“Bayan samun rahoton, jami’in ‘yansanda reshen Faskari ya yi gaggawar tara tawagar jami’an tsaro zuwa wurin.

 

“Rundunar ta hanyar amfani da dabaru, ta yi kwanton bauna, inda ta rikita ‘yan bindigar da ruwan harsashi wanda ya hakan ya ta tilasta musu guduwa da raunuka daban-daban, an yi nasarar ceto dukkan mutanen 30 da aka yi garkuwa da su ba tare da sun ji rauni ba, kuma an kwato dabbobin da suka sace.

 

“Kwamishanan ‘yansandan jihar Katsina, CP Aliyu Abubakar Musa, ya yaba wa jami’an da suka nuna kwazo da jajircewa wajen gudanar da aikin ceto, ya bukaci jama’ar jihar da su ci gaba da bayar da hadin kai ga rundunar ta hanyar samar da sahihin bayanai a kan lokaci domin daukar matakin gaggawa kan masu aikata muggan laifuka,” In ji Sadiq

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC

Kusoshin gwamnatin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari sun shiga haɗakar jam’iyyun adawa ta ADC da nufin kayar da Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta APC.

Tsofaffin mukarraban gwamnatin Buhari da suka koma haɗakar ADC sun haɗa da tsofaffin ministoci da tsofaffin gwamnoni da masu muƙaman siyasa.

Yawanci sun raba gari da APC ne saboda zargin an yi musu rashin adalci a jam’iyyar da kuma gazawar Gwamnatin Tinubu wajen magance matsalolin da ke ci wa ’yan Najeriya tuwo a ƙwarya.

1- Nasiru El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai na gaba ne a tafiyar haɗakar inda tun farko ya lashi takobin ƙalubalantar gwamnatin Tinubu a zaɓen 2027.

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta? Rasha ta amince da gwamnatin Taliban a Afghanistan

Fara maganar haɗakar ke da wuya aka ga El-Rufai a gidan Buhari da ke Kaduna, inda ya sanar da ficewarsa daga APC.

Daga bisani El-Rufai tare da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar da wasu jaga-jigan ’yan APC a gwamnatin Buhari suka ziyarci shugaba kasan.

An yi zargin sun je ne domin neman albarkarsa domin ya amince wa ’yan tsohuwar jam’iyyarsa ta CPC su fice daga APC su shiga haɗakar.

2- Abubakar Malami

Ministan Shari’a a wa’adi biyu da Buhari ya yi, ya sanar da ficewarsa daga APC da kuma aniyarsu ta yaƙar Gwamnatin Tinubu a zaɓen 2027 saboda ta jefa ’yan Najeriya cikin halin ƙaƙa-ni-ka-yi da kuma gaza magance matsalolin tsaro da na tattalin arziki.

Tsohon ministan shari’an, kuma wanda tsohon wanda a baya ya nemi takarar Gwamnan Jihar Kebbi, an lura ya yi baya-baya a harkokin APC tun bayan hawan mulkin Tinubu.

3- Hadi Sirika

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama a zamanin Buhari, dan asalin Jihar Katsina ne, wato mahaifar tsohon shugaban ƙasan.

Hadi Siriya sun jima da taba da raba gari da Gwamnatin Tinubu kuma a halin yanzu yana fuskantar shari’a kan zargin karkatar da kuɗaɗen kwangila da sauran zarge-zarge a ma’aikatar sufurin jiragen sama.

4- Rotimi Amaechi

Tsohon Ministan Sufuri a zamanin Buhari, kuma tsohon Gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, ya bayyana aniyarsa ta fitowa takarar shugaban ƙasa a ADC.

Amaechi kamar takwarorinsa da suka fice daga APC bisa zargin an yi musu ba daidai ba, na zargin gwamnatin Tinubu da gazawa.

5- Rauf Aregbesola

Tsohon Gwamnan Jihar Osun wanda Buhari ya naɗa Ministan Harkokin Cikin Gida, tsohon na hannun daman Tinubu ne.

A halin yanzu shi ne ADC ta nada a matsayin Sakataren Jam’iyya.

6- Solomon Dalung

Tsohon Ministan Wasanni ya daga cikin waɗanda suka shiga wannan haɗaka ta ADC.

Ko da yake wa’adi daya kadai Dalung ya yi minista a zamanin Buhari, ida gaba bisani ya koma sukan kamun ludayin gwamnatin.

Bayan shafe watanni ana tattaunawa kan haɗakar jam’iyyun adawar ne dai a ranar Laraba suka ƙaddamar da shugabannin riƙo a ƙarƙashin jagorancin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata David Mark.

Haka kuma sun naɗa tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola a matsayin sakataren riko na ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
  • An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa
  • Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano
  • ’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
  • NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
  • Makusantan Gwamnatin Buhari da suka shiga haɗakar ADC
  • Filato: Mahara sun cire hannun matashi a kan hanyar komawa gida daga jana’iza
  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3