Aminiya:
2025-11-01@01:44:37 GMT

Yadda za a girka ‘Kamoniya’

Published: 16th, March 2025 GMT

Barkan mu da sake haɗuwa a zauren girke-girke na watan Ramadana. Tare da fatan ana cikin koshin lafiya.

A yau na kawo wa uwargida wani girkin shuwa daga Jihar Borno, wato ‘Kamoniya’ domin yin buda baki. A sha ruwa lafiya.

Abubuwan da za ki bukata:

· Hanta · Tumbi · Huhu · Albasa 3 · Lemun tsami · Attaruhu · Man gyada · Curry da thyme · Maggi da gishiri

Yadda ake hadin:

A wanke kayan ciki (banda hanji), sai a yanka su kanana.

A zuba man gyada a cikin tukunya, sai a dora a kan wuta.

Sannan sai a yanka albasa a zuba man gyadan kadan a cikin tukunyar.

Bayan haka, sai a zuba curry da thyme da gishiri kadan a wankakken kayan cikin. Sai a gauraya su kafin a zuba a tukunya.

Idan an gama gaurayawa, sai a zuba su a tukunya ana juya su har sai ruwan da man sun shiga cikin kayan cikin.

Za a ga kayan cikin sun koma ruwan kasa. Sai a juye a kula a rufe. Hakan za a rika yi kadan-kadan har sai kayan cikin sun kare.

A wanke attaruhu da lemon tsami. A kirba attarugu ya kirbu sosai, sannan sai a zuba maggi wanda zai kashe zafin attaruhun.

Sai a matsa lemon tsami a kan attaruhun.

Ana cin kamoniya ne da wannan hadin attarugun. Ana dangwalawa a attaruhu don samin dandano mai gamsarwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kamoniya kayan cikin

এছাড়াও পড়ুন:

Duk da ce-ce-ku-ce sunan Maryam Sanda na cikin wadanda Tinubu ya yi wa afuwa

Shugaba Bola Tinubu, ya janye afuwar da ya yi wa wasu wadanda suka hada da masu manyan laifuka kamar kisan kai, safarar miyagun ƙwayoyi da sauransu.

A baya dai wasu sun yi ta suka da ce-ce-ku-ce kan sanya sunan Maryam Sanda cikin wadanda shugaba Tinubu ya yi wa afuwa.

Tinubu ya janye afuwar da ya yi wa Maryam Sanda da masu manyan laifuka Super Falcons ta samu gurbin buga Kofin Afrika

Duk da maganganun mutane sunan Maryam Sanda na cikin sabon jerin sunayen wadanda aka bari, bayan cire wasu.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga ne, ya tabbatar a ranar Laraba cewa an cire sunan aƙalla mutum 50 daga tsohon jerin sunayen da aka fitar bayan ce-ce-ku-cen jama’a.

“Bayan martanin jama’a, Shugaba Tinubu ya umarci a cire sunayen waɗanda aka samu da manyan laifuka kamar garkuwa da mutane, safarar miyagun ƙwayoyi, da fataucin mutane daga jerin waɗanda aka yi wa afuwa,” in ji Onanuga.

Ya ƙara da cewa an ɗauki wannan mataki ne “don mutunta ra’ayoyin jama’a, inganta haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro, da tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa da al’umma baki ɗaya.”

Tsohon jerin sunayen da aka fitar ya haifar da cece-kuce a tsakanin jam’iyyun adawa da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam.

Sun bayyana matakin a matsayin amfani da ikon shugaban ƙasa ta hanyar da ba ta dace ba, wanda hakan barazana ce ga tsarin shari’a.

Sun yi gargaɗin cewa sakin waɗanda suka aikata manyan laifuka zai iya ƙarfafa aikata laifi da kuma rage wa doka tasiri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – Zulum
  • Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
  • An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin
  • Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a
  • Duk da ce-ce-ku-ce sunan Maryam Sanda na cikin wadanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC