“Bayan samun rahoton, jami’in ‘yansanda reshen Faskari ya yi gaggawar tara tawagar jami’an tsaro zuwa wurin.

 

“Rundunar ta hanyar amfani da dabaru, ta yi kwanton bauna, inda ta rikita ‘yan bindigar da ruwan harsashi wanda ya hakan ya ta tilasta musu guduwa da raunuka daban-daban, an yi nasarar ceto dukkan mutanen 30 da aka yi garkuwa da su ba tare da sun ji rauni ba, kuma an kwato dabbobin da suka sace.

 

“Kwamishanan ‘yansandan jihar Katsina, CP Aliyu Abubakar Musa, ya yaba wa jami’an da suka nuna kwazo da jajircewa wajen gudanar da aikin ceto, ya bukaci jama’ar jihar da su ci gaba da bayar da hadin kai ga rundunar ta hanyar samar da sahihin bayanai a kan lokaci domin daukar matakin gaggawa kan masu aikata muggan laifuka,” In ji Sadiq

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sanadiyar Hare-Haren HKI Ya Dara 400

HKI ta keta yarjeniyar tsagaita wuta a Gaza, a jiya inda ta kai hare-hare masu yawa, wadanda suka yi sanadiyar mutuwar mutane fiye da 300 ya zuwa safiyar yau.

Tashar talanijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, jiragen yakin HKI sun kai hare-haren a kan yankunan zirin Gaza da dama, kuma yawan mutanen da suka yi shahada ya zuwa yanzu ya kai 342 kumamafi yawansu mata da yara ne.

Labarin ya kara da cewa a garin Khan Yunus na kudancin Gaza jiragen yakin HKI sun kashe falasdinawa 77 sannan falasdinawa akalla 20 suka kashe a birnin Gaza. SAMA kamfanin dillancin labaran Falasdinawa ya bayyana cewa daruruwan Falasdinawa sun rasa rayukansu, kuma har yanzun ana neman wasu a wuraren da yahudawan suak kai hare hare.

Tashar talabijin ta Aljazeera ta bada labarin cewa hare-haren yahudawan sun game dukkan zirin gaza kuma sai da suka girgiza yanking aba daya.

Wasu masana suna ganin sojojin yahudawan sun yi amfani da sabbin makamai masu tun 20 wadanda gwamnatin Trump ta bawa HKI bayan ya dare kan kujerar shugabancin kasar ta Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 84, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 3 A Katsina
  • Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 10, Sun Ceto Mutane 101 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara.
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
  • ’Yan Banga Sun Ceto Mutum 3 Daga Hannun ’Yan Bindiga A Taraba
  • Za Mu Bi Doka Domin Dawo Da Haƙƙinmu – Fubara
  • ‘Yansanda Sun Kama Wata Mata Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Katsina
  • Gaza: Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sanadiyar Hare-Haren HKI Ya Dara 400
  • Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
  • Me Ya Sa Ba Za a Ba Yankin Taiwan Damar Samun ‘Yancin Kai Ba?