Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar haraji
Published: 18th, March 2025 GMT
Majalisar Wakilai ta amince da ƙudirin dokar haraji bayan ya tsallake karatu uku a wannan Talatar.
Wannan na zuwa ne bayan karatun tsanaki da majalisar ta yi ƙudirin a ranar Alhamis ta makon jiya.
Wike ya ƙwace filin Sakatariyar PDP da ke Abuja Janar Tsiga ya shafe kwanaki 40 a hannun masu garkuwa duk da biyan kuɗin fansaAna iya tuna cewa, a makonnin bayan nan ne kwamitin kuɗi na majalisar ya gudanar da sauraron ra’ayin jama’a kan ƙudirin, inda kuma ya tattara ra’ayoyin al’umma ya miƙa wa majalisar.
Dokar harajin da majalisar ta amince da ita ta ƙunshi ƙudiri guda huɗu da suka haɗa da ƙudirin dokar tafiyar da haraji da na kafa hukumar tattara haraji mai suna Nigeria Revenue Service da hukumar haɗaka ta tattara haraji da kuma ƙudirin haraji na Najeriya.
A watan Okotoban bara ne Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aike da ƙudirin dokar ga majalisar dokokin ƙasar.
An dai shafe watanni ana taƙaddama kan dokar harajin wadda daga bisani gwamnonin jihohi 36 na Nijeriya suka cimma matsaya tare da amincewa da ƙudirin sabuwar dokar haraji, bayan gyare-gyaren da aka yi a kan rabon harajin kayayyaki na VAT da ya tayar da kura a ƙasar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dokar Haraji Majalisar Wakilai da ƙudirin dokar dokar haraji
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Babu wanda ko da a kuskure ya yi magana a kan tattaunawa da Amurka saboda tsananin fushin da al’ummar Iran ta yi
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Ismail Baqa’i ya ce dangane da tattaunawar da aka yi da Amurka, “A halin yanzu al’ummar Iran suna cikin fushi matuka, ta yadda babu wanda ya isa ya yi magana kan batun gudanar da zaman tattaunawa da Amurka ko harkar diflomasiyya.”
A cikin wata hira da gidan talabijin na Sky News, yayin da yake mayar da martani kan wata tambaya kan shirin nukiliyar Iran biyo bayan harin wuce gona da iri da Amurkawa da ‘yan sahayoniyya suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran, Baqa’i ya ce: “Sun yi imani da farko dole ne su fahimci abin da ya faru, kwarai abin da ya faru shi ne wani danyen aikin wuce gona da iri da gwamnatin mamayar Isra’ila ta yi aikata kan kasar Iran, sannan kuma Amurka, kan ‘yancin kan kasar Iran da kuma ikon kasar.”