HausaTv:
2025-12-13@23:41:51 GMT

MDD, ta la’anci Isra’ila kan katse wutar lantarki a Gaza

Published: 11th, March 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya, ta yi tir da matakin Isra’ila na kate wutar lantarki a Gaza, tana mai matukar gargadi game da ilan da hakan zai janyo wa Zirin.

Matakin da Isra’ila ta dauka na katse wutar lantarki a zirin Gaza da aka yi wa kawanya zai hana yankin Falasdinawa samun “ruwa mai tsafta,” in ji wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan yankunan Falasdinawa da aka mamaye.

Francesca Albanese ta fada a ranar Litinin cewa shawarar da Isra’ila ta dauka na yanke wuta a Gaza na nufin tsaida hanyoyin samar da ruwa a zirin.

Albanese ta kuma yi Allah wadai da rashin daukar mataki kan hakan daga kasashen duniya.

A ranar Lahadin da ta gabata ne, kafofin yada labaran Isra’ila suka mabato cewa ministan makamashi da ababen more rayuwa na gwamnatin Isra’ila Eli Cohen ya umarci Kamfanin Lantarki na Isra’ila da ya katse wutar lantarki zuwa Gaza “nan take.”

Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023 bayan harin ba zata na kungiyar Hamas, kuma tun lokacin ta kashe Falasdinawa sama da 48,400, baya ga lalata duk wasu cibiyoyi masu mahimmanci na Zirin kama daga asibitoci, sansanonin ‘yan gudun hijira, makarantu gidajen jama’a da dai saurensu tare da goyan bayan Amurka, lamarin da gwamnatocin kasashen duniya dama suka danganta da yunkurin share wata al’umma daga doron kasa.

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta fitar a bara da sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, da tsohon ministan tsaron kasar Yoav Galant, bisa zarginsu da aikata laifukan yaki a Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

 Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza

Ministan harkokin wajen Turkiya Hakan Faidan ne ya bayyana cewa; kasarsa za ta iya daukar nauyin wararen matsalar Falasdinu, kuma a shirye take ta aike da sojoji zuwa yankin na Gaza idan bukatar hakan ta taso.

Fidan ya fada wa kamfafen watsa labaru cewa; Tukriya a shirye take ta yi duk abinda za ta iya yi, ta kuma dauki nauyin da ya dace akan batun Falasdinu.

A can Amurka kuwa, manzon musamman na Amurka akan harkokin yammacin Asiya, Barrack ya  fada wa jaridar  “Jerrusalem Post” cewa: Kasar Turkiya tana da sojoji masu karfi, kuma tana hulda da Hamas, a dalilin hakan shigarta cikin rundunar da za a aike Gaza, zai yi amfani.”

A ranar 18 ga watan Nuwamba ne dai kwamitin tsaro na MDd ya amince da rinjaye akan wani kuduri da Amurka ta gabatar domin kawo karshen yakin Gaza. A karkashin wannan kudurin zai a kuma aike da sojojin kasa da kasa daga nan zuwa karshen 2027.

Kudurin ya kuma tanadi cewa za a kafa gwamnati a yankin na Gaza ta kwararru wacce kwamijin tsaro ne zai rika kula da tafiyar da ita.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro  Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Yi Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi AkanDoron Ruwa December 12, 2025 Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi da dama December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu   December 11, 2025 Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta Ce Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Isra’ila Ya Nuna Gazawar Tsarin Duniya Na Dakatar Da Ita.
  • MDD ta amince da wani kuduri da ke neman Isra’ila ta bada damar shigar da agaji a Gaza   
  • Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
  • Nazarin CGTN: Fahimtar Matsayin Sin Cikin Yanayin Tattalin Arzikin Duniya Na Da Muhimmanci
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  •  Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza
  • Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila