MDD, ta la’anci Isra’ila kan katse wutar lantarki a Gaza
Published: 11th, March 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya, ta yi tir da matakin Isra’ila na kate wutar lantarki a Gaza, tana mai matukar gargadi game da ilan da hakan zai janyo wa Zirin.
Matakin da Isra’ila ta dauka na katse wutar lantarki a zirin Gaza da aka yi wa kawanya zai hana yankin Falasdinawa samun “ruwa mai tsafta,” in ji wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan yankunan Falasdinawa da aka mamaye.
Francesca Albanese ta fada a ranar Litinin cewa shawarar da Isra’ila ta dauka na yanke wuta a Gaza na nufin tsaida hanyoyin samar da ruwa a zirin.
Albanese ta kuma yi Allah wadai da rashin daukar mataki kan hakan daga kasashen duniya.
A ranar Lahadin da ta gabata ne, kafofin yada labaran Isra’ila suka mabato cewa ministan makamashi da ababen more rayuwa na gwamnatin Isra’ila Eli Cohen ya umarci Kamfanin Lantarki na Isra’ila da ya katse wutar lantarki zuwa Gaza “nan take.”
Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023 bayan harin ba zata na kungiyar Hamas, kuma tun lokacin ta kashe Falasdinawa sama da 48,400, baya ga lalata duk wasu cibiyoyi masu mahimmanci na Zirin kama daga asibitoci, sansanonin ‘yan gudun hijira, makarantu gidajen jama’a da dai saurensu tare da goyan bayan Amurka, lamarin da gwamnatocin kasashen duniya dama suka danganta da yunkurin share wata al’umma daga doron kasa.
Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta fitar a bara da sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, da tsohon ministan tsaron kasar Yoav Galant, bisa zarginsu da aikata laifukan yaki a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky
Shugaban mabiya Shi’a a Najeriya, Sheikh Ibraheem El-Zakzaky, ya ce zai yi hisabi da tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, a gaban Allah kan abin da ya faru a Zariya a 2015.
Rikicin ya fara ne bayan da mambobin IMN sun tare wa tsohon Hafsan Soji, Tukur Buratai, hanya.
Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025 Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a AdamawaLamarin fara a matsayin ƙaramin rikici daga baya ya rikiɗe zuwa babban al’amari, lamarin da ya sanya sojoji buɗe wa mabiyan wuta.
Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam da kwamitin bincike na jihar, sun bayyana cewa an kashe tare binne ɗaruruwan mambobin IMN a asirce bayan faruwar lamarin.
Daga baya an kama Zakzaky da matarsa, an tsare su har zuwa 2021, kafin daga baya kotu ta wanke su.
Bayan cikar lamarin da shekara 10, Zakzaky ya ce gwamnati ta kasa ɗaukar alhakin abin da ya faru.
Ya ce: “Babu abin da aka yi. Ba su yadda cewa wani abu ya faru ba, duk da cewa kwamitin bincike ya miƙa rahotonsa tun 2016.”
Zakzaky, ya kuma zargi gwamnatin yanzu da yin shiru a kan lamarin, duk da alƙawarin da ta yi na duba rahoton da kuma biya iyalan waɗanda abin ya shafa diyya.
Ya ce: “Sun tabbatar mana cewa za su magance batun, amma tun daga lokacin shiru kake ji.”
Da aka tambaye shi ko ya yafe wa Buhari, Zakzaky, ya ce ya bar komai a hannun Allah, kuma zai masa hisabi da shi ranar gobe ƙiyama.
Zakzaky ya ce: “Game da Buhari, za mu gana a Ranar Alƙiyama. Lissafin Buhari ya ƙare.”
Ya ƙara da cewa harin bai yi nasarar daƙile IMN ba, sai ma ƙara ɗaukaka sunan ƙungiyar inda ta yi fice a duniya.
Zakzaky, ya ce sun kai ƙarar lamarin kotun ƙasa da ƙasa, sannan ƙofarsu a buɗe ta ke domin tattaunawa da gwamnati.
Ya ce: “Ko ba sa son ganinmu, za su gan mu. Ko ba sa son jinmu, za su ji mu.”