HausaTv:
2025-03-20@11:31:58 GMT

MDD, ta la’anci Isra’ila kan katse wutar lantarki a Gaza

Published: 11th, March 2025 GMT

Majalisar Dinkin Duniya, ta yi tir da matakin Isra’ila na kate wutar lantarki a Gaza, tana mai matukar gargadi game da ilan da hakan zai janyo wa Zirin.

Matakin da Isra’ila ta dauka na katse wutar lantarki a zirin Gaza da aka yi wa kawanya zai hana yankin Falasdinawa samun “ruwa mai tsafta,” in ji wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan yankunan Falasdinawa da aka mamaye.

Francesca Albanese ta fada a ranar Litinin cewa shawarar da Isra’ila ta dauka na yanke wuta a Gaza na nufin tsaida hanyoyin samar da ruwa a zirin.

Albanese ta kuma yi Allah wadai da rashin daukar mataki kan hakan daga kasashen duniya.

A ranar Lahadin da ta gabata ne, kafofin yada labaran Isra’ila suka mabato cewa ministan makamashi da ababen more rayuwa na gwamnatin Isra’ila Eli Cohen ya umarci Kamfanin Lantarki na Isra’ila da ya katse wutar lantarki zuwa Gaza “nan take.”

Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023 bayan harin ba zata na kungiyar Hamas, kuma tun lokacin ta kashe Falasdinawa sama da 48,400, baya ga lalata duk wasu cibiyoyi masu mahimmanci na Zirin kama daga asibitoci, sansanonin ‘yan gudun hijira, makarantu gidajen jama’a da dai saurensu tare da goyan bayan Amurka, lamarin da gwamnatocin kasashen duniya dama suka danganta da yunkurin share wata al’umma daga doron kasa.

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta fitar a bara da sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, da tsohon ministan tsaron kasar Yoav Galant, bisa zarginsu da aikata laifukan yaki a Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 330 Sun Mutu Yayin da Isra’ila Ta Kai Wa Gaza Sabbin Hare-hare 

Ministan Tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ce, “A daren yau mun koma yaƙi a Gaza.”

Hamas ta zargi Isra’ila da karya yarjejeniyar tsawon kusan wata biyu, tana mai cewa hakan na barazana ga lafiyar fursunonin da ke tsare a Gaza.

Amma Isra’ila ta ce Hamas ce ke ƙin sakin fursunonin tare da bijirewa yarjejeniyar sulhu.

A lokacin yarjejeniyar, an yi musayar wasu fursunonin Isra’ila da Falsɗinawa da ke tsare a gidajen yarin Isra’ila.

Sai dai har yanzu kimanin mutum 59 daga cikin fursunonin Isra’ila suna hannun Hamas, kuma ana zargin rabinsu sun mutu.

Rahotanni sun nuna cewa Amurka ta amince da harin da Isra’ila ta sake kai wa Gaza, inda ƙasashen biyu suka sha alwashin yaƙar Hamas, ‘yan tawayen Houthi na Yemen, da sauran ƙungiyoyin da suka ɗauki makamai.

Kakakin fadar White House, Karoline Leavitt, ta yi gargaɗin cewa, “Hamas da Houthi za su fuskanci sakamako mai tsanani. Duniya za ta girgiza.”

A cewar Ma’aikatar Lafiya ta Gaza, aƙalla Falasɗinawa 48,577 ne suka mutu, yayin da Ofishin Yaɗa Labarai na Gaza ya ce adadin ya haura 61,700, ciki har da waɗanda ke birne a ƙarƙashin gine-ginen da aka rushe.

Yaƙin ya fara ne bayan harin da Hamas ta kai kudancin Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoba, 2023, wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla Isra’ilawa 1,139 tare da tsare da sama da mutum 200.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin HKI Sun Kara Kisan Karin Falasdinawa 71 A Zirin Gaza
  • Kungiyar Hamas Ta Ce Falasdinawa Ba Za Su Bar Kasarsu Ba, Ko Da Son Ransu Ko Da Karfi
  • Hare-haren Isra’ila sun yi sanadin shahadar falasdinawa kusan 1,000 a cikin sa’o’I 48
  • Iran : hare-haren Isra’ila a Gaza ci gaba da kisan kare dangi ne
  • Amurka ce Kadai Ta Ki Yin Allawadai Da Killace Gaza A Tsakanin Mambobin Kwamitin Tsaro na MDD
  • Mutum 330 Sun Mutu Yayin da Isra’ila Ta Kai Wa Gaza Sabbin Hare-hare 
  • Nijar Ta Fice Daga Kungiyar Kasashen Da Ke Amfani Da Faransanci
  • Nijar Ta Fice Daga Kungiyar Kasashen Da Ke Amfani Da da Faransanci
  • Munanan Hare-hare  Sojojin HKI A Gaza Da Safiyar Yau Talata Sun Yi Sanadiyyar Shahadar Fiye Da Falasdinawa 200
  • Isra’ila ta ƙaddamar da sabon hari a Zirin Gaza