Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi
Published: 11th, April 2025 GMT
Sama da gidaje dari biyu da arba’in ne aka lalata a daren Talatar da ta gabata, ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka shafe sa’o’i ana yi a unguwar Garin Kestu Atuwo dake karamar hukumar Shanga ta jihar Kebbi.
Da yake jajantawa wadanda abin ya shafa, Gwamna Nasir Idris ya shawarci gidajen da abin ya shafa da su dauki lamarin a matsayin wani kaddara daga Allah Ta’ala.
Shugaban karamar hukumar Shanga, Alhaji Audu Dan Audu, ya wakilce shi, ya ce ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi a daren ranar Talata ya lalata gidaje da dukiyoyi na miliyoyin Naira, ya kuma yi godiya ga Allah Madaukakin Sarki ganin yadda ba a yi asarar rayuka ba.
Ya kuma yi kira gare su da su yi hakuri domin nan bada jimawa gwamnatin jihar za ta mika musu tallafi da suka hada da kayayyakin gini.
Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Umaurci Matawalle Ya Koma Kebbi a Cigaba da Kokarin Kubutar da Daliban da Aka Sace
Daga Bello Wakili
Shugaba Bola Tinubu ya umurci Ministan Tsaro, Alhaji Bello Matawalle, da ya koma Jihar Kebbi biyo bayan sace dalibai ’yan mata 24 a jihar.
An umurci Matawalle, wanda tsohon gwamnan Jihar Zamfara ne, da ya zauna a jihar domin sa ido kan ƙoƙarin da ake yi na kubutar da ɗaliban da aka sace.
’Yan bindiga sun sace ɗalibai mata 24 na Makarantar Sakandare ta ’Yan Mata da ke garin Maga, Jihar Kebbi, da misalin ƙarfe 4 na asubar ranar Litinin.
Matawalle, wanda ake sa ran zai isa Birnin Kebbi a ranar Juma’a, ya samu ƙwarewa wajen fuskantar matsalar ’yan fashi da garkuwa da mutane a lokacin da yake gwamnan Jihar Zamfara daga shekarar 2019 zuwa 2023.
Idan za a iya tunawa ranar 26 ga watan Fabrairun 2021, ’yan bindiga sun sace ɗalibai mata 279 da ke tsakanin shekaru 10 zuwa 17 a Makarantar Sakandare ta Kimiyya ta ’Yan Mata da ke Jangebe, a Jihar Zamfara. ’Yan bindigar sun saki dukkan waɗanda suka yi garkuwa da su a ranar 2 ga Maris 2021.
Shugaba Tinubu ya ɗage tafiyarsa da aka shirya zuwa Johannesburg, Afrika ta Kudu, da kuma Luanda, na kasar Angola, domin ya jira bahasin halin da ake ciki game da ’yan matan makarantar da aka sace a Kebbi da kuma harin da aka kai wa masu ibada na Cocin Christ Apostolic da ke Eruku, Jihar Kwara.