Leadership News Hausa:
2025-12-13@18:12:33 GMT

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

Published: 11th, April 2025 GMT

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

Kungiyar Afica city of Refugee ta gabatar da taron bukatar da kuma muhimmancin samun zaman lafiya a tsakanin Makiyaya da Manoma a garin Saka wanda ya ke karkashin jagorancin gundumar ci gaba ta Karshi da Uke,Karamar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa saboda a tattaunakan lamarin daya shafi zaman lafiya tsakanin Fulani Makiyaya da kuma Manoma.

Mutane da dama ne suka samu halartar taron wanda aka yi a Saka a makarantar Sakandare ta Saka daga cikin Shugaban kungiyar zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kirista na Karamar HUkumar Karu Reberend Timothy.

Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba Huawei Ya Daddale Yarjejeniya Da Kenya Don Habaka Kwarewar Ma’aikatan Kasar A Fannin Dijital

Reberend Justin darekta wanda kuma shi ne Shugaban kungiyar ya yi jawabi ne mai daukar hankali kan muhimmancin zaman lafiya,shi ma Sarkin Saka,Injiniya Adamu ya nuna farincikinsa dangane da shi taron.

A na shi jawabin Bound Bradam ya yi kira da makiyaya Fulani da manoma da cewar su hada kansu da Sarakuna,Hakimai,Dagatai,da masu Unguwanni, domin habaka,da kuma inganta harkar zaman lafiya a tsakaninsu,a kuma kara da cewa yana son Fulani makiyaya a zuciyarsa, hakan ya sa yake ta ta duk yin abinda zai iya ba domin komai bas a don ya ga an ci gaba da zaman lafiya tsakanin su Manoma da Fulani makiyaya wadanda a shekarun da suka gabata ba jin tsakaninsu,zama ne suke na ‘yan’uwantaka da zumunci domin kuwa suna amfana da juna.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Makiyaya zaman lafiya tsakanin

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Ilimi ta Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 18 a 2026

Daga Usman Muhammad Zaria 

Ma’aikatar ilimi matakin farko ta jihar Jigawa ta ce za ta kashe fiye da naira miliyan dubu 18 domin gudanar da harkokinta a sabuwar shekara.

Kwamishinan ma’aikatar, Dr. Lawal Yunusa Danzomo ne ya bayyana haka lokacin da yake kare kiyasin kasafin kudin 2026 a gaban kwamatin ilimi matakin farko na majalisar dokokin jihar Jigawa.

Dr. Lawan Yunusa Danzomo ya ce zasu mayar da hankali ga aikin gina ajujuwa da gyaran wadanda suka lalace.

Za kuma a samar da littatafan darussa da tebura da kujeru domin inganta harkokin koyo da koyarwa.

Hakazalika za a  gina bandakuna da samar da ruwan sha da wutar lantarki da tsaro.

Danzomo, ya ce aiwatar da haka zai yi matukar tabbatar da kyakkyawar da’irar ilimi da ta kunshi samar da ilimi cikin sauki ta hanyar shiga makaranta har a kammmala karatu.

Dr. Lawan Danzomo ya kara da cewar za a dauki malaman wucin gadi har su 4000 a karkashin shirin J-Teach.

Ya kuma yi nuni da cewar, za a shirya jarrabawa ga kason farko na malaman J-Teach su 1,450 na gwamnatin da ta gabata domin daukar su aiki na dindindin.

A nasa jawabin shugaban kwamatin ilimi matakin farkio na majalisar dokokin jihar Jigawa kuma wakilin mazabar Fagam, Alhaji Yahaya Zakari Kwarko ya bada tabbacin hadin kai da goyon baya domin samun nasarar da ake bukataa sabuwar shekara.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • Ma’aikatar Ilimi ta Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 18 a 2026
  • Shuwagabannin Kasashen Iran Da Iraqi Sun Tattauna A Wajen Taron Zaman Lafiya A Kasar Turkmanistan
  • Pezeshkian: Duniya Tana Bukatar Amintaccen Madogara, Zaman Lafiya Da Kuma Hadin Kai
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026