Aminiya:
2025-11-07@07:32:46 GMT

Yadda ’yan Boko Haram suka sha da ƙyar a hannun tawagar Gwamna Zulum

Published: 13th, March 2025 GMT

Jami’an tsaro da ke rakiyar tawagar Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, sun daƙile wani harin Boko Haram a kusa da garin Gujba a Jihar Yobe.

Gwamnan da tawagarsa na kan hanyarsu ta komawa Maiduguri daga Biu lokacin da suka haɗu da ’yan ta’addan, wanda hakan ya tilasta musu tserewa bayan musayar wuta.

Majalisar wakilai ta dakatar da CBN daga ƙara kuɗin cajin ATM Ba abin da zai faru idan aka tsige Fubara – Wike

Bayanai sun ce dakarun tawagar sun ƙwato bindigogi, harsasai, babur, tare da ceto wasu fasinjoji da aka sace.

Wani direba da aka ceto, Malum Ari, ya bayyana yadda maharan suka tare hanyar: “Sun karɓe motata suka tilasta mana kwanciya a ƙasa.

“Amma da suka hango tawagar gwamna, sai suka firgita suka tsere. Wani daga cikinsu ya faɗi a kasa sau biyu kafin ya tsere saboda tsananin firgici.”

Wani fasinja da aka ceto ya koka kan yadda hare-haren suka zama ruwan dare: “Boko Haram na tare hanya da tsakar rana. Ba mu da kwanciyar hankali kwata-kwata.”

Wannan na zuwa ne kwana uku bayan da ’yan ta’adda suka kai hari gari Gujba, inda suka kashe wani ɗan sa-kai mai suna Modu Bulama, tare da ƙone gidaje da shaguna.

Wani jami’in tsaro da ya shaida lamarin ya ce, “Waɗannan ’yan ta’adda sun ƙara samun ƙarfi sosai. Suna kai hare-hare ba tare da tsoro ba. Dole a ɗauki ƙwararan matakai don tabbatar da tsaro.”

A baya-bayan nan ne mayaƙan Boko Haram suka sace wani Farfesan Jami’ar Soji ta BIU da ke Jihar Borno (NAUB) da wasu fasinjoji.

Haka kuma sun sace wani alƙalin kotun Borno, wanda daga baya suka sako shi bayan biyan kuɗin fansa mai yawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram Jami an Tsaro Tawaga

এছাড়াও পড়ুন:

Ajax ta kori kocinta John Heitinga

Kungiyar kwallon ƙafa ta Ajax da ke ƙasar Netherlands ta sanar da sallamar kocinta, John Heitinga, a sakamakon rashin kataɓus da a yanzu ƙungiyar ta maƙale a ƙasan teburin gasar Zakarun Turai ta Champions League.

A wata sanarwa da ta Ajax ta fitar a ranar Alhamis, ta ce tana neman sabon koci, inda a halin yanzu, Fred Grim zai riƙe aikin Heitinga har zuwa lokacin da za a naɗa sabon mai horarwa.

Cin zarafin Wakilin NTA ya tada ƙura a Yobe An rantsar da shugaban Kamaru Paul Biya karo na 8

Heitinga, wanda ya sanya hannu kan kwantiragi na shekaru biyu a watan Mayu, ya gaza sauya akalar ƙungiyar, lamarin da Ajax ɗin ta tabbatar cewa ta kawo ƙarshen yarjejeniyar.

Daraktan fasaha na kulob ɗin, Alex Kroes, ya bayyana cewa wannan mataki “yana da raɗaɗi”, amma ya ce ya zama dole don ci gaban ƙungiyar.

“Mun san yana ɗaukar lokaci kafin sabon koci ya daidaita tawagar da aka yi mata zubin sabbin ‘yan wasa. Mun ba John wannan damar, amma yanzu mun ga ya dace mu naɗa wani sabon mutum,” in ji Kroes.

Mummunan sakamako na ƙarshe shi ne rashin nasarar da Ajax ɗin ta yi har gida a hannun Galatasaray a gasar Champions League, wadda ta doke ta 3-0 a ranar Laraba. Wannan na zuwa ne bayan da kwasar kashinta a hannun da ta yi yayin da Chelsea ta doke ta 5-1 a baya.

Haka kuma, Ajax ta sha kashi a hannun Marseille wadda ta doke ta 4-0, sai kuma ci 2-0 a hannun Inter Milan, lamarin da ya sa ta gaza samun ko da maki ɗaya a babbar gasar ta Turai.

A lig ɗin gida kuwa, Ajax tana matsayi na huɗu a teburin Eredivisie, da tazarar maki takwas tsakaninta da Feyenoord da PSV Eindhoven.

Magoya bayan kulob ɗin sun yi zanga-zangar rashin jin daɗi saboda yawan sauye-sauyen da Heitinga ke yi yayin wasanni, yayin da wasu ke ganin lokaci ya ƙure masa.

Sai dai ƙungiyar magoya bayan Ajax ta bayyana rashin jin daɗi bisa korar Heitinga, tana mai cewa: “Duk abin da muke so shi ne mu ga Ajax tana samun nasara, saboda haka rabuwa juna ba zai kai ga nasara ba.”

Heitinga dai tsohon ɗan wasan Ajax ne da ya buga wa ƙasarsa Netherlands wasanni 87.

Haka kuma, ya taɓa murza leda a Atletico Madrid, Everton da Fulham.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ajax ta kori kocinta John Heitinga
  • Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
  • Ta yi garkuwa da kanta don karbar kuɗin fansa daga hannun mijinta
  • ‘YanSandan Jihar Kwara Sun Ceto Wasu Mutane Da Aka Yi Garkuwa Da Su
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Farmaki Ga Wani Dan Majalisa A Jihar Niger
  • Ayatollah Khamenei: Rikici Tsakanin Iran da Amurka na asasi
  • DAGA LARABA: Yadda ‘Yanbindiga Ke Amfani Da Hakar Zinare Wajen Mallakar Makamai
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara
  • KADUNA TA ZAMA JIHAR FARKO A NIJERIYA DA TA AIWATAR DA SHIRIN SAMAR DA ABINCIN MAI GINA JIKI GA YARA – UNICEF