An Ware Sama Da Naira Biliyan 1.5 Don Fara Aiki A Sabon Kamfanin Injinan Noma Na Jigawa
Published: 18th, March 2025 GMT
A yunkurin da gwamnatin jihar Jigawa ke yi na sauya fasalin harkar noma, majalisar zartaswa ta jihar ta amince da ware sama da naira biliyan daya da miliyan dari biyar domin fara aiki da sabon Kamfanin injinan noma na jihar.
Kwamishinan Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ne ya bayyana hakan ga manema labarai, jim kadan bayan kammala taron majalisar zartaswa da aka gudanar a fadar gwamnatin jihar da ke Dutse, babban birnin jihar.
A cewarsa, an kafa kamfanin ne domin rage tsadar sarrafa kayayyakin amfanin gona a fadin jihar.
Ya kara da cewa, majalisar ta kuma amince da fitar da sama da naira miliyan dari tara da sittin da tara domin ci gaba da aiwatar da ayyukan kamfanin injinan noma.
Ya ce, wannan amincewa ta hada da biyan harajin kwastam da kudaden haraji na gwamnati kan kayan aikin injinan noma da kuma sassan gyara da aka sayo daga kasar Sin.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana cewa, majalisar ta tattauna kan wani kudirin doka da ya shafi kafa Asusun Tallafin Ibtila’in Ambaliyar ruwa na Jihar Jigawa.
Kwamishinan ya kara da cewa, amincewar ta yi daidai da kudirin Gwamna Umar Namadi na kawo dauwamammen mafita kan matsalolin ambaliya a jihar.
Ya ce, bayan tattaunawa, majalisar ta amince da kudirin dokar tare da mika shi zuwa majalisar dokokin jihar domin tantancewa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
Dabbobi sama da miliyan guda ne ake sa ran za a yi wa rigakafi a fadin karamar hukumar Babura da ke jihar Jigawa.
Shugaban karamar hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu, ne ya bayyana hakan yayin kaddamar da aikin rigakafin dabbobi na bana.
A cewarsa, fiye da tumaki da awaki miliyan daya da shanu dubu ashirin ake sa ran za a yi wa rigakafi a fadin karamar hukumar.
Ya jaddada cewa karamar hukumar na da cikakken shiri da kudurin tallafawa sauyin noma na Gwamna Umar Namadi, domin inganta rayuwa da tattalin arzikin al’ummar jihar.
Shugaban ya jaddada muhimmancin masu kiwon dabbobi su bada hadin kai yayin aikin rigakafin domin tabbatar da lafiyar dabbobinsu.
Alhaji Hamisu Garu ya kuma nuna jin dadinsa game da zaman lafiya tsakanin manoma da makiyaya a yankin, yana mai kira gare su da su ci gaba da gudanar da rayuwa cikin fahimta da hadin kai.
Haka zalika, yayin taron, Shugaban Sashen Noma da Albarkatun Kasa, Malam Lawan Sabo Kaugama, ya bayyana cewa an ware cibiyoyi guda goma sha biyu domin gudanar da aikin rigakafin wanda ake sa ran zai dauki kwanaki hudu.
Ya yaba da kokarin gwamnatin jiha da ta karamar hukuma wajen samar da allurar rrigakafn da kuma duk wasu kayan aiki da ake bukata.
Usman Muhammad Zaria