Gwamna Buni Ya Naɗa Matasa 200 A Matsayin Hadimansa
Published: 12th, March 2025 GMT
Sabbin hadiman da aka naɗa za su fara aiki nan take, tare da kawo sabbin dabaru domin inganta sadarwa a gwamnatin jihar.
Wannan shiri kuma na ɗaya daga cikin ƙoƙarin gwamnatin na ƙarfafawa matasa guiwa da rage rashin aikin yi a jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda matsalar tsaro a Najeriya
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya dakatar da tafiyarsa zuwa Birnin Johannesburg na Afrika ta Kudu, da Luanda na Angola, sakamakon sace ɗalibai a Jihar Kebbi da kuma harin da aka kai wa masu ibada a wata coci da ke yankin Eruku a Jihar Kwara.
Tinubu, shirya barin Abuja a ranar Laraba domin halartar taron G20 karo na 20 da kuma Taron AU-EU karo na bakwai.
Sanatan Enugu ya mutu a Birtaniya ‘Yadda aka harbe mijina a gabana lokacin sace daliban Kebbi’Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Laraba.
“Shugaban ƙasa ya umarci sojoji da ’yan sanda da su aike ƙarin jami’ai zuwa waɗannan yankuna domin a tabbatar an bi diddigin ’yan bindigar da suka kai wa masu ibada hari.”
Shugaban ya ɗage tafiyar domin samun ƙarin bayanan tsaro da ɗaukar matakan gaggawa.
Bayan neman agaji da Gwamnan Jihar Kwara ya yi, Shugaba Tinubu ya umurci jami’an tsaro da su tura ƙarin dakaru da ’yan sanda zuwa Eruku da dukkanin yankin Ƙaramar Hukumar Ekiti domin inganta tsaro.
Idan ba a manta ba ’yan bindiga sun kai wa masu ibada hari a Cocin Christ Apostolic Church a ranar Litinin.
Shugaba Tinubu na jiran cikakken rahoto daga Mataimakinsa Kashim Shettima, wanda ya kai wa al’ummar Jihar Kebbi ziyarar jaje kan sace ɗalibai mata da wasu mahara suka yi.
Hakazalika, yana jiran rahotan ’yan sanda da Hukumar DSS game da harin da aka kai a Jihar Kwara.
Onanuga, ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa ya damu matuƙa kan sace ɗaliban da aka yi a Jihar Kebbi.
“Shugaba Tinubu ya bayyana a fili cewa dole ne a yi duk mai yiwuwa domin ceto ɗalibai 24 da aka sace tare da dawo da su gida lafiya,” in ji shi.
Fadar Shugaban Ƙasa ta ce kiyaye rayukan ’yan Najeriya shi ne babban abin da shugaban ƙasa ya fi mayar da hankali a kai.
A cewar fadar wannan ne dalilin da ya sa ya ɗage tafiyarsa don mayar da hankali kan inganta tsaro a yankunan da abin ya shafa.