’Yan sanda sun ceto mutum 30 daga hannun ’yan bindiga a Katsina
Published: 12th, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Katsina, ta daƙile wani harin ’yan bindiga tare da ceto mutum 30 da aka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Faskari.
A wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ƙauyen Unguwar Sarkin Fulani da ke yankin.
“Da misalin ƙarfe 1 na dare, muka samu rahoto cewa wasu ’yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun kai hari ƙauyen Unguwar Sarkin Fulani inda suka sace mutum 30,” in ji sanarwar.
Bayan samun rahoton, jami’an tsaro sun kai ɗauki, inda suka yi wa maharan kwanton ɓauna, sannan suka yi musayar wuta da su.
DSP Sadiq, ya ce babu wanda ya ji rauni daga cikin waɗanda aka kuɓutar, kuma jami’an tsaro sun samu nasarar dawo da wasu dabbobin da maharan suka sace.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Garkuwa hari musayar wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Cutar Diphtheria ta yi ajalin ƙananan yara 3 a Zariya
Kananan yara uku sun rasu yayin da wasu da shidan ke kwance a asibiti sakamakon sake bullar cutar nan ta mashako a garin Zariya da ke Jihar Kaduna.
Wani mazaunin unguwar Kwarbai a yankin na Zariya, Mallam Bashir Magaji wanda ya rasa ’yarsa sakamakon barkewar cutar wadda a turance ake kira Diphtheria, ya bayyana yadda take bazuwa cikin sauri a kwanakin nan.
Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi Amurka za ta ɗauki nauyin ’yan tawaye domin yaƙi da ta’addanciA cewarsa, ’yarsa da ta nuna alamun kamuwa da cutar na kumburin wuya da sarkewar numfashi, an gaggauta mika ta Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika, amma daga bisani ta ce ga garinku nan.
Mallam Bashir ya bayyana cewa, tun bayar rasuwar ’yarsa, a yanzu haka an samu wasu karin yaran uku da suka soma nuna alamun kamuwa da cutar kamar dai yadda ta kasance ga ’yarsa.
Sai dai ya ce ya gaggauta kai rahoton lamarin ga wasu muhukuntan lafiya mafi kusa wadanda suka turo tawagar jamiai da ta soma bayar da allurar riga kafi a yankin.
“Na samu labarin cewa alamun cutar sun bayyana a jikin wasu yaran makwabcina biyu da wata mata a layin da nake zama.”
Ya kara da cewa an kwantar da wasu yaran hudu da su ma suka nuna alamun cutar a wata cibiyar lafiya ta Kakaki da ke kusa da Kwarbai, kuma tuni har an sallami yaro daya.
Ya kuma bayyana damuwa kan zargin cewa babu allurar rigakafin cutar a duk fadin Jihar Kaduna, “wadda na samu labarin cewa sai daga Jihar Neja aka kawo mana ita.”
Aminiya ta yi kokarin jin ta bakin sakatariyar lafiya ta Karamar Hukumar Zariya, amma ba ta amsa kiran da wakilinmu ya yi mata ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.