Najeriya ta yi hasashen samun karuwar kashi 4.6 cikin dari na GDP a 2025
Published: 12th, March 2025 GMT
Gwamnatin Najeriya a ranar Talata ta bayyana fatanta na ganin tattalin arzikin kasar zai karu da a kalla kashi 4.6 cikin dari a shekarar 2025, daga kashi 3.19 a shekarar 2024.
Da yake kaddamar da wani cikakken tsarin tattalin arziki na samun ci gaba mai dorewa a babban birnin tarayyar Abuja, ministan kudi kuma mai kula da harkokin tattalin arzikin kasar, Wale Edun, ya ce har yanzu daidaita sassan tattalin arzikin kasa shi ne abin da aka fi sa a gaba, tare da samun daidaito a darajar musayar kudi, da rarar cinikayya, da karuwar samar da man fetur da ke sanya kasar a matsayin kasa mai karfi a duniya.
A sa’i daya kuma, hukumar kididdiga ta kasa a baya ta bayar da rahoton cewa, jimillar darajar kayayyakin cikin gida wato (GDP) ya karu da kashi 3.84 cikin dari a rubu’i na hudu na shekarar 2024, idan aka kwatanta da makamancin lokaci a 2023, inda jimillar ta karu daga kashi 3.46 a rubu’i na baya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
China ta yi martani kan barazanar Trump ta kai hari Najeriya
Ƙasar China ta soki abin da ta kira yunƙurin Shugaban Amurka Donald Trump na yin katsalandan cikin harkokin cikin gida na Najeriya, inda ta bayyana cikakken goyon bayanta ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar, Mao Ning, ce ta bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Talata, a matsayin martani kan barazanar Shugaba Trump ta tura sojojin Amurka zuwa Najeriya domin yaƙi da abin da ya kira kisan kiyashi ga Kiristoci.
Tsohon Mataimakin Shugaban Amurka Dick Cheney ya mutu An kama barawo da wayoyin sata 17 a taron sauya shekar Gwamnan BayelsaTrump, wanda ya yi ikirarin cewa ana kisan Kiristoci a Najeriya, ya zargi gwamnatin Shugaba Tinubu da yin biris da zarge-zargen, yana mai cewa Amurka za ta iya ɗaukar mataki, ciki har da kai hare-hare ta sama ko ta ƙasa.
Sai dai gwamnatin Najeriya ta musanta zargin, tana mai cewa irin wannan kalami ba ya nuna haƙiƙanin halin da ake ciki a ƙasar.
A martaninta, Mao Ning ta ce, “China tana da kyakkyawar alaƙa da Najeriya, kuma muna bai wa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu cikakken goyon baya wajen gudanar da mulki bisa tsarin da ya dace da yanayin ƙasarsu.”
A cewarta, China ba ta goyon bayan ƙasashen da ke amfani da addini ko batun haƙƙin ɗan Adam a matsayin hujjar yin katsalandan cikin harkokin wasu ƙasashe masu cikakken ‘yanci.
“Ina mai jaddada cewa China tana adawa da duk wani yunƙuri na barazana, takunkumi ko amfani da ƙarfin soja wajen tsoma baki cikin harkokin cikin gida na wata ƙasa,” in ji Mao Ning.