Barkan mu da sake haɗuwa a zauren girke-girke na watan Ramadana. Tare da fatan ana cikin koshin lafiya.
A yau na kawo wa uwargida wani girkin shuwa daga Jihar Borno, wato ‘Kamoniya’ domin yin buda baki. A sha ruwa lafiya.
Abubuwan da za ki bukata:
· Hanta · Tumbi · Huhu · Albasa 3 · Lemun tsami · Attaruhu · Man gyada · Curry da thyme · Maggi da gishiri
Yadda ake hadin:
A wanke kayan ciki (banda hanji), sai a yanka su kanana.
Sannan sai a yanka albasa a zuba man gyadan kadan a cikin tukunyar.
Bayan haka, sai a zuba curry da thyme da gishiri kadan a wankakken kayan cikin. Sai a gauraya su kafin a zuba a tukunya.
Idan an gama gaurayawa, sai a zuba su a tukunya ana juya su har sai ruwan da man sun shiga cikin kayan cikin.
Za a ga kayan cikin sun koma ruwan kasa. Sai a juye a kula a rufe. Hakan za a rika yi kadan-kadan har sai kayan cikin sun kare.
A wanke attaruhu da lemon tsami. A kirba attarugu ya kirbu sosai, sannan sai a zuba maggi wanda zai kashe zafin attaruhun.
Sai a matsa lemon tsami a kan attaruhun.
Ana cin kamoniya ne da wannan hadin attarugun. Ana dangwalawa a attaruhu don samin dandano mai gamsarwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kamoniya kayan cikin
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
Daga Ali Muhammad Rabi’u
An samu mummunan rikici tsakanin mambobin ƙungiyoyin asiri wanda ya shafi tsofaffin daliban kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kwara da ke Ilorin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutum ɗaya.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa dalibin mai suna Oyelade Olawale wanda ya karanci aikin Injiniya a fannin Gine-gine, ya rasu ne a yayin wannan rikici na kungiyoyin asiri.
An samu labarin cewa an kama wasu daga cikin wadanda ake zargi da hannu a tarzomar da ta faru a Kwalejin.
A cikin wata sanarwa, Jami’ar Hulɗa da Jama’a ta Kwalejin, Halima Garba, ta tabbatar da mutuwar matashin da kuma kama wasu mutane da ake zargi da hannu a rikicin.
Sanarwar ta yi kira ga dalibai da al’umma su rika kai rahoton duk wani abin da suke zargin zai iya haddasa fitina ga hukumomin da suka dace domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a makarantar.