‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutanen 30 A Katsina
Published: 12th, March 2025 GMT
“Bayan samun rahoton, jami’in ‘yansanda reshen Faskari ya yi gaggawar tara tawagar jami’an tsaro zuwa wurin.
“Rundunar ta hanyar amfani da dabaru, ta yi kwanton bauna, inda ta rikita ‘yan bindigar da ruwan harsashi wanda ya hakan ya ta tilasta musu guduwa da raunuka daban-daban, an yi nasarar ceto dukkan mutanen 30 da aka yi garkuwa da su ba tare da sun ji rauni ba, kuma an kwato dabbobin da suka sace.
“Kwamishanan ‘yansandan jihar Katsina, CP Aliyu Abubakar Musa, ya yaba wa jami’an da suka nuna kwazo da jajircewa wajen gudanar da aikin ceto, ya bukaci jama’ar jihar da su ci gaba da bayar da hadin kai ga rundunar ta hanyar samar da sahihin bayanai a kan lokaci domin daukar matakin gaggawa kan masu aikata muggan laifuka,” In ji Sadiq
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota
Aƙalla ɗalibai takwas na Jami’ar Jos ne aka ruwaito sun mutu, yayin da wasu uku suka samu munanan raunuka, a wani mummunan hatsarin da ya rutsa da wata tirela da wata motar bas.
Hatsarin ya faru ne a hanyar Zariya, cikin ƙaramar hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.
NAFDAC ta lalata kayayyakin Naira biliyan 5 a Jihar Nasarawa Zanga-zanga ta ɓarke bayan haɗarin tirela ta kashe mutum a YobeLamarin ya faru ne da misalin ƙarfe biyu na tsakar daren ranar Alhamis lokacin da ɗaliban ke dawowa daga wani biki.
Jami’in kula da wayar da kan jama’a na hukumar kiyaye haɗɗura ta ƙasa (FRSC) Peter Yakubu Longsan ne ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa motar bas ɗin na ɗauke da ɗalibai 11 na Jami’ar.
A cewar Hukumar ta FRSC, shaidun gani da ido sun danganta hatsarin da tsananin gudu na direban motar yake yi na wuce gona da iri.
Da yake bayar da cikakken bayani kan lamarin, Longsan ya bayyana cewa, “A yau 11 ga Disamba, 2025, Hukumar FRSC reshen Jihar Filato ta samu kiran waya da misalin ƙarfe 02:30 na tsakar dare, inda aka ba da rahoton wani haɗarin mota da ya afku a kusa da hanyar Zariya wajen Unity Bank, a Jos.
“Hatsarin ya haɗa da motoci biyu, tirela da bas, mutum 11 ne a cikin motar kuma an ce ɗaliban jami’ar Jos ne. Da faruwar lamarin ne mutum bakwai ake zargin nan take sun mutu, domin daga ƙarshe likita ya tabbatar da cewa sun mutu, sai kuma wani da ya mutu a asibitin wanda ya kawo adadin waɗanda suka mutu zuwa takwas.
“A yanzu haka wasu uku suna karɓar magani a asibitin, dukkan waɗanda abin ya rutsa da su maza ne, kamar yadda wani ganau ya shaida cewar motar bas ɗin na cikin tsananin gudu, lamarin da ya kai ga rasa natsuwa daga bisani kuma lamarin ya faru. A halin yanzu dai ana ci gaba da gudanar da cikakken bincike,” in ji shi.