HausaTv:
2025-11-04@21:18:28 GMT

MDD, ta la’anci Isra’ila kan katse wutar lantarki a Gaza

Published: 11th, March 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya, ta yi tir da matakin Isra’ila na kate wutar lantarki a Gaza, tana mai matukar gargadi game da ilan da hakan zai janyo wa Zirin.

Matakin da Isra’ila ta dauka na katse wutar lantarki a zirin Gaza da aka yi wa kawanya zai hana yankin Falasdinawa samun “ruwa mai tsafta,” in ji wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan yankunan Falasdinawa da aka mamaye.

Francesca Albanese ta fada a ranar Litinin cewa shawarar da Isra’ila ta dauka na yanke wuta a Gaza na nufin tsaida hanyoyin samar da ruwa a zirin.

Albanese ta kuma yi Allah wadai da rashin daukar mataki kan hakan daga kasashen duniya.

A ranar Lahadin da ta gabata ne, kafofin yada labaran Isra’ila suka mabato cewa ministan makamashi da ababen more rayuwa na gwamnatin Isra’ila Eli Cohen ya umarci Kamfanin Lantarki na Isra’ila da ya katse wutar lantarki zuwa Gaza “nan take.”

Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023 bayan harin ba zata na kungiyar Hamas, kuma tun lokacin ta kashe Falasdinawa sama da 48,400, baya ga lalata duk wasu cibiyoyi masu mahimmanci na Zirin kama daga asibitoci, sansanonin ‘yan gudun hijira, makarantu gidajen jama’a da dai saurensu tare da goyan bayan Amurka, lamarin da gwamnatocin kasashen duniya dama suka danganta da yunkurin share wata al’umma daga doron kasa.

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta fitar a bara da sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, da tsohon ministan tsaron kasar Yoav Galant, bisa zarginsu da aikata laifukan yaki a Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ƙasarsa na shirin ɗaukar matakan soja da ka iya haɗawa da hare-haren ƙasa da na sama a Nijeriya.

Trump ya bayyana haka ne yayin da yake tattaunawa da manema labarai, inda yake amsa tambayar yanayin yadda hare-haren za su kasance ta sama ko ta ƙasa.

NAJERIYA A YAU: Ko Kawo Dakarun Amurka Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya? Tsagin Damagum da Anyanwu sun shirya mamaye hedikwatar PDP a yau

A cewarsa, “komai na iya faruwa, abubuwa da dama za su faru. Ina nufin abubuwa masu yawa,” in ji shi kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na Reuters ya ruwaito.

Shugaban ya ƙara da cewa, “Suna kashe Kiristoci, kuma suna kashe su da yawa. Ba za mu bari hakan ta ci gaba da faruwa ba.”

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a ranar Asabar, Trump ya bayyana cewa ya umarci Ma’aikatar Tsaron Amurka ta Pentagon da ta tsara yiwuwar kai hari kan Najeriya.

Wannan na zuwa ne kwana guda bayan ya yi gargaɗin cewa Kiristoci na fuskantar kisan kiyashi a ƙasar.

Sai dai gwamnatin Najeriya ta ce tana kallon wannan batu a matsayin lamarin da za a iya warwarewa ta hanyar diflomasiyya, tana mai cewa ƙasashen biyu abokan hulɗa ne wajen yaƙi da ta’addanci.

Cikin wani saƙo da mai magana da yawun fadar gwamnatin Nijeriya Daniel Bwala ya wallafa ranar Lahadi, ya ce idan shugabannin ƙasashen biyu suka gana, akwai fatan samun mafita mai kyau.

Barazanar Trump

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Truth Social da tsakiyar daren ranar Asabar, Donald Trump ya ce Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan take idan har gwamnati ta ci gaba da nuna halin ko in kula kan kisan da ake yi wa mabiya addinin Kirista a kasar.

Hakazalika, Trump ya ce Amurka na iya kutsa wa Nijeriya da ƙarfin soji domin kakkabe ’yan ta’adda masu aikata ta’asa da sunan addinin Islama, sannan ya umurci Ma’aikatar Yaƙi ta Amurka da ta shirya domin yiwuwar kai wa Nijeriya samame.

Wannan furici na Trump na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatinsa ta saka Najeriya a jerin ƙasashen da ake yi wa Kirista kisan ƙare dangi, zargin da fadar mulki ta Abuja ta musanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau
  • Falasdinawa Biyu Sun Yi Shahada A Nablus Da Khalil
  • Komai zai iya faruwa a hare-haren da za mu kai Nijeriya — Trump
  • Isra’ila ta aikata laifuka 194 tun bayan tsagaita wuta a Gaza
  • Yadda matata ta ɓace a Abuja aka tsince ta a Sakkwato
  • Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
  • Fursunan da aka yanke wa hukuncin kisa ya tsere daga gidan yari a Yobe
  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza