Leadership News Hausa:
2025-03-28@09:37:54 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Published: 13th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [5]

Wannan magana tana nuni da cewa idan mutum ya nemi kariya a wurin Allah da zuciya ɗaya, to Allah zai amsa roƙonsa kuma zai kare shi daga duk wani abu mai cutarwa. Wannan yana da asali a cikin koyarwar Musulunci, inda ake koyar da Musulumi su nemi tsari wurin Allah kaɗai daga sharrin Shaiɗanun aljanu da mutane da duka wani maicutarwa a cikin halittu baki ɗaya, da kuma neman tsari da kariya daga miyagun halaye, da duk wani abu da zai cutar da su a duniya da lahira.

Allah Ya yi umurni da a nemi tsari da kariya a wurinsa inda Ya ce: “ Idan kuma wani tunzuri daga Shaiɗan ya tunzura ka, to sai ka nemi tsari daga Allah; lalle Shi mai ji ne, Masani” Suratu Fussilat aya ta 36.

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [1] Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [2]

A taƙaice, wannan magana ta Ibnu Juzai a-Kalbi tana da muhimmanci sosai a rayuwar Musulumi, domin tana ƙarfafa imani da cewa duk wanda ya dogara ga Allah kuma ya nemi kariya da gaske, Allah zai kare shi daga duk wani sharri. Wannan yana ƙarfafa Musulumi su kasance masu gaskiya a addu’arsu da neman tsari da Allah cikin kowane hali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

 Nigeria: An  Kashe Sojoji Da DAma A Wani Hari Da Aka Kai Wa Sansanonin Soja Biyu Hari A Jihar Borno

Kamfanin dillancin labarun “Reuters” ya nakalto cewa; An kai harinn ne wanda ya yi sanadiyyar mutuwa da kuma jikkatar wasu sojoji da dama a wasu sansanoni biyu dake Jihar Borno.

Mayakan kungiyoyin Boko Haram da Daesh suna kai wa fararen hula hare-hare a kasashen yammacin Afirka daga ciki har da Najeriya, inda suke kashe fararen hula da jami’an tsaro.

 Majiyar ta kamfanin dillancin labarun “Reuters’ ta ce, kungiyoyin na “Da’esh’ da Boko Haram sun kai harin ne a yankin Wajiroko dake jihar borno, tare da cinna wuta a wurin da hakan ya yi sanadiyyar konewar kayan soja.

Wani soja ya bayyana cewa, a kalla 4 daga cikin sojoji ne su ka wanta dama sanadiyyar wannan harin, tare da jikkata wasu da dama daga cikinsu har da kwamanda.

Wasu madau dauke da makaman sun kai wani harin ne a garin Wolgu dake kan iyaka da kasar Kamaru, sai dai babu cikakken bayani akan yawan wadanda su ka kwanta dama ko su ka jikkata.

Wani daga cikin rundunar farar hula masu taimakawa sojoji a yaki da Bko haram din, mai suna Makinta Modu, ya fada wa manema labaru cewa, maharani sun kwace iko da sansanin sojan da su ka kai wa hari a Wajiroko.

Sai dai kuma an kawo  dauki daga sojan sama da misalin karfi 10;30 na dare, da su ka yi nasarar kashe masu dauke da makaman da dama.. Sai dai babu cikakken bayani akan ko sojojin sun sake kwato sansanin nasu da ya shiga hannun ‘yan ta’adda.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [20]
  • Miliyoyin  ‘Yahudawa Sun Gudu Neman Mafaka Saboda Makamin Mai Linzami Daga Yemen
  • Wani abu kan Zakkatul Fidir da Sallar Idi
  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Matasa Suka Tsinci Kansu A Najeriya
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]
  •  Nigeria: An  Kashe Sojoji Da DAma A Wani Hari Da Aka Kai Wa Sansanonin Soja Biyu Hari A Jihar Borno
  • Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina
  • Boko Haram Ta Kashe Sojoji A Wani Sabon Hari A Borno
  • Wani Bawan Allah Ya Rasu Jim Kadan Bayan Sallar Asuba A Wani Masallaci A Abuja
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]