Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-20@07:00:52 GMT

Sabon Kwamishinan Na Kwara Ya Sha Alwashin Dakile Laifuka

Published: 11th, April 2025 GMT

Sabon Kwamishinan Na Kwara Ya Sha Alwashin Dakile Laifuka

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara, ta ce an shirya shirye-shirye domin karfafa tsaro a jihar da kuma tabbatar da mazauna yankin suna rayuwa cikin yanayi na zaman lafiya da tsaro.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Adekimi Ojo ne ya bayyana haka da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ‘yan sanda da ke Ilorin.

 

Ya ce gwamnatinsa ba za ta amince da rashin da’a, take hakkin bil’adama, yana mai cewa ma’aikatan da suka yi kuskure za su fuskanci tsauraran mataki.

 

Ojo ya yi alkawarin samarwa jihar tsaro ta hanyar magance miyagun laifuffuka da kuma kiyaye da’a da kwarewa a cikin rundunar ‘yan sanda.

 

Ya bayyana cewa rundunar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen yakar laifuka da aikata laifuka.

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya jaddada cewa aikin ‘yan sanda mai inganci yana bukatar sanya hannun masu ruwa da tsaki da suka hada da shugabannin gargajiya da na addini da kungiyoyin farar hula da kuma kafafen yada labarai.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara Yansanda

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi

Jami’an tsaro a Jihar Kogi, sun kama wasu ’yan bindiga biyu da suka ji rauni tare da likitocin bogi da ke yi musu magani.

Hakazalika, sun lalata sansaninsu a lokacin da suka kai musu farmaki.

Ba mu ji dadin yi wa mahaifinmu afuwa tare da riƙaƙƙun masu laifi ba – Iyalan Herbert Macaulay Akwai yiwuwar matsin lamba ya sa Tinubu cire sunayen wasu da ya yi wa afuwa saboda cece-kuce

Mai bai wa Gwamnan Jihar Kogi, shawara kan harkar tsaro, Kwamanda Jerry Omodara (mai ritaya), ya bayyana cewa rundunar haɗin gwiwa da ta ƙunshi sojoji, mafarauta da ’yan sa-kai ne suka kai samamen a garin Aherin-Bunu da ke Ƙaramar Hukumar Kabba-Bunu.

A cewar Omodara, jami’an tsaron sun samu bayanan sirri cewa ana yi wa ’yan bindigar da suka ji rauni magani a wani gida.

Ya ce: “Mun samu bayanai cewa wasu ’yan bindiga biyu da suka ji rauni, ana musu magani a wani gida a Aherin-Bunu.

“Nan da nan muka tura jami’an tsaro, suka kama su tare da likitocin bogi da ke yi musu magani.

“Duk wanda aka kama yana taimaka wa ko yana haɗa kai da masu aikata laifi, za a hukunta shi ba tare da la’akari da muƙaminsa ba.”

Omodara, ya ƙara da cewa jami’an tsaron sun lalata sansanin ’yan bindigar, tare da ƙone wani wani waje da suke amfani da shi a matsayin asibiti da kuma gonakinsu.

Ya gargaɗi jama’a da su guji kowace irin alaƙa da masu laifi, inda ta jadadda cewa gwamnati ba za ta ƙyale duk mai tallafa wa miyagu ba a Jihar Kogi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tsinci gawar wata mata da aka yi wa kisan gilla a Yobe
  • Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
  • An tsinci gawar wata mata a kusa da Jami’ar Tarayya a Yobe
  • Sojoji sun tallafa wa mutanen Yobe da N23m bayan harin kuskure
  • ’Yan sanda sun ƙwato miyagun ƙwayoyi a Gombe
  • Dantawaye ya zama sabon kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
  • Jami’an tsaro sun kama ’yan bindiga 2, sun ƙone sansaninsu a Kogi
  • Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Kura
  • Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da KuraAfuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka Ta Bar Baya Da Kura