Ukraniya Ta Hai Wa Birnin Moscow Hari Da Jirage Marasa Matuki
Published: 11th, March 2025 GMT
Tare da cewa Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuki fiye da 60 da Ukiraniya ta harba, sai dai an sanar da mutuwar mutum daya a birnin Moscow.
Kantoman yankin Moscow Andrey Vorobyov ne ya sanar da cewa mutum daya ya rasa ransa yayin da wasu 3 su ka jikkata, sanadiyyar hare-haren da Ukiraniya ta kai wa birnin da makamai masu linzami masu yawa da safiyar yau Talata.
Kantoman Mascow ya rubuta a shafinsa na “Telegram’ cewa; “ ya zuwa yanzu an sami labarin mutuwar mutum guda da kuma jikkata wasu 3 a garin Fidnoveh a kudancin Moscow.”
Sai dai daga baya wasu kafafen watsa labarun Rasha sun ambaci cewa adadin wadanda su ka jikkata din ya karu zuwa 5.
Haka nan kuma Andrey Vorobyov ya kara da cewa; Wasu gidaje bakwai sun illata saboda faduwar jirgin maras matuku a kansu.
A garin Domodedovo kuwa an sanar da tashin gobara sanadiyyar faduwar jirgi maras matuki da Ukiraniya ta harba, kuma wasu baraguzan jirgin da su ka fadi a kusa da tashar jirgin kasa ya yi barna sai dai ba mai girma ba. Tuni aka dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa a yankin.
Kantoman birnin Moscow ya kuma sanar da cewa, sojoji sun yi nasarar kakkabo jiragen sama marasa mutuki 73 da ukiraniya ta harba wa birnin.
Saboda wadannan hare-haren an dakatar da tashi da saukar jiragen saman a cikin filayen sama fiye da uku da suke kusa da Moscow.
A ranar Lahadin da ta gabata ma dai sojojin Rasha sun sanar da kakkabo fiye da jirage marasa matuki 88 a saman yankunan kasar mabanbanta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
UNDP : An ruguza fiye da kashi 80 cikin 100 na gine-ginen Gaza
Hukumar ci gaban kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya (UNDP) ta fitar da wani rahoto dake cewa an ruguza fiye da kashi 80 cikin 100 na gine-ginen zirin Gaza.
UNDP ta ce, a Gaza kadai an lalata fiye kashi 92 cikin 100 na gine-ginen birnin.
Kakakin hukumar ya bayyana rugujewar gine-ginen da ”mummuna”,inda ta kiyasta cewa akwai akalla tan miliyan 55 na baraguzai da ke bukatar sharewa a yankin.
UNDP ta ce tuni ta fara aikin share baraguzan yankin, amma barazanar abubuwan fashewa da aka binne na kawo musu cikas a aikin.
Hukumar ta kara da cewa akwai gawarwakin mutane da ake ta tonowa yayin aikin.
Majalisar Dinkin Duniya da Bankin Duniya da kungiyar Tarayyar Turai sun kiyasta bukatar dala biliyan 70 domin sake gina Gaza.
shugaban kasar Turkiyya, Recep Tayyib Erdogan dake cikin shugabannin da suka ratabba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a Gaza ya ce ya yi imanin cewa za a samar da kudin sake gina Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Araghchi : Trump bai cancanci mai samar da zaman lafiya ba yayin da yake haifar da yake-yake October 14, 2025 Sojojin Madagaska sun karbe mulkin kasar October 14, 2025 Trump ya ce zai yi shawara game da batun kafa kasar Falasdinu October 14, 2025 Islamic Jihad : jarumtakar ‘yan gwagwarmaya ce ta haifar da sako fursunonin falasdinawa October 14, 2025 Aragchi Yana Uganda Don Halattan Taron Ministocin Kungiyar NAM October 14, 2025 Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata October 14, 2025 Ma’aikatar Harkokin wajen Kasar Iran Ta Yi Tir Da Jawabin Trump A Knesset Ta HKI October 14, 2025 An Gudanar Gagarumar Zanga Zangar Goyon Bayan Falasdinawa A Australia Da Indonasia October 14, 2025 Syria: Busaina Sha’aban Ta Karyata Labaran Da Aka Danganta Ma Ta Na Ganawa Da Jami’an Iraniyawa October 14, 2025 Mahalarta Taron ‘Sherm-Sheikh” Sun Rattaba Hannu Akan Yarjejeniyar Zaman Lafiya October 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci