HausaTv:
2025-07-13@07:08:16 GMT

MDD, ta la’anci Isra’ila kan katse wutar lantarki a Gaza

Published: 11th, March 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya, ta yi tir da matakin Isra’ila na kate wutar lantarki a Gaza, tana mai matukar gargadi game da ilan da hakan zai janyo wa Zirin.

Matakin da Isra’ila ta dauka na katse wutar lantarki a zirin Gaza da aka yi wa kawanya zai hana yankin Falasdinawa samun “ruwa mai tsafta,” in ji wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan yankunan Falasdinawa da aka mamaye.

Francesca Albanese ta fada a ranar Litinin cewa shawarar da Isra’ila ta dauka na yanke wuta a Gaza na nufin tsaida hanyoyin samar da ruwa a zirin.

Albanese ta kuma yi Allah wadai da rashin daukar mataki kan hakan daga kasashen duniya.

A ranar Lahadin da ta gabata ne, kafofin yada labaran Isra’ila suka mabato cewa ministan makamashi da ababen more rayuwa na gwamnatin Isra’ila Eli Cohen ya umarci Kamfanin Lantarki na Isra’ila da ya katse wutar lantarki zuwa Gaza “nan take.”

Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023 bayan harin ba zata na kungiyar Hamas, kuma tun lokacin ta kashe Falasdinawa sama da 48,400, baya ga lalata duk wasu cibiyoyi masu mahimmanci na Zirin kama daga asibitoci, sansanonin ‘yan gudun hijira, makarantu gidajen jama’a da dai saurensu tare da goyan bayan Amurka, lamarin da gwamnatocin kasashen duniya dama suka danganta da yunkurin share wata al’umma daga doron kasa.

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta fitar a bara da sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, da tsohon ministan tsaron kasar Yoav Galant, bisa zarginsu da aikata laifukan yaki a Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI

Majalisar limaman musulmin nahiyar turai ta fitar da wani bayani da ta nesanta kanta daga wasu mutane da su ka kai ziyarar HKI tare da bayyana kansu a matsayin limamai daga kasashen turai, tana mai cewa, ko kadan ba su wakiltar al’ummar musulmin da suke cikin nahiyar ta turai.

A ranar Litinin din da ta gabata ne dai ofishin shugaban HKI Ishaq Herzog ya fitar da bayani da a ciki yake cewa; A ofis dinsa dake birnin Kudus ya karbi bakuncin limaman musulmi daga kasashen Faransa,Belgium, Holland, Italia da kuma Birtyaniya.”.

Ofishin majalisar limaman musulmin na turai, mai  matsugunni  a Faransa ya bayyana ziyarar mutanen zuwa Isra’ila da cewa, tana da daure kai, haka nan kuma lokacin da aka yi ta.”

Majalisar ta limaman turai din ta yi kira ga dukkanin ‘yantattu a duniya da su kasance a tare da al’ummar Falasdinu da ake zalunta, domin ganin an kawo karshen kisan kiyashin da sojojin mamaya suke yi musu.

Bugu da kari majalisar ta ce, wannan ziyarar tana nuni da yadda wadanda su ka yi ta ba su da lamiri na ‘yan’adamtaka da rashin riko da mafi karancin koyarwar musulunci ta yin kira da a taimaki gaskiya.”

Majalisar limaman na Turai ta kuma kara da cewa; ziyarar wani kokari ne na wanke ‘yan mamaya, kuma cin amanar Allah da manzon Allah ne da jinanen raunana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a sa zare tsakanin Amurka da Turai kan harajin kasuwanci
  • Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra\ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa A Zirin Gaza
  • NYT: Natanyahu Yana Tsawaita Yaki A Gaza Don Ci Gaba Da Kasancewa Kan Iko A HKI
  •   Fiye Da Falasdinawa 60 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i Kadan
  • “Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
  • HKI Ta Roki Amurka Ta Taimake Ta A Fada Da Kasar Yemen
  • An Kashe Jami’in Sojan HKI A Gaza
  • Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya
  • Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza