Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
Published: 13th, April 2025 GMT
Wata mata mai suna Jennifer Castro ta shigar da ƙarar kamfanin jiragen sama na GOL da wata fasinja a kotu bisa wani faifan bidiyo aka wallafa da yake nuna matar ta ki barin kujerarta da ke kusa da taga saboda wani yaro da yake kuka.
Matar ’yar ƙasar Brazil da ta ƙi barin kujerar kusa da taga saboda wani yaro mai kuka ta shigar da ƙara a kotu.
Jennifer Castro, mai shekara 29 na daukar matakin shari’a a kan kamfanin jiragin sama na GOl da kuma fasinjar da ta ɗauki bidiyonta a lokacin da lamarin ya faru.
Lamarin wanda aka yi ta yadawa ta intanet, ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a.
A cewar jaridar The New York Post, Castro na tuhumar kamfanin jirgin da kuma matar da ya nadi musayar takaddamar da suka yi, inda ta nemi diyya kan halin kunci da barnar da lamarin ya haifar mata.
Ta bayyana cewa, matakin da ta ɗauka na shigar da ƙarar shi ne don hana afkuwar irin wannan abin kunya ga jama’a a nan gaba.
Al’amarin ya ja hankalin jama’a saboda yada lamarin a kafafen sada zumunta.
Da take bayani a kan shari’ar, Castro ta ki bayyana adadin diyyar da take nema.
Ta ce, tana son hana irin wannan tozarta jama’a da abin da ta kira fallasa ba tare da izini ba a nan gaba.
Hakan na zuwa ne bayan da aka bayar da rahoton cewa, a watan da ya gabata ta fara “tunanin” daukar matakin shari’a.
Castro ta bayyana cewa, “tun bayan faruwar wannan lamarin, rayuwata ta shiga wani yanayi da ban taba tunanin sa ba.”
“Abin da ya kamata ya kasance kawai jirgin zirgazirgar na yau da kullun ya sauya zuwa wani abun kunya, yana fallasa ni da rashin adalci da haifar da sakamakon da ya shafi rayuwata ta sirri da ta sana’a.
Ni ce ake so na yanke hukunci a kan takaddama da hasashen mutanen da ba su ma san cikakken labarin ba.”
Castro ta ce lamarin ya fara ne a lokacin da take hawa jirgi, sai ta hangi wani yaro a zaune a lambar kujerar da ya kamata ta zauna.
Tunda ta riga ta zabi wurin zama na kusa da taga, Castro ta yi tsammanin yaron zai koma wani wurin zaman na daban.
“Na jira shi yadda ya kamata, amma ya kwantar da kansa a wata kujerar, sannan sai na zauna a kujerata ,” in ji ta.
Lamarin ya ta’azzara lokacin da wata ta fara daukar bidiyon Castro ba tare da izininta ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yaro
এছাড়াও পড়ুন:
An Bayyana Sunayen Kasashen Da Su Fi Sayarwa “Isra’ila” Man Fetur A Lokacin Yakin Gaza
Kungiyar “Oil Change International” mai zaman kanta ta bayyana cewa da akwai kasashe 25 da su ne su ka rika sayar wa da “Isra’ila” man fetur a tsawon lokacin yakin Gaza.
Rahoton wannan jaridar ya yi ishara da kasashe 25 da su ne madogarar Haramtacciyar Kasar Isra’ila” wajen samun makamashin da ta rika amfani da shi a motocinta nay akin Gaza.
Jaridar “al-Ahbar” wacce ta buga wannan rahoton da kungiyar “ Oil Change International” mai zaman kanta ta watsa a yayin taron da ake yin a muhalli a kasar Brazil, ta ce; Kasashen Azerbaijan da kuma Kazakhstan ne a gaba da su ka bai wa ‘yan sahayoniya kaso70% na man fetur din da motocinsu na yaki su ka rka amfani da su tun daga watan Oktoba 2023 zuwa2025.
Rahoton ya kuma ce, wadannan kasashen biyu suna da cikakkiyar masaniya akan cewa man fetur din da suke bai wa Haramtacciyar Kasar Isra’ila za a yi amfani da shi ne a yakin Gaza.
A dalilin hakan, kungiyar ta yi kira ga wadannan kasashen da su yi furuci da cewa da su aka yi laifukan yaki a Gza, musamman yi wa mutane kisan kare dangi.
Tun a farkon yakin ne dai kungiyar ta “Oil Change International” ta bai wa kamfanin tattara bayanai na “Data Disk” kwangiyar bibiyar yadda ake jigilar man fetur zuwa Haramtacciyar kasar ta Yahudawa. Kamfanin kuwa ya iya gano an yi jigilar man fetur din har sau 323, da nauyinsa ya kai miliyan 21.1.
Bayan wadannan kasashen biyu da akwai kasashen Rasha, Girka da Amurka a cikin jerin wadanda suke bai wa Haramtacciyar Kasar ta Yahudawa man fetur.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka MDD: Mutane 100,000 Ne Su Ka Fice Daga Birnin Al-Fasher Na Kasar Sudan November 15, 2025 Jakadan Iran A Majalisar Dinkin Duniya Yace Iran Ba za Ta Taba Mika Wuya Ga Duk Wata Barazana Ba November 15, 2025 Kasashen Latin Amurka Sun Shirya Tsaf Don Mayar Da Martani Kan Wuce Gona Da Irin Amurka Kan Venuzuwela November 15, 2025 Rasha Tace Bata Da Shirin Kai wa Kungiyar Nato Hari Amma Za ta Mayar Da Martani Kan Duk Wata Barazana November 15, 2025 Shugaban Iran Da Prime Ministan Iraqi Sun Tattaunawa Kan Batun Zabe Da Kuma Alakar Dake Tsakaninsu. November 15, 2025 M D D Ta yi Tir Da Harin Da Yahudawa Yan Share Wuri Zauna Suka Kai A Masallaci A Yammacin kogin Jodan November 15, 2025 Mali ta Dakatar da Tashoshin Talabijin na Faransa TF1 da LCI November 15, 2025 Gaza: Amurka na matsin lamba ga kwamitin tsaro don amincewa da shirin Trump November 15, 2025 AU da MDD, sun karfafa dabarun tabbatar da zaman lafiya da tsaro November 15, 2025 Iran ta bukaci duniya ta gaggauta daukar mataki a Sudan November 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci