Aminiya:
2025-11-02@05:41:48 GMT

A ɗora min laifin hatsarin jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja — Shugaban NRC

Published: 27th, August 2025 GMT

Shugaban hukumar kula da jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC), Kayode Opeifa, ya ce ya ɗauki alhakin hatsarin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna da ya auku a ranar Talata.

Aminiya ta ruwaito cewa hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 11 na safe bayan jirgin ya taso daga Abuja zuwa Kaduna.

Dilan ƙwaya ya shiga hannu a Borno ASUU: Malaman Jami’ar FUK sun yi zanga-Zanga kan rashin cika musu alƙawura 

Da yake zantawa da gidan talabijin na Channels a yau Laraba, Opeifa ya ce ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen binciken abin da ya haddasa lamarin.

“Bayan neman gafarar ’yan Najeriya, a matsayina na shugaban hukumar, na ɗauki alhakin duk abin da ya faru,” in ji shi.

“Ba za mu ɗebe tsammanin faruwar irin wannan lamari ba, amma duk lokacin da hakan ta kasance, tana ƙara mana fahimtar wuraren da suke buƙatar mu inganta.”

Hukumar agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) ta tabbatar da cewa mutum bakwai suka ji rauni bayan aukuwar hatsarin waɗanda tuni sun samu kulawar gaggawa daga likitoci.

A jiyan ne dai NRC ta sanar da dakatar da sufurin jirgin ƙasan da ke jigila tsakanin Kaduna da Abuja har zuwa lokacin da za ta kammala bincike kan musabbabin faruwar lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jirgin Ƙasa Kayode Opeifa

এছাড়াও পড়ুন:

Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Wata kotu da ke birnin Madrid ta yi watsi da ƙarar da Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nahiyyar Turai UEFA, LaLiga da Hukumar Kwallon Kafa ta Sipaniya suka shigar kan ƙin amincewa da gasar Super League.

Wannan yana nufin yanzu Real Madrid da sauran ƙungiyyoyin za su iya neman diyyar kudi Euro Milyan 4.

Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa 

Real Madrid ta ce, wannan hukuncin ya tabbatar da cewa UEFA ta karya dokokin gasa, kuma ƙungiyyoyi sun rasa maƙuden kuɗaɗe tun daga lokacin da aka dakatar da gasar.

Gasar wacce aka shirya farawa a shekarar 2021 tare da manyan ƙungiyoyin Turai, an yi hasashen zata samar da kusan Yuro miliyan 200 ga ƙungiyoyin da suka shiga.

A nata martanin hukumar UEFA ta dage cewa wannan sabon hukuncin ba ya nufin an dawo ko an amince da a buga gasar Super League ba ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • Ƙwallo ta kashe ɗan wasan Cricket
  • Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher
  • Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja
  • Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba