Leadership News Hausa:
2025-11-25@01:47:50 GMT

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

Published: 11th, April 2025 GMT

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

Kungiyar Afica city of Refugee ta gabatar da taron bukatar da kuma muhimmancin samun zaman lafiya a tsakanin Makiyaya da Manoma a garin Saka wanda ya ke karkashin jagorancin gundumar ci gaba ta Karshi da Uke,Karamar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa saboda a tattaunakan lamarin daya shafi zaman lafiya tsakanin Fulani Makiyaya da kuma Manoma.

Mutane da dama ne suka samu halartar taron wanda aka yi a Saka a makarantar Sakandare ta Saka daga cikin Shugaban kungiyar zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kirista na Karamar HUkumar Karu Reberend Timothy.

Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba Huawei Ya Daddale Yarjejeniya Da Kenya Don Habaka Kwarewar Ma’aikatan Kasar A Fannin Dijital

Reberend Justin darekta wanda kuma shi ne Shugaban kungiyar ya yi jawabi ne mai daukar hankali kan muhimmancin zaman lafiya,shi ma Sarkin Saka,Injiniya Adamu ya nuna farincikinsa dangane da shi taron.

A na shi jawabin Bound Bradam ya yi kira da makiyaya Fulani da manoma da cewar su hada kansu da Sarakuna,Hakimai,Dagatai,da masu Unguwanni, domin habaka,da kuma inganta harkar zaman lafiya a tsakaninsu,a kuma kara da cewa yana son Fulani makiyaya a zuciyarsa, hakan ya sa yake ta ta duk yin abinda zai iya ba domin komai bas a don ya ga an ci gaba da zaman lafiya tsakanin su Manoma da Fulani makiyaya wadanda a shekarun da suka gabata ba jin tsakaninsu,zama ne suke na ‘yan’uwantaka da zumunci domin kuwa suna amfana da juna.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Makiyaya zaman lafiya tsakanin

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa ’yan sanda umarnin daina tsaron manyan mutane a faɗin Najeriya.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ne, ya bayyana hakan a ranar Lahadi.

’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe ’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 5 a Bauchi

Onanuga, ya ce daga yanzu ’yan sanda za su mayar da hankalinsu ne aikin kare al’umma da yaƙar ’yan ta’adda.

An ɗauki wannan mataki ne a wani taron tsaro da aka gudanar a Abuja, wanda manyan shugabannin tsaro suka halarta, ciki har da shugabannin ’yan sanda, sojin sama, sojin ƙasa da hukumar DSS.

Sabon tsarin ya nuna cewa duk wani babban mutum da yake buƙatar tsaro dole ne, ya nemi jami’an tsaro daga Hukumar NSCDC maimakon ’yan sanda.

Najeriya ba ta da isassun ’yan sanda a yankunan karkara, kuma hakan yana haifar da tsaiko wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Saboda haka Shugaba Tinubu, ya umarci a ƙara yawan ’yan sandan da ke bai wa jama’a tsaro.

Onanuga, ya kuma ce Shugaban Ƙasa ya amince da ɗaukar ƙarin sabbin ’yan sanda 30,000.

Gwamnatin Tarayya za ta haɗa kai da gwamnatocin jihohi domin inganta cibiyoyin horas da ’yan sanda a faɗin Najeriya.

Taron tsaron da aka gudanar a ranar Lahadi, ya samu halartar Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Sunday Kelvin Aneke, Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, da Darakta-Janar na DSS, Tosin Adeola Ajayi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen
  • Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya
  • Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji
  • An  Cimma Yarjejeniya A Karshen Taron Kare Muhalli Na Duniya A Kasar Brazil
  • An Fitar Da Kudurin Bayan Taron Kungiyar G20 Ba Tare Da Halartar Kasar Amurka Ba
  •  An Kulla Yarjejeniyar Aikin Soja A Tsakanin Kasashen UAE Da Ethiopia
  • An Gabatar Da Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar G20 Duk Tare Da Kauracewar Amurka
  • Obi ya yi watsi da hukuncin ɗaurin rai da rai da aka yi wa Kanu
  •  Afirka Ta Kudu: Rashin Halartar Amurka Taron G-20 Ba Zai Yi Wani Tasiri Ba
  • Yan Wasan Kasar Iran Sun tashi Da Lambobin Yabo 81 A Wasannin Zumunci Tsakanin Kasashen Musulmi