’Yan bindiga sun sace ma’aurata da ’yarsu mai shekara ɗaya a Katsina
Published: 27th, August 2025 GMT
Maharan da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne a ranar Talata sun sace mata da miji tare da ’yarsu mai shekara ɗaya a cikin birnin Katsina.
An dai kai harin ne a gidan ma’uratan, Anas Ahmadu, da matarsa Halimatu, da kuma ’yarsu Jiddah a Unguwar Kanada a yankin Ƙofar Ƙaura a Katsina.
DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa NRC ta dakatar da jigilar jirgin ƙasan Kaduna zuwa AbujaRahotanni sun ce an kai harin ne wajen misalin ƙarfe 3:00 na daren Litinin inda maharan suka sace magidancin mai suna Malam Anas tare da matarsa mai suna Halimatu da ’yarsa.
Bayanai sun kuma nuna wani dan bangar da yayi ƙoƙarin kai musu ɗauki ya rasa ransa.
Sai dai wasu mazauna unguwar sun ce tun da farko sun yi zargin wasu mutane biyu da aka ga suna zirga-zirga a yankin har suka sanar da ’yan bangar da ke unguwar.
Sai dai ko da aka neme su ba a gan su ba, sun buya tun da suka lura jama suna zargin su.
Rundunar ’Yan Sandan Jihar ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da Kakakinta, DSP Abubakar Sadiq ya fitar.
Ya ce wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun ƙaddamar da harin a ranar Talata a gidan wani Anas Ahmadu, mai shekaru 33, a unguwar Filin Kanada a cikin garin Katsina, inda suka yi garkuwa da shi.
Kakakin ya kuma ce maharan sun yi awon gaba da matar mutumin mai suna Halimatu da ’yarsa Jidda Anas.
Ya tabbatar da cewa, ’yan bindigar sun kuma harbe wani mai suna Abdullahi Muhammad, mai shekaru 25, wanda ke aikin banga, kuma sun tsere daga wurin kafin isowar jami’an ’yan sanda.
DSP Abubakar ya kuma ce rundunar ta shiga yin bincike don gano maharan da kuma kubutar da wadanda aka yi garkuwar da su.
Mazauna birnin Katsina dai sun fara nuna damuwarsu kan yadda ’yan bindiga ke karuwa a Jihar wanda ta kai har suna shiga cikin manyan biranen jihar suna kai hare-hare.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
Fitattun dalibai akalla 12 ne daga makarantun gwamnati suka samu guraben tallafin karatun sakandare a ƙarƙashin Asusun Tallafin Karatu na Jihar Kwara (Kwara-ETF).
A wajen taron gabatarwa ga waɗanda suka fara cin moriyar shirin, Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya bayyana cewa ci gaban harkar ilimi a Najeriya abu ne mai tsada kuma ya zama wajibi kowa ya bayar da gudummawarsa.
Ya roƙi masu masu hannu da shuni da kungiyoyi masu zaman kansu da su tallafa wajen gina makarantu ko kuma su ɗauki nauyin daliban da suka nuna bajinta da jajircewa a harkar karatu.
A cewarsa, an zabo daliban 12 ne sakamakon bajintar da suka nuna a matakai daban-daban na tantancewa da Kwara ETF ta gudanar.
Gwamnan ya bayyana cewa tallafin ya kunshi dukkan kuɗin da ake buƙata a karatun sakandaren daliban.
“Muna kira da jama’a su ba da gudummawa da kuma ɗaukar nauyin ɗalibai. Kada a bar wannan aiki ga gwamnati da iyaye kadai. Ilimantar da ‘ya’yanmu hakki ne da ya rataya a kanmu gaba ɗaya,” in ji Gwamna.
Ya yaba da tsarin zaɓen kuma ya taya waɗanda suka yi nasara murna.
A nata jawabin, Babbar Shugabar Kwara ETF, Oluwadamilola Amolegbe, ta ce daliban 12 sun fito ne daga cikin jerin ɗalibai 640 da aka fara tantancewa bisa cancanta.
Ta bayyana cewa tsarin zaɓen ya fara ne da rubuta jarabawa ga dukkan daliban firamare na aji shida da suka amfana da shirin KwaraLEARN na koyon fasahar zamani, har zuwa lokacin da aka kammala tantancewa.
Ali Muhammad Rabi’u