Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]
Published: 13th, March 2025 GMT
Wannan magana tana nuni da cewa idan mutum ya nemi kariya a wurin Allah da zuciya ɗaya, to Allah zai amsa roƙonsa kuma zai kare shi daga duk wani abu mai cutarwa. Wannan yana da asali a cikin koyarwar Musulunci, inda ake koyar da Musulumi su nemi tsari wurin Allah kaɗai daga sharrin Shaiɗanun aljanu da mutane da duka wani maicutarwa a cikin halittu baki ɗaya, da kuma neman tsari da kariya daga miyagun halaye, da duk wani abu da zai cutar da su a duniya da lahira.
A taƙaice, wannan magana ta Ibnu Juzai a-Kalbi tana da muhimmanci sosai a rayuwar Musulumi, domin tana ƙarfafa imani da cewa duk wanda ya dogara ga Allah kuma ya nemi kariya da gaske, Allah zai kare shi daga duk wani sharri. Wannan yana ƙarfafa Musulumi su kasance masu gaskiya a addu’arsu da neman tsari da Allah cikin kowane hali.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Ta yi garkuwa da kanta don karbar kuɗin fansa daga hannun mijinta
Jami’an Rundunar ’Yan Sandan Jihar Edo sun kama wata mata mai suna Chioma Success mai shekaru 27, bisa zargin kitsa garkuwa da kanta don karɓar kuɗin fansa daga mijinta.
An kuma kama wasu mutum biyu da ake zargin sun taimaka mata wajen aikata laifin, wato Martins Chidozie mai shekaru 23 da Osita Godfrey mai shekaru 33.
Mamdani ya zama Musulmi na farko da ya zama magajin garin New York na Amurka Tinubu na neman majalisa ta amince masa ya ciyo sabon bashin Tiriliyan 1.150Mataimakiyar Kakakin rundunar a jihar, ASP Eno Ikoedem, ta ce an kama waɗanda ake zargin ne bayan bincike kan wani rahoton garkuwa da aka kai wa ’yan sanda.
Ta ce a ranar 27 ga Oktoba, 2025, wani mutum mai suna Paul Adaniken ya kai rahoto a ofishin ’yan sanda na New Etete cewa ya bar matarsa, Chioma Success Ezebie, da ɗansu mai shekaru uku, Andrea Ojiezelabor, a gida kafin ya tafi shagonsa.
A cewarta, daga bisani an kira shi da wata lamba da bai sani ba, ana sanar da shi cewa an yi garkuwa da matarsa da ɗansa.
Mai magana da yawun rundunar ta ce masu garkuwa sun nemi a biya su kuɗin fansa naira miliyan 5 kafin su sako su.
Ta ce yayin bincike, an gano cewa ɗan uwanta, Osita Godfrey, wanda a baya ake zaton yana taimakawa da bayani, shi ma yana da hannu a cikin laifin, kuma an kama shi.
Ta ƙara da cewa bayanin da Godfrey ya bayar ya kai ga kama Chioma Success, wadda ta haɗa baki da abokan aikinta don ƙitsa garkuwa da kanta da nufin karɓar kuɗi daga mijinta.
Ta ce an kuma kama wani da ake zargi, Martins Chidozie, dangane da laifin.
ASP Eno Ikoedem ta tabbatar da cewa an kwato kuɗin fansar da aka biya na naira miliyan biyar, kuma yanzu haka an mika batun zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka na Rundunar (SCID) domin ci gaba da bincike da gurfanar da wadanda ake zargin a kotu.