An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Published: 11th, April 2025 GMT
Kungiyar Afica city of Refugee ta gabatar da taron bukatar da kuma muhimmancin samun zaman lafiya a tsakanin Makiyaya da Manoma a garin Saka wanda ya ke karkashin jagorancin gundumar ci gaba ta Karshi da Uke,Karamar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa saboda a tattaunakan lamarin daya shafi zaman lafiya tsakanin Fulani Makiyaya da kuma Manoma.
Mutane da dama ne suka samu halartar taron wanda aka yi a Saka a makarantar Sakandare ta Saka daga cikin Shugaban kungiyar zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kirista na Karamar HUkumar Karu Reberend Timothy.
Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba Huawei Ya Daddale Yarjejeniya Da Kenya Don Habaka Kwarewar Ma’aikatan Kasar A Fannin DijitalReberend Justin darekta wanda kuma shi ne Shugaban kungiyar ya yi jawabi ne mai daukar hankali kan muhimmancin zaman lafiya,shi ma Sarkin Saka,Injiniya Adamu ya nuna farincikinsa dangane da shi taron.
A na shi jawabin Bound Bradam ya yi kira da makiyaya Fulani da manoma da cewar su hada kansu da Sarakuna,Hakimai,Dagatai,da masu Unguwanni, domin habaka,da kuma inganta harkar zaman lafiya a tsakaninsu,a kuma kara da cewa yana son Fulani makiyaya a zuciyarsa, hakan ya sa yake ta ta duk yin abinda zai iya ba domin komai bas a don ya ga an ci gaba da zaman lafiya tsakanin su Manoma da Fulani makiyaya wadanda a shekarun da suka gabata ba jin tsakaninsu,zama ne suke na ‘yan’uwantaka da zumunci domin kuwa suna amfana da juna.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Makiyaya zaman lafiya tsakanin
এছাড়াও পড়ুন:
Ribadu ya jagoranci tawaga zuwa Amurka don ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu, ya jagoranci wata tawagar gwamnati zuwa Amurka domin mayar da martani kan zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi a Najeriya.
Wannan zargi ya samo asali ne bayan mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, ya nuna goyon bayansa wajen kafa ƙasashe biyu tsakanin Isra’ila da Gaza.
Wardley ya zama zakaran damben boksin na duniya Hakimi ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na banaA farkon wannan watan ne Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ayyana Najeriya cikin jerin ƙasashen matsala ta musamman.
Sannan Trump ya umarci wasu ’yan majalisar Amurka, ciki har da Ɗan Majalisa Riley Moore da su binciki lamarin.
Duk da ƙoƙarin da Najeriya ta yi na bayyana haƙiƙanin abin da ke faruwa bai sa wasu jami’an Amurka sun sauya ra’ayi ba.
Daga cikin tawagar akwai: Bianca Ojukwu, Ƙaramar Ministar Harkokin Waje; Kayode Egbetokun, Sufeto Janar na ’Yan Sanda; Lateef Olasunkami Fagbemi, Antoni-Janar na Ƙasa; Janar Olufemi Olatunbosun Oluyede, Shugaban Ma’aikatan Tsaro; da Laftanar Janar E.A.P. Undiendeye, Shugaban Leƙen Asirin Tsaro na Ƙasa.
Sauran sun haɗa da Idayat Hassan, Jakada Ibrahim Babani, Daraktan Hulɗar Ƙasashen Waje a ONSA; Jakada Nuru Biu, Mai Riƙe da Muƙamin CDA na Ƙasashen Waje a Ma’aikatun Jakadancin Najeriya; da Paul Alabi, daga Sashen Siyasa da Tattalin Arziƙi a Ofishin Jakadancin Najeriya.
A ranar Talata, an gayyaci fitacciyar mawakiyar Amurka, Nicki Minaj zuwa zauren Majalisar Ɗinkin Duniya domin gabatatar da jawabi, inda ita ma ta nemi a kai wa Kiristocin Najeriya ɗauki.
Sai dai ba a bai wa Najeriya damar halartar taron ba wanda ya gudana a Birnin New York, lamarin da ya ƙara tayar da ƙura.
Wakilin Najeriya a Majalisar Ɗinkin Duniya, Syndoph Endoni, ya ce hakan tamkar “aske mana kai ba tare da mu ba.”
A ranar Laraba, tawagar Najeriya ta gana da Ɗan Majalisar Amurka Moore domin tattaunawa kan matsalolin tsaro a ƙasar da ƙoƙarin gwamnati ke yi na shawo kan tashe-tashen hankula.
Bayan ganawa da wakilan gwamnatin Najeriya, Moore ya ce ya fahimci yadda abubuwan suke.
Moore ya ce: “Yau na yi magana ta gaskiya, a buɗe kuma mai amfani da manyan jami’an gwamnatin Najeriya game da mummunan tashin hankali da bazaranar da Kiristoci ke fuskanta a faɗin Najeriya.
“Na bayyana a fili cewa dole Amurka ta ga an ɗauki ƙwararan matakai da za su tabbatar da cewa Kiristoci ba su fuskanci tashin hankali, zalunci, ko kisa saboda ba saboda sun gaskata Yesu Almasihu.”
Ya kara da cewa: “Mun shirya mu yi aiki tare da ’yan Najeriya domin taimaka musu su yaƙi ta’addancin da Boko Haram, ISWAP, da makiyaya Fulani ke aikatawa musamman a kan Kiristoci a yankin Arewa maso Gabas da Kudancin Kaduna da sauran yankunan Najeriya.”
Haka kuma Moore ya ce: “Gwamnatin Najeriya na da damar ƙarfafa dangantakarta da Amurka.
“Shugaba Trump da Majalisa sun haɗa kai kuma suna da niyyar kawo ƙarshen tashin hankalin da Kiristoci ke fuskanta da kuma karya ƙungiyoyin ta’addanci a Najeriya.
“Ina kira ga ’yan Najeriya su yi aiki tare da mu cikin haɗin kai domin magance wannan babban lamari.”
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, tawagar Najeriya ba ta fitar da sanarwarta kan wannan ziyara ba.