta a lokacin da lamarin ya faru.

Lamarin wanda aka yi ta yadawa ta intanet, ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a.

A cewar jaridar The New York Post, Castro na tuhumar kamfanin jirgin da kuma matar da ya nadi musayar takaddamar da suka yi, inda ta nemi diyya kan halin kunci da barnar da lamarin ya haifar mata.

Ta bayyana cewa, matakin da ta ɗauka na shigar da ƙarar shi ne don hana afkuwar irin wannan abin kunya ga jama’a a nan gaba.

Al’amarin ya ja hankalin jama’a saboda yada lamarin a kafafen sada zumunta.

Da take bayani a kan shari’ar, Castro ta ki bayyana adadin diyyar da take nema.

Ta ce, tana son hana irin wannan tozarta jama’a da abin da ta kira fallasa ba tare da izini ba a nan gaba.

Hakan na zuwa ne bayan da aka bayar da rahoton cewa, a watan da ya gabata ta fara “tunanin” daukar matakin shari’a.

Castro ta bayyana cewa, “tun bayan faruwar wannan lamarin, rayuwata ta shiga wani yanayi da ban taba tunanin sa ba.”

“Abin da ya kamata ya kasance kawai jirgin zirgazirgar na yau da kullun ya sauya zuwa wani abun kunya, yana fallasa ni da rashin adalci da haifar da sakamakon da ya shafi rayuwata ta sirri da ta sana’a.

Ni ce ake so na yanke hukunci a kan takaddama da hasashen mutanen da ba su ma san cikakken labarin ba.”

Castro ta ce lamarin ya fara ne a lokacin da take hawa jirgi, sai ta hangi wani yaro a zaune a lambar kujerar da ya kamata ta zauna.

Tunda ta riga ta zabi wurin zama na kusa da taga, Castro ta yi tsammanin yaron zai koma wani wurin zaman na daban.

“Na jira shi yadda ya kamata, amma ya kwantar da kansa a wata kujerar, sannan sai na zauna a kujerata ,” in ji ta.

Lamarin ya ta’azzara lokacin da wata ta fara daukar bidiyon Castro ba tare da izininta ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yaro

এছাড়াও পড়ুন:

An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas

Wata tsohuwa mai shekara 80 a kasar Turkiyya za ta shafe sama da shekara 4 a gidan yari, saboda ta daki jikarta ’yar shekara 18 da silifa a lokacin da suke takaddama.

Asiye Kaytan na zaune tare da jikarta Vural a unguwar Topraklık da ke Denizli a Kudu maso Yammacin Turkiyya.

Tuntuni dai iyayen yarinyar suka rabu, inda tsohuwar mai shekara 80 take kulawa da ita fiye da kanta.

A ranar 9 ga Agustan bara, bayan Vural ta dawo daga aiki, ta fada wa kakarta cewa, za ta fita waje tare da wasu abokanta.

Tsohuwar ta ji tsoron fitar don kare lafiyarta, ta ce ba za ta yarda ba, har ma ta kulle kofa don tabbatar da cewa Vural ba ta iya fita ba.

Zuwa wani lokaci, sai budurwar ta yi kokarin bude kofar, inda Kaytan ta dauko takalmi silifas, ta dake ta.

Vural ta rama dukan da kakarta ta yi mata a ka da wayarta. Kaytan ta fara zubar da jini, inda yarinyar ta kira motar asibiti.

“Jikata ta so fita da yamma, amma na hana ta, na kulle kofa,”

Kaytan ta shaida wa jaridar Sabah News. “Na buge ta a hannu da silifas, sai ta buge ni da wayarta a ka. Lokacin da na fara zubar da jini, sai ta tsorata ta kira motar daukar marasa lafiya.”

Kaytan da jikarta ba su kai kara a kan junansu ba, amma sun bayyana wa wadanda suka amsa da farko yadda tsohuwar ta samu rauni a ka, inda suka kai rahoto a asibitin Jihar Denizli, wanda daga baya aka mika wa ’yan sandan yankin.

An gayyaci matan biyu domin amsa tambayoyi, kuma duk da bayyana cewa sun sasanta rikicin nasu kuma sun yi sulhu, sai aka buɗe ƙofar ƙarar jama’a, kuma ofishin mai shigar da kara na gwamnati ya shigar da karar kakar mai shekara 80.

A shari’ar tasu, masu gabatar da kara sun yi zargin cewa, silifas da Kaytan ta yi amfani da shi wajen dukan jikarta makami ne, kuma yarinyar ’yar shekara 18 ta yi kokarin kare kanta ne a lokacin da ta bugi kakarta da wayarta.

An kuma tuhumi kakar da tauye ’yancin dan-adam saboda ta kulle Vural a cikin gidanta tare da hana ta fita, zargin da zai iya kai ga hukuncin daurin shekaru 14 a gidan yari.

A ranar 25 ga watan Fabrairu ne kotun hukunta manyan laifuka ta 12 ta kasar ta yanke wa Asiye Kaytan hukuncin daurin shekaru 2 da wata 6 a gidan yari saboda laifin ‘tauye ’yancin dan-adam ta hanyar amfani da karfi ko barazana ko yaudara da kuma ƙarin shekaru 2 da watanni 6 kan amfani da “makami” wajen aikata laifin da ta yi wa jikarta.

Daga ƙarshe an rage hukuncin zuwa shekaru 4 da watanni 2, amma lauyan Kaytan ya ɗaukaka ƙara kan hukuncin.

Idan kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin da aka yanke mata, za ta je gidan yari.

“Zan shiga kurkuku ina da shekara 80? Ta yaya zan zauna a can? An yi mini tiyata, kuma ina tafiya da kyar, za su saka ni a kurkuku saboda silifas,” tsohuwar ta yi kuka.

‘‘Babu wanda ya isa ya daki yaronsa da silifas saboda ana daukar sa a matsayin makami. Ba ni da masaniyan cewa silifas ya zama makami’’, in ji ta. “

An yi wa kakata hukuncin zaman gidan yari ne saboda ta doke ni da silifas, ta hana ni fita daga gidan. Ban so haka ta kasance ba, ban kai karar ta ba, amma an bude karar jama’a,” in ji Asiye Vural.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka
  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi