Leadership News Hausa:
2025-11-18@15:36:52 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Published: 13th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Wannan magana tana nuni da cewa idan mutum ya nemi kariya a wurin Allah da zuciya ɗaya, to Allah zai amsa roƙonsa kuma zai kare shi daga duk wani abu mai cutarwa. Wannan yana da asali a cikin koyarwar Musulunci, inda ake koyar da Musulumi su nemi tsari wurin Allah kaɗai daga sharrin Shaiɗanun aljanu da mutane da duka wani maicutarwa a cikin halittu baki ɗaya, da kuma neman tsari da kariya daga miyagun halaye, da duk wani abu da zai cutar da su a duniya da lahira.

Allah Ya yi umurni da a nemi tsari da kariya a wurinsa inda Ya ce: “ Idan kuma wani tunzuri daga Shaiɗan ya tunzura ka, to sai ka nemi tsari daga Allah; lalle Shi mai ji ne, Masani” Suratu Fussilat aya ta 36.

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [1] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [2]

A taƙaice, wannan magana ta Ibnu Juzai a-Kalbi tana da muhimmanci sosai a rayuwar Musulumi, domin tana ƙarfafa imani da cewa duk wanda ya dogara ga Allah kuma ya nemi kariya da gaske, Allah zai kare shi daga duk wani sharri. Wannan yana ƙarfafa Musulumi su kasance masu gaskiya a addu’arsu da neman tsari da Allah cikin kowane hali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan bindiga sun kai hari a makarantar Government Girls Comprehensive Senior Secondary School (GGCSS), Maga, da ke ƙaramar hukumar Danko/Wasagu a Jihar Kebbi, inda suka kashe Mataimakin Shugaban makarantar, Hassan Yakubu Makuku, tare da sace wasu ɗalibai mata da ba a san adadinsu ba. Al’ummar yankin sun ce harin ya sake tayar da hankula a garin, wanda ke fama da yawan hare-hare a kwanakin nan.

Wani mazaunin Maga, Aliyu Yakubu, ya ce maharan sun shigo makarantar ne kimanin ƙarfe 5 na safiyar Litinin, ba tare da wata ƙwaƙƙwarar musayar wuta daga jami’an tsaro ba. Ya bayyana cewa harin ya jefa mazauna yankin cikin firgici da tashin hankali, abin da ya sa jama’a ke cikin tsananin damuwa da alhini.

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Yakubu ya ce sun harbe Shugaban Makarantar ne a lokacin da yake ƙoƙarin kare ɗalibansa daga faɗawa hannun ƴan bindigar. Ya bayyana rasuwar tasa a matsayin babban rashi ga makarantar da kuma al’ummar yankin gaba ɗaya.

ADVERTISEMENT

Daily Trust ta rawaito cewa, a halin da ake ciki, babu wata sanarwa daga Rundunar ƴansanda Jihar Kebbi game da harin. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Nafiu Abubakar, bai amsa kiran waya da dama da aka yi masa ba yayin rubuta wannan rahoto.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka November 17, 2025 Manyan Labarai Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda November 17, 2025 Manyan Labarai Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon November 17, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana
  • Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi
  • MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
  • Ansarullah Ta Yi Allah Wadai Da Sabunta Takunkumin MDD Kan Yemen
  • Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
  • Fintiri ya yi watsi da korar Wike daga PDP
  • Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA
  • Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba