Najeriya ta yi hasashen samun karuwar kashi 4.6 cikin dari na GDP a 2025
Published: 12th, March 2025 GMT
Gwamnatin Najeriya a ranar Talata ta bayyana fatanta na ganin tattalin arzikin kasar zai karu da a kalla kashi 4.6 cikin dari a shekarar 2025, daga kashi 3.19 a shekarar 2024.
Da yake kaddamar da wani cikakken tsarin tattalin arziki na samun ci gaba mai dorewa a babban birnin tarayyar Abuja, ministan kudi kuma mai kula da harkokin tattalin arzikin kasar, Wale Edun, ya ce har yanzu daidaita sassan tattalin arzikin kasa shi ne abin da aka fi sa a gaba, tare da samun daidaito a darajar musayar kudi, da rarar cinikayya, da karuwar samar da man fetur da ke sanya kasar a matsayin kasa mai karfi a duniya.
A sa’i daya kuma, hukumar kididdiga ta kasa a baya ta bayar da rahoton cewa, jimillar darajar kayayyakin cikin gida wato (GDP) ya karu da kashi 3.84 cikin dari a rubu’i na hudu na shekarar 2024, idan aka kwatanta da makamancin lokaci a 2023, inda jimillar ta karu daga kashi 3.46 a rubu’i na baya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Barau FC ta doke Enugu Rangers a Firimiyar Najeriya
Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta doke Enugu Rangers da ci 2-0 a wasan mako na 13 na Firimiyar Najeriya da suka buga a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mata a Jihar Kano.
Umar Bala Mohammed ne ya fara zura ƙwallo ta farko a minti na 25, kafin Joseph Kemin ya ƙara ta biyu a minti na 72 bayan dawowa daga hutun rabin lokaci.
HOTUNA: Fada ya barke a Hedikwatar Jam’iyyar PDP ’Yan bindiga sun sako mutane 45 bayan sulhu a KatsinaWannan nasarar ce ta uku da Barau FC ta yi cikin wasanni 12 da ta buga a kakar bana, inda ta yi kunnen doki a wasanni huɗu, aka kuma doke ta a biyar.
Yanzu haka Barau FC ta hau mataki na 16 a teburin gasar da maki 13, yayin da Enugu Rangers kuwa ta koma mataki na 14.
A gobe Laraba, Barau FC za ta kece raini da Rivers United a kwantan wasan mako na biyar da za a buga a filin wasa na Sani Abacha.
A wani kwantan wasan mako na biyar, Kano Pillars za ta yi tattaki zuwa filin wasa na Remo Stars domin ɓarje gumi.