Yadda ’yan Boko Haram suka sha da ƙyar a hannun tawagar Gwamna Zulum
Published: 13th, March 2025 GMT
Jami’an tsaro da ke rakiyar tawagar Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, sun daƙile wani harin Boko Haram a kusa da garin Gujba a Jihar Yobe.
Gwamnan da tawagarsa na kan hanyarsu ta komawa Maiduguri daga Biu lokacin da suka haɗu da ’yan ta’addan, wanda hakan ya tilasta musu tserewa bayan musayar wuta.
Bayanai sun ce dakarun tawagar sun ƙwato bindigogi, harsasai, babur, tare da ceto wasu fasinjoji da aka sace.
Wani direba da aka ceto, Malum Ari, ya bayyana yadda maharan suka tare hanyar: “Sun karɓe motata suka tilasta mana kwanciya a ƙasa.
“Amma da suka hango tawagar gwamna, sai suka firgita suka tsere. Wani daga cikinsu ya faɗi a kasa sau biyu kafin ya tsere saboda tsananin firgici.”
Wani fasinja da aka ceto ya koka kan yadda hare-haren suka zama ruwan dare: “Boko Haram na tare hanya da tsakar rana. Ba mu da kwanciyar hankali kwata-kwata.”
Wannan na zuwa ne kwana uku bayan da ’yan ta’adda suka kai hari gari Gujba, inda suka kashe wani ɗan sa-kai mai suna Modu Bulama, tare da ƙone gidaje da shaguna.
Wani jami’in tsaro da ya shaida lamarin ya ce, “Waɗannan ’yan ta’adda sun ƙara samun ƙarfi sosai. Suna kai hare-hare ba tare da tsoro ba. Dole a ɗauki ƙwararan matakai don tabbatar da tsaro.”
A baya-bayan nan ne mayaƙan Boko Haram suka sace wani Farfesan Jami’ar Soji ta BIU da ke Jihar Borno (NAUB) da wasu fasinjoji.
Haka kuma sun sace wani alƙalin kotun Borno, wanda daga baya suka sako shi bayan biyan kuɗin fansa mai yawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Jami an Tsaro Tawaga
এছাড়াও পড়ুন:
Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma
Paparoma Leo XIV ya halarci taron Musulunci da Kiristanci da tattaunawa tsakanin addinai a dandalin Shahidai da ke Beirut.
Bayan isowarsa, Paparoma ya samu tarba daga shugaban Mabiya addinin kirista na Lebanon Bechara Boutros al-Rahi, da shugaban Mabiya darikar Katolika na Syria Ignatius Joseph III Younan, da kuma Babban Mufti na Lebanon Sheikh Abdul Latif Derian, da Mataimakin Shugaban Majalisar koli ta Mabiya mazhabar Shi’a a Lebanon Sheikh Ali al-Khatib.
A lokacin taron, Mataimakin Shugaban Majalisar Shi’a a Lebanon ya yi maraba da Paparoma, yana mai cewa: “Muna farin ciki da zuwnku a Lebanon a madadin Majalisar da kuma daukacin mabiya mazhabar shi’a na Lebanon, Muna maraba da kuma godiya da ziyararku zuwa kasarmu a wannan mawuyacin lokaci da kasarmu ke ciki.”
Ya ƙara da cewa: “Muna fatan ziyararku za ta taimaka wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa wadda ke fama da raunukan da hare-haren Isra’ila ke ci gaba da haifarwa na zalunci.”
Ya ci gaba da cewa: “Ba ma son ɗaukar makamai, kuma muna sanya alkiblar Lebanon ta zama a hannu na gari, muna fatan duniya za ta taimaka wa ƙasarmu ta sami zaman lafiya.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Chuck Schumer: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela December 2, 2025 Najeriya: Matatar Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba December 2, 2025 Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20 December 2, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165 December 1, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya December 1, 2025 Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3 A Kasar Lebanon December 1, 2025 Kamaru: Madugun Adawa Ya Rasu A Gidan Kaso December 1, 2025 Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi December 1, 2025 Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100% December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci