Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto
Published: 11th, April 2025 GMT
Gwamnatin jihar Sokoto ta tabbatar da samun ɓullar cutar sanƙarau guda 300 a wasu ƙananan hukumomin jihar.
Kwamishinan lafiya na jihar Dakta Farouk Abubakar ne ya tabbatar da hakan a taron wayar da kan jama’a na kwana ɗaya da ƙungiyar raya unguwanni ta jiha (WDC) tare da haɗin gwiwar ma’aikatar lafiya ta jiha da hukumar kula da lafiya matakin farko ta jihar suka shirya a ranar Juma’a.
Sai dai kwamishinan bai yi ƙarin bayani kan adadin mace-macen da aka samu tun watan Fabrairu da aka fara samun ɓullar cutar ba.
Ya ce har yanzu mutane 16 na ci gaba da karɓar magani a asibitoci yayin da sauran kuma aka sallame su.
A jawabansu daban daban, mai ba da shawara na musamman kan harkokin kiwon lafiya a matakin farko na jiha, Dakta Muhammad Bello Marnona, da babbar sakatariyar hukumar, Dakta Larai Aliyu Tambuwal, sun yaba da irin hangen nesa na shugabancin hukumar ta WDC.
Sun ce, ana iya rigakafin cutar kuma sun shawarci mutane da su ziyarci cibiyoyin lafiya da ke kusa don samun magungunan da suka dace a duk lokacin da suka fuskanci wata matsala.
Shima da yake tsokaci shugaban yankin Malam Ya’u Muhammad Danda wanda mataimakinsa Alhaji Faruk Umar Garba ya wakilta ya bayyana taron a matsayin wanda ya dace.
A nasa jawabin, Sarkin Musulmi Sultan Sa’ad Abubakar wanda Hakimin Gagi, Alhaji Sani Umar Jabbi ya wakilta, ya yaba wa Gwamna Ahmed Aliyu da jagororin gwamnatinsa na inganta lafiyar al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: sankarau
এছাড়াও পড়ুন:
Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
Jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ta tabbatar da mutuwar mataimakin gwamnan jihar Bayelsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo.
Jam’iyyar ta tabbatar da rasuwar ce a cikin wata sanarwa da sakatarenta yada labaranta na kasa, Kwamared Ini Ememobong, ya fitar.
Rahotanni sun ce Ewhrudjakpo ya yanke jiki ya faɗi a ofishinsa da ke gidan gwamnati, Yenagoa, a ranar Alhamis, inda aka garzaya da shi zuwa Cibiyar Lafiya ta Ƙasa (FMC) da ke Yenagoa.
Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis.
An haifi Ewhrudjakpo ranar ranar biyar ga watan Satumban 1965, a ƙauyen Ofoni da ke Ƙaramar Hukumar Sagbama, Jihar Bayelsa. Ya rasu yana da shekaru 60.
Kodayake ba a san ainihin dalilin faɗuwarsa ba, majiyoyi sun ce ya faɗi ne ba zato ba tsammani yayin da yake gudanar da ayyukan ofis, lamarin da ya sa dogarai da ma’aikatansa suka yi gaggawar taimaka masa.
Wasu majiyoyi da ke kusa da marigayin sun nuna cewa mutuwarsa na iya zama sakamakon bugun zuciya.
Lamarin ya haifar da ɗan tashin hankali a gidan gwamnati da kuma fadin Yenagoa, inda mazauna garin suka nuna damuwa game da mutumin da suke kira da “Mataimakin Gwamna Mai Aikin Dare.”
Sun ce sau da yawa yana yin aiki har dare ba tare da hutu ba.
A lokacin da ake rubuta wannan rahoto da yammacin jiya, gwamnatin Jihar Bayelsa ba ta fitar da wata sanarwa ba a hukumance a kan lamarin.
Kazalika, da mai taimaka wa mataimakin gwamnan kan yaɗa labarai, Doubra Atazi, da kuma Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar, Ebiuwou Koku-Obiyai, sun ƙi yin bayani lokacin da aka tuntube su.
Sai dai a cikin sanarwarta, PDP ta bayyana kaduwa da alhini kan rasuwar mataimakin gwamnan, tana bayyana shi a matsayin “amintaccen ɗan jam’iyya kuma mai gaskiya.”
Sanarwar ta ce: “Jam’iyyar PDP ta kadu matuƙa da labarin rasuwar Mataimakin Gwamnan Jihar Bayelsa kuma ɗan jam’iyya mai aminci, Mai Girma Sanata Lawrence Oborawharievwo Ewhrudjakpo, wanda rahotanni suka ce ya faɗi ya rasu a yau.
“Wannan labari mai tayar da hankali ya jefa Kwamitin Zartarwa na Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki, SAN, da kuma dukkan mambobin jam’iyyarmu mai girma, musamman mambobinmu masu aminci a Jihar Bayelsa, cikin baƙin ciki mai yawa.
“Tun yana raye, Sanata Ewhrudjakpo ya kasance ɗan siyasa mai gaskiya da daidaito wanda ya yi siyasa bisa ƙa’ida. Mutum ne da ya yi tsayin daka, jagora ne wanda rayuwarsa ta ta’allaka da imani, gaskiya da ƙarfin hali. Ya tsaya tsayin daka kan waɗannan dabi’u har zuwa ƙarshe.
“Muna cikin baƙin ciki matuƙa da rasuwar wannan jarumin siyasa mai gaskiya, kuma muna roƙon Allah ya ba shi hutu na har abada. Muna mika ta’aziyyarmu ga gwamnati da al’ummar jihar Bayelsa kan wannan babban rashin da ba za a iya maye gurbinsa ba.”