Aminiya:
2025-11-02@06:37:20 GMT

’Yan bindiga sun sace ma’aurata da ’yarsu mai shekara ɗaya a Katsina

Published: 27th, August 2025 GMT

Maharan da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne a ranar Talata sun sace mata da miji tare da ’yarsu mai shekara ɗaya a cikin birnin Katsina.

An dai kai harin ne a gidan ma’uratan, Anas Ahmadu, da matarsa Halimatu, da kuma ’yarsu Jiddah a Unguwar Kanada a yankin Ƙofar Ƙaura a Katsina.

DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa NRC ta dakatar da jigilar jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja

Rahotanni sun ce an kai harin ne wajen misalin ƙarfe 3:00 na daren Litinin inda maharan suka sace magidancin mai suna Malam Anas tare da matarsa mai suna Halimatu ​​da ’yarsa.

Bayanai sun kuma nuna wani dan bangar da yayi ƙoƙarin kai musu ɗauki ya rasa ransa.

Sai dai wasu mazauna unguwar sun ce tun da farko sun yi zargin wasu mutane biyu da aka ga suna zirga-zirga a yankin har suka sanar da ’yan bangar da ke unguwar.

Sai dai ko da aka neme su ba a gan su ba, sun buya tun da suka lura jama suna zargin su.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da Kakakinta, DSP Abubakar Sadiq ya fitar.

Ya ce wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun ƙaddamar da harin a ranar Talata a gidan wani Anas Ahmadu, mai shekaru 33, a unguwar Filin Kanada a cikin garin Katsina, inda suka yi garkuwa da shi.

Kakakin ya kuma ce maharan sun yi awon gaba da matar mutumin mai suna Halimatu da ’yarsa Jidda Anas.

Ya tabbatar da cewa, ’yan bindigar sun kuma harbe wani mai suna Abdullahi Muhammad, mai shekaru 25, wanda ke aikin banga, kuma sun tsere daga wurin kafin isowar jami’an ’yan sanda.

DSP Abubakar ya kuma ce rundunar ta shiga yin bincike don gano maharan da kuma kubutar da wadanda aka yi garkuwar da su.

Mazauna birnin Katsina dai sun fara nuna damuwarsu kan yadda ’yan bindiga ke karuwa a Jihar wanda ta kai har suna shiga cikin manyan biranen jihar suna kai hare-hare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m

Wani gidan shan kofi a birnin Dubai ya fara sayar da kofi guda na haɗaɗɗen kofi a kan kusan Dala 1,000, wato kimanin Naira miliyan 1.5, wanda da haka ya zama mafi tsada a duniya.

Gidan shan kofin mai suna Julith Café — da ke cikin unguwar masana’antu da ya zama sabuwar cibiyar masu son kofi, shi ne ya ƙaddamar da wannan sabon nau’in abin sha mai daraja.

Ana sa ran gidan shan kofi ɗin zai fara ba da wannan abin sha ga mutane kimanin 400 kacal, ciki har da wani ɗan adadi da aka tanadar wa dangin gidan sarautar Dubai.

Wani daga cikin masu mallakar gidan, Serkan Sagsoz, ya ce sun zaɓi Dubai ne saboda “birni ne da  ya dace da irin jarin da ke nuna ƙawa da kuma salo.

“Mun ga Dubai a matsayin wuri mafi dacewa don wannan kasuwanci. Wannan birni ne da ke son abubuwan da suka bambanta,” in ji Sagsoz.

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi

Kofin kofi ɗin, wanda ake sayarwa a kan Dirhami 3,600 (kimanin 980), an yi shi ne daga ’ya’yan kofi na musamman da ake kira Nido 7 Geisha ,daga ƙasar Panama — waɗanda aka saya a gasa ta duniya bayan tashin rububin mai tsanani tsakanin masu saye.

Kamfanin Julith Café ya ce ya biya kimanin Dirhami miliyan 2.2 (dala 600,000) don sayen kilo 20 na waɗannan ’ya’yan kofi, abin da ya kafa sabon tarihin farashi mafi tsada da aka taɓa sayen kofi a duniya.

Sagsoz ya bayyana cewa kofi ɗin yana da ƙamshi da ɗanɗano na musamman. “Yana da ƙamshin furanni farare irin na jasmine, ɗanɗanon lemo da bergamot, har da ɗanɗano irin na apricot da peach. Kamar zuma yake — laushi kuma mai daɗi sosai.”

A bara, wani gidan kofi mai suna Roasters ya kafa tarihin Guinness na kofin kofi mafi tsada a duniya a Dubai, inda ya sayar da shi a kan Dirhami 2,500, amma yanzu Julith Café ta karya wannan tarihin.

Wasu mazauna Dubai sun ce duk da abin mamaki ne, amma abin ba baƙo ba ne a garin da aka sani da abubuwan alfarma.

“Abin mamaki ne amma ai wannan Dubai ce,” in ji wata mazauniya mai suna Ines.

“Ai akwai masu kuɗi, wannan wani sabon abin alfahari ne kawai,” in ji wata mai suna Maeva.

Ana sa ran gidan shan kofi ɗin zai fara ba da wannan abin sha ga mutane kimanin 400 kacal, ciki har da wani ɗan adadi da aka tanadar wa dangin gidan sarautar Dubai.

Shin idan kuna da kudin za ku saya?

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 
  • Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba