Aminiya:
2025-12-13@12:36:19 GMT

Yadda ’yan Boko Haram suka sha da ƙyar a hannun tawagar Gwamna Zulum

Published: 13th, March 2025 GMT

Jami’an tsaro da ke rakiyar tawagar Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, sun daƙile wani harin Boko Haram a kusa da garin Gujba a Jihar Yobe.

Gwamnan da tawagarsa na kan hanyarsu ta komawa Maiduguri daga Biu lokacin da suka haɗu da ’yan ta’addan, wanda hakan ya tilasta musu tserewa bayan musayar wuta.

Majalisar wakilai ta dakatar da CBN daga ƙara kuɗin cajin ATM Ba abin da zai faru idan aka tsige Fubara – Wike

Bayanai sun ce dakarun tawagar sun ƙwato bindigogi, harsasai, babur, tare da ceto wasu fasinjoji da aka sace.

Wani direba da aka ceto, Malum Ari, ya bayyana yadda maharan suka tare hanyar: “Sun karɓe motata suka tilasta mana kwanciya a ƙasa.

“Amma da suka hango tawagar gwamna, sai suka firgita suka tsere. Wani daga cikinsu ya faɗi a kasa sau biyu kafin ya tsere saboda tsananin firgici.”

Wani fasinja da aka ceto ya koka kan yadda hare-haren suka zama ruwan dare: “Boko Haram na tare hanya da tsakar rana. Ba mu da kwanciyar hankali kwata-kwata.”

Wannan na zuwa ne kwana uku bayan da ’yan ta’adda suka kai hari gari Gujba, inda suka kashe wani ɗan sa-kai mai suna Modu Bulama, tare da ƙone gidaje da shaguna.

Wani jami’in tsaro da ya shaida lamarin ya ce, “Waɗannan ’yan ta’adda sun ƙara samun ƙarfi sosai. Suna kai hare-hare ba tare da tsoro ba. Dole a ɗauki ƙwararan matakai don tabbatar da tsaro.”

A baya-bayan nan ne mayaƙan Boko Haram suka sace wani Farfesan Jami’ar Soji ta BIU da ke Jihar Borno (NAUB) da wasu fasinjoji.

Haka kuma sun sace wani alƙalin kotun Borno, wanda daga baya suka sako shi bayan biyan kuɗin fansa mai yawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Jami an Tsaro Tawaga

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP

PDP wanda ke da gwamnonin 11 bayan zaben 2023, yanzu tana da biyar kawai tare da karin wasu suna nuna suna son barin jam’iyyar.

Yawancin gwamnonin da suka sauya sheka a cikin wannan lokaci sun koma APC, yayin da jam’iyyar Accord ta samu guda daya.

Gwamnonin da suka bar PDP zuwa APC su ne Umoh Eno na Akwa Ibom da Sheriff Oborebwori na Delta da Douye Diri na Bayelsa da Peter Mbah na Jihar inugu. Gwamnan Jihar Taraba, Agbu Kefas, ya dade yana son barin PDP kuma yanzu yana jiran lokaci mai ya yi ne ya shiga APC.

Akwai fargaba cewa gwamnonin Caleb Muftwang na Jihar Filato da gwamnan Zamfara, Dauda Lawal ma na iya canza sheka. Gwamnonin PDP kadai da suka bayyana a fili cewa za su tsaya cikin jam’iyyar don gyara al’amuran gida su ne gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad da abokin aikinsa na Jihar Oyo, Seyi Makinde, yayin da Ahmadu Umaru Fintiri na Adamawa ya bayyana tamkar yana son sauya sheka.

Rikicin PDP y afara kuno kai ne tun bayan zabukan 2023, baya ga gwamnoni, jam’iyyar ta rasa karin ‘yan majalisa, ciki har da manyan mambobin majalisar tarayya zuwa APC.

Daga cikin ‘yan majalisar tarayya da suka bar tsohuwarsu zuwa APC akwai Sanata Agom Jarigbe daga Jihar Kuros Ribas da Sunday Marshal Katung daga Kaduna.

Tun daga shekarar 2023 har zuwa yanzu, jam’iyyun adawa a majalisar wakilai sun rasa akalla mambobi 66 zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Babbar jam’iyyar adawa ta PDP wadda ta rasa ‘yan majalisu 44, sai LP 14, NNPP 6, ADC 1 da YPP 1.

A lokacin da aka kaddamar da majalisar a watan Yuni 2023, tsarin majalisar wakilai ya kasance APC tana da kujeru 178, PDP 115, LP 35, NNPP 19, APGA 5, SDP 2, YPP 2 da ADC 2.

Bayan guguwar sauya sheka, yawan ‘yan majalisar yanzu sun kasance kamar haka: APC 246, PDP 71, LP 21, NNPP 13, APGA 5, SDP 2, ADC 1 da YPP 1.

A ranar Juma’a da ta gabata, mambobi 16 na majalisar dokokin Jihar Ribas karkashin jagorancin shugaban majalisan, Martin Amaewhule, sun sauya sheka daga PDP zuwa APC.

Lokacin da aka kaddamar da majalisar dokoki ta kasa ta 10 a ranar 13 ga Yunin 2023, jam’iyyar APC ta rike kujeru 59 a majalisar dattawa.

Amma jam’iyyar ta kara tumbatsa zuwa samu sanatoci 76, ta wuce kashi biyu bisa uku na samun rinjaye, bayan samun sauya sheka da ‘yan majalisar dattawan suka shiga cikinta.

Lokacin da aka amince da ADC a matsayin jam’iyyar hadaka ta tsofaffin shugabannin PDP, jam’iyyar ta sami sabon rayuwa tare da shigowar manyan mambobin PDP da suka hada da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon shugaban majalisar dattawa, Dabid Mark da tsohon gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola da wasu.

Yawan wadanda ke barin PDP suna shiga APC ne, yayin da kadan daga ciki suke shiga ADC.

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Elrufai ya sauya sheka daga APC zuwa SDP, sannan daga baya ya shiga ADC.

PDP ita ce kawai babbar jam’iyya da ba ta amfana daga guguwar sauyin sheka ba, amma tana ci gaba da rasa babban adadin mambobinta.

Wani masanin siyasa kuma farfesa a fannin kimiyyar siyasa, Gbade Ojo, wanda ya yi magana da wakilinmu kan wannan batu, ya lura cewa rushewar jam’iyyun adawa yana da babban tasiri wajen yawan tserewar mambobi, yana mai cewa hakan ya kara rage gwarin gwiwar al’ummar Nijeriya.

“Idan ka kalli majalisa, APC yanzu tana da gagarumi rinjaye a duka majalisar wakilai da majalisar dattawa. Ayyukan sa ido nasu suna da rauni sosai saboda shugaban kasa ya nada jami’an da su ne za su je su gudanar da ayyukan sa ido a kansu. Amma yawancinsu yanzu suna cikin jam’iyyar gwamnati,” in ji shi.

Sau da dama PDP ta yi kokari dawo da martabar jam’iyyar. Ta gudanar da babban taro a matakin gundumomi da karamar hukumomi da jihohi da dama kuma kasa baki daya, inda mambobi suka zabi sabon shugaban jam’iyyar na kasa.

Amma lamarin ya ci tura, inda magoya bayan ministan Abuja, Nyesom Wike suka kalubalantar babban taron.

Wasu na cewa ko da an gudanar da babban taron zaben, jam’iyyar ta kasa haifar da irin amincewar da zai sa mambobinta su ci gaba da kasancewa wuri guda.

Duk da yake akwai alamun da ke cewa ko wadanda suka saura na iya barin jam’iyyar a kowane lokaci.

Masana na cewa ci gaban rikicin a jam’iyyar da shari’o’i da dama na iya sanya ‘yan takararta a 2027 cikin hadari ta fuskar doka, musamman gwamnonin da ke neman wa’adi na biyu su nemi wasu jam’iyyar.

A hankali, ADC tana samun karuwa a matsayin babban jam’iyyar adawa a kasar, tana matsar da PDP zuwa baya, wacce ta rike wannan matsayi tun bayan ta fadi a zaben shugaban kasa a 2015, zuwa matsayi na biyu.

A kwanan nan, jam’iyyar ta ce tana shirin karbar sama da mambobin majalisar ta 10 guda 100 kafin zaben shekarar 2027.

A halin yanzu APC na da yawancin ‘yan majalisa a duka majalisun dokoki kasar nan tare da zargin cewa wasu na shirin shiga jam’iyyar.

Akwai rahotannin da ke cewa a jihohi kamar Benuwai, Kano, Adamawa da Yobe cewa ADC ta kafu kuma za ta bunkasa c

ikin ‘yan watanni kadan masu zuwa.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa December 12, 2025 Manyan Labarai Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su December 12, 2025 Manyan Labarai Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro December 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Kotu Ta Umarci EFCC Ta Biya Wani Ƴan Kasuwar Kano Miliyan 5, Ta Nemi Afuwar Su
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Yadda APC Da ADC Ke Amfana Da Rikicin Jam’iyyar PDP
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano
  • Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota
  • Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a Yobe
  • EFCC ta tsare Malami kan binciken kuɗaɗen Abacha
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara