’Yan sanda sun ceto mutum 30 daga hannun ’yan bindiga a Katsina
Published: 12th, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina, ta daƙile wani harin ’yan bindiga tare da ceto mutum 30 da aka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Faskari.
A wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ƙauyen Unguwar Sarkin Fulani da ke yankin.
“Da misalin ƙarfe 1 na dare, muka samu rahoto cewa wasu ’yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun kai hari ƙauyen Unguwar Sarkin Fulani inda suka sace mutum 30,” in ji sanarwar.
Bayan samun rahoton, jami’an tsaro sun kai ɗauki, inda suka yi wa maharan kwanton ɓauna, sannan suka yi musayar wuta da su.
DSP Sadiq, ya ce babu wanda ya ji rauni daga cikin waɗanda aka kuɓutar, kuma jami’an tsaro sun samu nasarar dawo da wasu dabbobin da maharan suka sace.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa hari musayar wuta
এছাড়াও পড়ুন:
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe
Ya ci gaba da cewa, “an kama masu laifuka da dama ta hanyar bayanai da muke bai wa jami’an tsaro wanda hakan ya taimaka sosai wajen magance aikata laifuka a POS”, domin a cewarsa “sun sanya tsauraran matakai yadda ko da an tura kudi kafin a zo karɓa mambobinmu suna ganewa idan an tura kudin ta hanyar da ya dace, idan ba su gamsu ba sai a sanar da jami’an tsaro a zo a kama mutum, an kama wasu a Abuja, an kama wasu a Maiduguri da wasu sassa na kasar nan”.
Ya bayyana kungiyar a matsayin mai farin jini, inda ya ce dukkan jami’an Nijeriya sun santa kuma sun yi marhaban da ita ta hanyar kai musu ziyara gami da samun goyon bayansu.
Ya ce ba ma a nan kasar ba har da wasu kasashen waje idan akwai wata matsala da shafi wannan bangare, jami’an tsaron kasar su kan tuntube su. A fannin inganta kanana da matsakaitan sana’o’i kuwa, ya ce kungiyar na yin duk mai yiwuwa wajen ganin mambobinta sun ci gajiyar shirin da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA