An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Published: 11th, April 2025 GMT
Kungiyar Afica city of Refugee ta gabatar da taron bukatar da kuma muhimmancin samun zaman lafiya a tsakanin Makiyaya da Manoma a garin Saka wanda ya ke karkashin jagorancin gundumar ci gaba ta Karshi da Uke,Karamar Hukumar Karu ta Jihar Nasarawa saboda a tattaunakan lamarin daya shafi zaman lafiya tsakanin Fulani Makiyaya da kuma Manoma.
Mutane da dama ne suka samu halartar taron wanda aka yi a Saka a makarantar Sakandare ta Saka daga cikin Shugaban kungiyar zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kirista na Karamar HUkumar Karu Reberend Timothy.
Sin Ba Za Ta Razana Da Zuwan Yakin Cinikayya Ba Huawei Ya Daddale Yarjejeniya Da Kenya Don Habaka Kwarewar Ma’aikatan Kasar A Fannin DijitalReberend Justin darekta wanda kuma shi ne Shugaban kungiyar ya yi jawabi ne mai daukar hankali kan muhimmancin zaman lafiya,shi ma Sarkin Saka,Injiniya Adamu ya nuna farincikinsa dangane da shi taron.
A na shi jawabin Bound Bradam ya yi kira da makiyaya Fulani da manoma da cewar su hada kansu da Sarakuna,Hakimai,Dagatai,da masu Unguwanni, domin habaka,da kuma inganta harkar zaman lafiya a tsakaninsu,a kuma kara da cewa yana son Fulani makiyaya a zuciyarsa, hakan ya sa yake ta ta duk yin abinda zai iya ba domin komai bas a don ya ga an ci gaba da zaman lafiya tsakanin su Manoma da Fulani makiyaya wadanda a shekarun da suka gabata ba jin tsakaninsu,zama ne suke na ‘yan’uwantaka da zumunci domin kuwa suna amfana da juna.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Makiyaya zaman lafiya tsakanin
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su a Borno
’Yan sanda sun ceto yara 2 da aka yi garkuwa da su, masu shekaru hudu da biyar, a Jihar Borno.
An ceto yaran ne a yayin wani samame da ’yan sanda suka kai a Ƙaramar Hukumar Jere, inda masu garkuwar suka je karbar kuɗin fansa.
Sanarwa da ASP Nahum Kenneth Daso, kakakin rundunar ya fitar ta ce, bayan sun sami rahoto a ranar 4 ga Disamba cewa yara uku sun bace, washegari masu garkuwar suka sako ɗaya daga cikin yaran da takardar neman naira miliyan 10 domin sakin sauran biyun.
A ranar ce jami’an rundunar suka kai samame a wurin da aka ware don karɓar kuɗin fansar.
Ganin hakan masu garkuwa da mutanen, suka farga da wannan tarko da aka musu nan da nan suka yi watsi da yaran suka gudu cikin duhu.
An ceto yaran ba tare da wani rauni ko biyan kuɗin fansa ba, kuma sun sake haɗuwa da iyalansu, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano waɗanda ake zargi.
Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Yobe, Naziru Abdulmajid, ya ba da umarnin zurfafa bincike kuma ya umurci jami’an rundunar da su qarfafa sintiri, su gudanar da ayyukan bincike mai tsauri, da kuma ci gaba da gudanar da ayyukansu don rage yawaitar aikata laifuka a baya-bayan nan.
Hukumar tsaron ta kuma yi kira ga mazauna yankin da su kasance cikin shiri da kuma bayar da rahoton ayyukan da ake zargi, tare da samar da lambobin tuntuɓar gaggawa don hanzarta kai xauki.