Barkan mu da sake haɗuwa a zauren girke-girke na watan Ramadana. Tare da fatan ana cikin koshin lafiya.
A yau na kawo wa uwargida wani girkin shuwa daga Jihar Borno, wato ‘Kamoniya’ domin yin buda baki. A sha ruwa lafiya.
Abubuwan da za ki bukata:
· Hanta · Tumbi · Huhu · Albasa 3 · Lemun tsami · Attaruhu · Man gyada · Curry da thyme · Maggi da gishiri
Yadda ake hadin:
A wanke kayan ciki (banda hanji), sai a yanka su kanana.
Sannan sai a yanka albasa a zuba man gyadan kadan a cikin tukunyar.
Bayan haka, sai a zuba curry da thyme da gishiri kadan a wankakken kayan cikin. Sai a gauraya su kafin a zuba a tukunya.
Idan an gama gaurayawa, sai a zuba su a tukunya ana juya su har sai ruwan da man sun shiga cikin kayan cikin.
Za a ga kayan cikin sun koma ruwan kasa. Sai a juye a kula a rufe. Hakan za a rika yi kadan-kadan har sai kayan cikin sun kare.
A wanke attaruhu da lemon tsami. A kirba attarugu ya kirbu sosai, sannan sai a zuba maggi wanda zai kashe zafin attaruhun.
Sai a matsa lemon tsami a kan attaruhun.
Ana cin kamoniya ne da wannan hadin attarugun. Ana dangwalawa a attaruhu don samin dandano mai gamsarwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kamoniya kayan cikin
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa yayin tsere wa harin ’yan bindiga a Neja
Wani jariri ya rasu a bayan mahaifiyarsa lokacin da take kokarin tserewa daga harin ’yan bindiga a ƙauyen Allawa da ke ƙaramar hukumar Shiroro ta Jihar Neja.
Hakkin ya fito ne daga bakin Hakimin Bassa, Bagudu Amos, yayin wani taron tattaunawa da mata kan rikici da zaman lafiya mai taken: “Ƙarfafa Matakan Kare Fyade da Cin Zarafin Mata a Jihar Neja”.
Gwamnatin Gombe ta gyara hanyoyin kiwo domin daƙile rikicin manoma da makiyaya HOTUNA: Yadda dubban magoya baya suka yi dafifi don tarbar FubaraTaron dai wata kungiya mai zaman kanta mai suna Tunani Initiative ce ta shira shi, tare da hadin gwiwar gidauniyar Dorothy Njemanze Foundation da kuma gidauniyar Foundation, domin ƙarfafa gwiwar mata wajen magance cin zarafin jinsi a jihar.
Hakimin ya ce mahaifiyar ta yi tafiya mai nisa domin tserewa daga farmakin ’yan bindigar, ba tare da ta san cewa jaririn da ke bayanta ya riga ya mutu ba.
Ya ce lamarin da ya faru a shekarar 2023 na daga cikin abubuwan da ke ci wa mata ’yan gudun hijira tuwo a ƙwarya a kullum, inda ya ƙara da cewa yawancin matan ba su da gogewar ilimin da zai ba su damar tinkarar cin zarafin jinsi da ke tasowa sakamakon rashin tsaro.
Shugabar ƙungiyar Tunani Initiative, Maryam Mairo Ibrahim, ta ce ana buƙatar a ba mata dama wajen samar da zaman lafiya da warware rikice-rikice a Jihar Neja.
Ta yi kira ga mata da su haɗa kai don karya shingen da ke hana su yin tasiri a rayuwa.
Ta ce, “A Jihar Neja, kamar yadda ake fama da rashin tsaro a wasu wurare, mata su ne suka fi shan wahalar mafi yawan hare-hare da kashe-kashen da ake yi. Idan ’yan bindiga suka kai hari, yawanci maza ne ake kashewa, sai matan da aka bari su ɗauki nauyin sake gina iyali.
“Wadannan rawar da mata ke takawa ba a lura da ita yadda ya kamata. Saboda haka, wannan tattaunawa ta mayar da hankali ne kan ƙarfafa rawar da mata ke takawa wajen samar da zaman lafiya da kuma magance cin zarafin jinsi a Jihar Neja,” in ji ta.
Daraktan Hukumar Kare Haƙƙin Dan Adam ta Jihar, Nuhu Muhammad, ya jaddada buƙatar ƙara yawan mata a majalisar dokoki ta jiha da ta ƙasa, domin samar da dokoki da manufofi da suka dace da bukatunsu.