Ukraniya Ta Hai Wa Birnin Moscow Hari Da Jirage Marasa Matuki
Published: 11th, March 2025 GMT
Tare da cewa Rasha ta sanar da kakkabo jiragen sama marasa matuki fiye da 60 da Ukiraniya ta harba, sai dai an sanar da mutuwar mutum daya a birnin Moscow.
Kantoman yankin Moscow Andrey Vorobyov ne ya sanar da cewa mutum daya ya rasa ransa yayin da wasu 3 su ka jikkata, sanadiyyar hare-haren da Ukiraniya ta kai wa birnin da makamai masu linzami masu yawa da safiyar yau Talata.
Kantoman Mascow ya rubuta a shafinsa na “Telegram’ cewa; “ ya zuwa yanzu an sami labarin mutuwar mutum guda da kuma jikkata wasu 3 a garin Fidnoveh a kudancin Moscow.”
Sai dai daga baya wasu kafafen watsa labarun Rasha sun ambaci cewa adadin wadanda su ka jikkata din ya karu zuwa 5.
Haka nan kuma Andrey Vorobyov ya kara da cewa; Wasu gidaje bakwai sun illata saboda faduwar jirgin maras matuku a kansu.
A garin Domodedovo kuwa an sanar da tashin gobara sanadiyyar faduwar jirgi maras matuki da Ukiraniya ta harba, kuma wasu baraguzan jirgin da su ka fadi a kusa da tashar jirgin kasa ya yi barna sai dai ba mai girma ba. Tuni aka dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa a yankin.
Kantoman birnin Moscow ya kuma sanar da cewa, sojoji sun yi nasarar kakkabo jiragen sama marasa mutuki 73 da ukiraniya ta harba wa birnin.
Saboda wadannan hare-haren an dakatar da tashi da saukar jiragen saman a cikin filayen sama fiye da uku da suke kusa da Moscow.
A ranar Lahadin da ta gabata ma dai sojojin Rasha sun sanar da kakkabo fiye da jirage marasa matuki 88 a saman yankunan kasar mabanbanta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu
Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta amince da wasu sauye-sauye da nufin rage tsadar tafiye-tafiyen jiragen sama a tsakanin kasashe mambobin kungiyar.
A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba, Hukumar ECOWAS ta sanar da cewa shugabannin kasashe da gwamnatoci, a taronsu a Abuja, sun amince da wata manufa ta kawar da harajin sufurin jiragen sama da kuma rage kudin tikitan jirgin sama da kashi 25 cikin 100, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Janairu, 2026.
Hukumar ta bayyana cewa wannan matakin ya biyo bayan shekaru da dama na koma baya a fannin sufurin jiragen sama a Yammacin Afirka, galibi saboda yawan haraji, wanda ke hana bukatar tafiye-tafiye da kuma raunana jarin da ake zubawa a fannin tafiye tafiye na jiragen sama.
Nazarin da ECOWAS da Tarayyar Afirka, da Kungiyar Jiragen Sama ta Afirka (AFRAA), da Kungiyar Sufurin Jiragen Sama ta Duniya (IATA) suka gudanar sun nuna cewa Yammacin Afirka ya kasance daya daga cikin yankuna mafi tsada don tafiye-tafiyen jiragen sama, inda fasinjoji wani lokacin ke biyan har zuwa caji 66 daban-daban, yayin da kamfanonin jiragen sama ke fuskantar kudade daban-daban.
ECOWAS ta yi gargadin cewa hauhawar farashin jiragen sama na hana tafiye-tafiyen fasinjoji, rage yawan yawon bude ido, kawo cikas ga ciniki, da kuma lalata ajandarta ta ‘yancin zirga-zirga da hadewar yankuna.
A cewar sanarwar, amincewa da Dokar na da nufin magance wadannan kalubalen da kuma daidaita yankin da ka’idojin jiragen sama na duniya.
Kungiyar ta jaddada cewa ya kamata wadannan gyare-gyare su taimaka wajen rage farashin tikiti, kara yawan fasinjoji, karfafa kamfanonin jiragen sama na yankin, bunkasa ayyukan filayen jiragen sama da kuma samar da karin damammaki na tattalin arziki ga al’ummomin da ke karbar bakuncin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Reuters: Amurka na matsa lamba kan kotun ICC don janye bincike kan yakin Gaza da Afghanistan December 11, 2025 Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci