Jiragen Yakin Kasar Amurka Suna Rusa Cibiyoyin Ilmi A Hare-Haren Da Suke Kaiwa Kasar Yemen
Published: 13th, April 2025 GMT
Jiragen yakin Amurka sun kai sabbin hare-hare kan wasu yankunan a kasar Yemen a safiyar a jiya Asabar, wadanda suka Baida Sa’ada da kuma Hudaidah wadanda sune sake zafafa yaki a ciki kasar na baya-bayan nan.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kafafen yada labarai na kasar ta Yemen na fadar cewa jiragen yakin kasar ta Amurka sun kai hare-hare har 5 a kan makarantar koyon sana’o’ii na Al-sawma da ke lardin Al-Bayda a jiya Asabar .
Labarin ya kara da cewa makarantar ita ce babbar makaranta a yankin, kuma cibiyar ilmi mafi girma. Har’ila yau labarin ya bayyana cewa jiragen yakin kasar ta Am,urka sun kai hare-hare har guda 3 a kan garin Al-Sahleen daga cikin yankunan Kitif da kuma Al-Bogee daga cikin lardin Sa’ada.
Labarin ya kara da cewa wannan yankin yana daga cikin yankunan da ake fafatawa da sojojin Amurka, kuma suna yawaita kan hare-hare a cikinsa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Siriya Zata Samar Da Huldar Jakadanci Da HKI A Dai-Dai Lokacinda Ya Dace
Shugaban rikon kwarya na kasar Siriya Ahmed Al-sharaa ya bayyana cewa gwamnatinsa a shirye take ta samar da hulda da HKI a dai-dai lokacinda ya dace.
Jaridar Middle East Eye ta kasar Burtaniya ta nakalto Ahmed Sharaa yana fadar haka a wata wasikar da ya rubutawa shugaba Donal Trump
Har’ila yau shugaba Al-sharaa ya fadawa wani dan majalisar dokokin kasar Amurka kan cewa gwamnatinsa zata samar da huldar jakadanci da HKI a lokacinda ya dace, sannan a bangaren kasar Siriya kuma tana bukatar da farko a dagewa kasar takunkuman da aka dora mata, sannan yana son a yi maganar yankunan kasar Siriya wadanda HKI ta mamaye bayan juyin mulkin da aka yi a kasar.
Dan majalisar dokokin kasar ta Amurka Cory Mills na hannun daman Trump ya ziyarci kasar Siriya a makon da ya gabata inda ya gana da shugaban, na kimani minti 90, don tattaunawa wadannan al-amura
Mill dai wanda ziyarci kasar ta tare naukar nauyin yan kasar Siriya a Amurka ya bayyana kamfanin dillancin labaran Bloomberg kan cewa ya fadawa shugaban matakan da yakamata ya dauka don ganin an daukewa kasar takunkuman tattalin arziki.
Ya kuba bukaci shugaban wargaza sauran masana’antun makaman guba a kasar, ya shiga cikin kasashen yankin masu yaki da ayyukan ta’addanci, ya kuma san yadda zai yi da yan kasashen waje wadanda suke cikin HTS, wanda suka taimaka masa ya sami damar kifar da gwamnatin Bashar al-asad. Sannan dole ne ya amintar da HKI kan cewa ba zai kai mata hari ba.