Yadda ’yan Boko Haram suka sha da ƙyar a hannun tawagar Gwamna Zulum
Published: 13th, March 2025 GMT
Jami’an tsaro da ke rakiyar tawagar Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, sun daƙile wani harin Boko Haram a kusa da garin Gujba a Jihar Yobe.
Gwamnan da tawagarsa na kan hanyarsu ta komawa Maiduguri daga Biu lokacin da suka haɗu da ’yan ta’addan, wanda hakan ya tilasta musu tserewa bayan musayar wuta.
Bayanai sun ce dakarun tawagar sun ƙwato bindigogi, harsasai, babur, tare da ceto wasu fasinjoji da aka sace.
Wani direba da aka ceto, Malum Ari, ya bayyana yadda maharan suka tare hanyar: “Sun karɓe motata suka tilasta mana kwanciya a ƙasa.
“Amma da suka hango tawagar gwamna, sai suka firgita suka tsere. Wani daga cikinsu ya faɗi a kasa sau biyu kafin ya tsere saboda tsananin firgici.”
Wani fasinja da aka ceto ya koka kan yadda hare-haren suka zama ruwan dare: “Boko Haram na tare hanya da tsakar rana. Ba mu da kwanciyar hankali kwata-kwata.”
Wannan na zuwa ne kwana uku bayan da ’yan ta’adda suka kai hari gari Gujba, inda suka kashe wani ɗan sa-kai mai suna Modu Bulama, tare da ƙone gidaje da shaguna.
Wani jami’in tsaro da ya shaida lamarin ya ce, “Waɗannan ’yan ta’adda sun ƙara samun ƙarfi sosai. Suna kai hare-hare ba tare da tsoro ba. Dole a ɗauki ƙwararan matakai don tabbatar da tsaro.”
A baya-bayan nan ne mayaƙan Boko Haram suka sace wani Farfesan Jami’ar Soji ta BIU da ke Jihar Borno (NAUB) da wasu fasinjoji.
Haka kuma sun sace wani alƙalin kotun Borno, wanda daga baya suka sako shi bayan biyan kuɗin fansa mai yawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Jami an Tsaro Tawaga
এছাড়াও পড়ুন:
DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci
Kungiyar ‘yan tawayen kasar DRC ta M23 ta kwace iko da wani gari mai muhimmanci bayan rushewar batun zaman lafiya
A jiya Juma’a ne dai kasar Amurka ta zargi kasar Rwanda da cewa ta keta yarjejeniyar sulhu da zaman lafita da ta kulla da DRC, tare da cewa, abinda Kigalin take yi shi ne jefa yankin zuwa yaki.
Mako daya da ya gabata ne dai aka kulla yarjejeniyar sulhu a tsakanin kasashen biyu wacce shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa; Ta tarihi ce.” Tare da nuna fatan ganin an sami zaman lafiya a cikin wannan yankin wanda ya dade cikin fadace-fadace.
Sai dai a ranar Larabar da ta gabata da yamma mayakan kungiyar M23 wacce Rwanda take goyawa baya sun sanar da kama garin Uvira wanda daya daga cikin muhimman wuraren da suke a hannun sojojin gwamnatin kasar a gabashin kasar.
Dama dai tun a baya wasu kwararru na MDD sun zargi Kigali da cewa, ita ce mai iko da akan dukkanin hare-haren da ‘yan tawayen suke kai wa a gabashin DRC.
Jakadan Amurka a MDD Mike Waltz ya ce; Amurka ba ta ji dadin abinda ya faru ba ko kadan, domin ya rusa yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla.
Su dai ‘yan tawayen ba su cikin yarjejeniyar zaman lafiyar da aka kulla da Amurka kai tsaye, amma da suna cikin tattaunawar da ake yi da kasar Qatar.
Amurka dai ta shiga cikin Shirin zaman lafiya a cikin DRC, domin ta sami damar dibar ma’adanai da Allah ya huwacewa wannan kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara December 13, 2025 Kalibaf: Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169 December 13, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta December 13, 2025 Ziyarar Da Shugaban Rasha Ya Kai Indiya Ta Kara Karfafa Dangantakar Mosko Da Delhi December 13, 2025 Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na Venuzuela December 13, 2025 Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita. December 13, 2025 Matatar Mai ta Dangote Ta Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 699 December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci