Leadership News Hausa:
2025-11-22@22:18:46 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Published: 13th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Wannan magana tana nuni da cewa idan mutum ya nemi kariya a wurin Allah da zuciya ɗaya, to Allah zai amsa roƙonsa kuma zai kare shi daga duk wani abu mai cutarwa. Wannan yana da asali a cikin koyarwar Musulunci, inda ake koyar da Musulumi su nemi tsari wurin Allah kaɗai daga sharrin Shaiɗanun aljanu da mutane da duka wani maicutarwa a cikin halittu baki ɗaya, da kuma neman tsari da kariya daga miyagun halaye, da duk wani abu da zai cutar da su a duniya da lahira.

Allah Ya yi umurni da a nemi tsari da kariya a wurinsa inda Ya ce: “ Idan kuma wani tunzuri daga Shaiɗan ya tunzura ka, to sai ka nemi tsari daga Allah; lalle Shi mai ji ne, Masani” Suratu Fussilat aya ta 36.

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [1] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [2]

A taƙaice, wannan magana ta Ibnu Juzai a-Kalbi tana da muhimmanci sosai a rayuwar Musulumi, domin tana ƙarfafa imani da cewa duk wanda ya dogara ga Allah kuma ya nemi kariya da gaske, Allah zai kare shi daga duk wani sharri. Wannan yana ƙarfafa Musulumi su kasance masu gaskiya a addu’arsu da neman tsari da Allah cikin kowane hali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su

’Yan bindigar da suka yi garkuwa da masu ibada a cocin Christ Apostolic Church da ke Eruku, a jihar Kwara, sun nemi Naira miliyan 100 a matsayin kudin fansar kowanne mutum da suka kama.

A cewar Faston cocin, Lawrence Bamidele, tsakanin mutane 30 zuwa 35 aka yi garkuwa da su a daren Talata lokacin da aka kai musu mummunan hari suna tsaka da ibada a cocin.

Sace ɗalibai: Tinubu ya bai wa Ministan Tsaro umarnin tarewa a Kebbi Muna roƙon Tinubu ya ƙawo ƙarshen taƙaddamar gwamnati da ASUU — Ɗalibai

Majiyoyi daga iyalai da shugabannin al’umma sun tabbatar a ranar Alhamis cewa masu garkuwar sun fara kiran ’yan uwan waɗanda aka sace ta hanyar amfani da wayoyinsu.

Sakataren cocin, Josiah Agbabiaka, ya ce tuni aka fara tuntubar wasu daga cikin dangin wadanda aka sace din.

Ya ce, “Gaskiya ne cewa ’yan bindigar sun fara kiran ’yan uwa ta amfani da wayoyin waɗanda aka sace don neman kudin fansa,” in ji Agbabiaka.
“Abin da aka shaida mana shi ne sun raba waɗanda aka sace gida-gida. Rukunin farko na mutane 11 an nemi su biya Naira miliyan 100 kowanne.”

Basaraken gargajiya na yankin, Olori Eta, Cif Olusegun Olukotun, wanda ’yan uwansa huɗu na cikin waɗanda aka sace, ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa masu garkuwar suna kiran dangin wadanda aka sace daya bayan daya.

“’Yan bindigar sun fara kiran wasu suna neman Naira miliyan 100 kan kowanne mutum. Sun ce sun raba waɗanda aka sace gida-gida, kuma suna kiran danginsu,” in ji shi.

Olukotun ya ce yana cikin cocin tare da ’yan uwansa biyar lokacin harin, inda ya ce ya tsere ta taga yayin da sauran aka tafi da su.

Jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ’yan sanda ta Jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ta ce rundunar ba ta samu wani rahoto a hukumance ba kan neman kudin fansar.

“Ba mu da masaniya kan wani neman kudin fansa ko tuntubar iyalan waɗanda aka sace,” in ji ta a ranar Alhamis.
“Dakarunmu na musamman tare da sojoji da sauran jami’an tsaro suna kan aiki don ceto waɗanda aka yi garkuwar da su.”

Ejire-Adeyemi ta ƙara da cewa Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Adekimi Ojo, ya roƙi al’umma da iyalan waɗanda aka sace da su bayar da bayanan da za su taimaka wa jami’an tsaro wajen aikin ceto mutanen kuma a kan lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya ta musanta jita-jitar rufe dukkanin makarantu a faɗin Najeriya
  • Atiku ya nemi a ayyana dokar ta-ɓaci kan satar ɗalibai a Najeriya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja
  • ’Yan bindiga sun sace dalibai a wata makarantar Neja
  • ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai da Malamai a Jihar Neja
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas
  • Yadda maganin sauro ya yi ajalin magidanci da iyalinsa a Kano
  • AU ta yi Allah-wadai da tsoma bakin kasashen waje a harkokin tsaron Afirka