Ukraniya Ta Hai Wa Birnin Moscow Hari Da Jirage Marasa Matuki
Published: 11th, March 2025 GMT
Tare da cewa Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuki fiye da 60 da Ukiraniya ta harba, sai dai an sanar da mutuwar mutum daya a birnin Moscow.
Kantoman yankin Moscow Andrey Vorobyov ne ya sanar da cewa mutum daya ya rasa ransa yayin da wasu 3 su ka jikkata, sanadiyyar hare-haren da Ukiraniya ta kai wa birnin da makamai masu linzami masu yawa da safiyar yau Talata.
Kantoman Mascow ya rubuta a shafinsa na “Telegram’ cewa; “ ya zuwa yanzu an sami labarin mutuwar mutum guda da kuma jikkata wasu 3 a garin Fidnoveh a kudancin Moscow.”
Sai dai daga baya wasu kafafen watsa labarun Rasha sun ambaci cewa adadin wadanda su ka jikkata din ya karu zuwa 5.
Haka nan kuma Andrey Vorobyov ya kara da cewa; Wasu gidaje bakwai sun illata saboda faduwar jirgin maras matuku a kansu.
A garin Domodedovo kuwa an sanar da tashin gobara sanadiyyar faduwar jirgi maras matuki da Ukiraniya ta harba, kuma wasu baraguzan jirgin da su ka fadi a kusa da tashar jirgin kasa ya yi barna sai dai ba mai girma ba. Tuni aka dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa a yankin.
Kantoman birnin Moscow ya kuma sanar da cewa, sojoji sun yi nasarar kakkabo jiragen sama marasa mutuki 73 da ukiraniya ta harba wa birnin.
Saboda wadannan hare-haren an dakatar da tashi da saukar jiragen saman a cikin filayen sama fiye da uku da suke kusa da Moscow.
A ranar Lahadin da ta gabata ma dai sojojin Rasha sun sanar da kakkabo fiye da jirage marasa matuki 88 a saman yankunan kasar mabanbanta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
An shiga yanayin zaman dar-dar a yankin Gabas ta Tsakiya bayan wasu munana hare-hare da Isra’ila ta kaddamar a kan tashoshin Nukiliya da manyan sojojin Iran a ranar Alhamis.
Hukumomin Isra’ila dai sun tabbatar da kai harin inda suka ce ya kunshi daruruwan jirage kan abin da suka kira da kololuwar wurin hada makaman Nukiliya na Iran da kuma manyan sojojinta.
NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a KadunaDaga cikin manyan mutanen da ake zargin harin ya hallaka har da Manjo-Janar Hossein Salami, Shugaban Rundunar IRGC ta Iran da wasu manyan kwamandoji da manyan masana a tashar Nukiliyar.
Rundunar Tsaron Isra’ila (IDF) ta sanar da cewa jiragen yaki sama da 200 ne suka yi aikin kai hare-haren kuma sun kai su ne a muhimman wurare sama da 100 a Iran.
Sai dai jim kadan bayan labarin kai harin, Iran ta mayar da martani.
Kafofin yada labaran gwamnatin kasar sun rawaito cewa Iran ta harba jirage marasa matuka sama da 100 da suke hakon wurare daban-daban a cikin Isra’ila.
Kazalika, Shugaban addini na kasar, Ayatollah Ali Khomenei ya sha alwashin sai Isra’ila ta dandana kudarta.
Tuni rahotanni daga Isra’ila suka nuna yadda mutane suka shiga sayayya a kasuwanni ba ji ba gani suna adanawa saboda gudun abin da zai faru na martani.
Wasu hotuna da kamfanin dillancin labaran Faransa (AFP) ya wallafa sun nuna tituna a biranen Tel Aviv da Kudus sun dade.
Lamarin dai ya sa an soke tashi da saukar jirage zuwa kasashe da dama na yankin na Gabas ta Tsakiya.