Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
Published: 13th, April 2025 GMT
Wata mata mai suna Jennifer Castro ta shigar da ƙarar kamfanin jiragen sama na GOL da wata fasinja a kotu bisa wani faifan bidiyo aka wallafa da yake nuna matar ta ki barin kujerarta da ke kusa da taga saboda wani yaro da yake kuka.
Matar ’yar ƙasar Brazil da ta ƙi barin kujerar kusa da taga saboda wani yaro mai kuka ta shigar da ƙara a kotu.
Jennifer Castro, mai shekara 29 na daukar matakin shari’a a kan kamfanin jiragin sama na GOl da kuma fasinjar da ta ɗauki bidiyonta a lokacin da lamarin ya faru.
Lamarin wanda aka yi ta yadawa ta intanet, ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a.
A cewar jaridar The New York Post, Castro na tuhumar kamfanin jirgin da kuma matar da ya nadi musayar takaddamar da suka yi, inda ta nemi diyya kan halin kunci da barnar da lamarin ya haifar mata.
Ta bayyana cewa, matakin da ta ɗauka na shigar da ƙarar shi ne don hana afkuwar irin wannan abin kunya ga jama’a a nan gaba.
Al’amarin ya ja hankalin jama’a saboda yada lamarin a kafafen sada zumunta.
Da take bayani a kan shari’ar, Castro ta ki bayyana adadin diyyar da take nema.
Ta ce, tana son hana irin wannan tozarta jama’a da abin da ta kira fallasa ba tare da izini ba a nan gaba.
Hakan na zuwa ne bayan da aka bayar da rahoton cewa, a watan da ya gabata ta fara “tunanin” daukar matakin shari’a.
Castro ta bayyana cewa, “tun bayan faruwar wannan lamarin, rayuwata ta shiga wani yanayi da ban taba tunanin sa ba.”
“Abin da ya kamata ya kasance kawai jirgin zirgazirgar na yau da kullun ya sauya zuwa wani abun kunya, yana fallasa ni da rashin adalci da haifar da sakamakon da ya shafi rayuwata ta sirri da ta sana’a.
Ni ce ake so na yanke hukunci a kan takaddama da hasashen mutanen da ba su ma san cikakken labarin ba.”
Castro ta ce lamarin ya fara ne a lokacin da take hawa jirgi, sai ta hangi wani yaro a zaune a lambar kujerar da ya kamata ta zauna.
Tunda ta riga ta zabi wurin zama na kusa da taga, Castro ta yi tsammanin yaron zai koma wani wurin zaman na daban.
“Na jira shi yadda ya kamata, amma ya kwantar da kansa a wata kujerar, sannan sai na zauna a kujerata ,” in ji ta.
Lamarin ya ta’azzara lokacin da wata ta fara daukar bidiyon Castro ba tare da izininta ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yaro
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
An tabbatar da mutuwar mutum ɗaya, tare da ƙona gidaje sama da 100, wanda ake zargin wasu makiyaya ne a unguwannin manoma da ke Ƙaramar hukumar Karim Lamido a Jihar Taraba suka yi.
An kai wa mazauna unguwar Bandawa Gwenzu, waɗanda suka haɗa da: Gwenzu da Langwanshin da Danzhan hari a daren Laraba.
Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a BornoDa yake magana da tashar Talabijin na Channels TV ta wayar tarho a ranar Alhamis, shugaban matasan Uunguwar yankin, Ishaya Peter ne ya bayyana harin a matsayin rashin gaskiya da abu mai muni kuma ya yi Allah-wadai da harin.
A cewarsa, mazauna garin na zaune suna tattaunawa, kwatsam sai suka ji ƙarar harbe-harbe daga nesa lamarin da ya sanya suka yi gaggawar gudu domin tsira da rayukansu.
Ya ce, ya ji muryoyin makiyaya tare da wasu maƙwabtansu da ke tunkarar ƙauyen, kuma duk yunƙurin hana su ya ci tura.
Peter ya ce sun bayar da sanarwar gargaɗi na sa’o’i kafin su kai harin ga hukumomin tsaro, amma ba a ɗauki matakin daƙile faruwar lamarin ba.
Ba za mu iya daƙile harin ba saboda sun zo da bindigogi kuma mu mutane ne masu son zaman lafiya ba mu da makami sai baka da kibiya, abin yankar ciyawa shi ke nan,” inji shi.
“Ɗaya daga cikinmu ya mutu ne dalilin rashin iya yin iyo a lokacin da yake tsallaka kogi, yayin da suka far mana, ƙauyukan ba kowa ne kuma har yanzu muna ƙirga asarar da muka yi.
“An buƙaci mata da yara da su ƙauracewa ƙauyukan saboda ba mu san lokacin da za su sake kai farmaki ba.”
Rundunar ‘yan sandan Jihar Taraba ba ta mayar da martani kan wannan sabon harin ba.
Idan dai za a iya tunawa, a cikin watan Mayun wannan shekara ne makamancin wannan lamari ya faru a yankin na Bandawa, wanda ya yi sanadin mutuwar mutum uku tare da jikkata wasu da dama.