Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]
Published: 13th, March 2025 GMT
Wannan magana tana nuni da cewa idan mutum ya nemi kariya a wurin Allah da zuciya ɗaya, to Allah zai amsa roƙonsa kuma zai kare shi daga duk wani abu mai cutarwa. Wannan yana da asali a cikin koyarwar Musulunci, inda ake koyar da Musulumi su nemi tsari wurin Allah kaɗai daga sharrin Shaiɗanun aljanu da mutane da duka wani maicutarwa a cikin halittu baki ɗaya, da kuma neman tsari da kariya daga miyagun halaye, da duk wani abu da zai cutar da su a duniya da lahira.
A taƙaice, wannan magana ta Ibnu Juzai a-Kalbi tana da muhimmanci sosai a rayuwar Musulumi, domin tana ƙarfafa imani da cewa duk wanda ya dogara ga Allah kuma ya nemi kariya da gaske, Allah zai kare shi daga duk wani sharri. Wannan yana ƙarfafa Musulumi su kasance masu gaskiya a addu’arsu da neman tsari da Allah cikin kowane hali.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC
Kakakin Majalisar Dokokin jihar Ribas, Martin Amaewhule tare da mambobin majalisar su 15 sun sanar da sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Amaewhule ya bayyana shawarar ’yan majalisar ne a zaman majalisa na ranar Juma’a, inda ya ce akwai abin da ya kira “rarrabuwar kai a fili” a cikin PDP wanda ya sa suka yanke wannan shawara.
Muna tafe da karin bayanai…