MDD, ta la’anci Isra’ila kan katse wutar lantarki a Gaza
Published: 11th, March 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya, ta yi tir da matakin Isra’ila na kate wutar lantarki a Gaza, tana mai matukar gargadi game da ilan da hakan zai janyo wa Zirin.
Matakin da Isra’ila ta dauka na katse wutar lantarki a zirin Gaza da aka yi wa kawanya zai hana yankin Falasdinawa samun “ruwa mai tsafta,” in ji wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan yankunan Falasdinawa da aka mamaye.
Francesca Albanese ta fada a ranar Litinin cewa shawarar da Isra’ila ta dauka na yanke wuta a Gaza na nufin tsaida hanyoyin samar da ruwa a zirin.
Albanese ta kuma yi Allah wadai da rashin daukar mataki kan hakan daga kasashen duniya.
A ranar Lahadin da ta gabata ne, kafofin yada labaran Isra’ila suka mabato cewa ministan makamashi da ababen more rayuwa na gwamnatin Isra’ila Eli Cohen ya umarci Kamfanin Lantarki na Isra’ila da ya katse wutar lantarki zuwa Gaza “nan take.”
Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023 bayan harin ba zata na kungiyar Hamas, kuma tun lokacin ta kashe Falasdinawa sama da 48,400, baya ga lalata duk wasu cibiyoyi masu mahimmanci na Zirin kama daga asibitoci, sansanonin ‘yan gudun hijira, makarantu gidajen jama’a da dai saurensu tare da goyan bayan Amurka, lamarin da gwamnatocin kasashen duniya dama suka danganta da yunkurin share wata al’umma daga doron kasa.
Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta fitar a bara da sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, da tsohon ministan tsaron kasar Yoav Galant, bisa zarginsu da aikata laifukan yaki a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Umarnin janye ’yan sanda daga faɗin manyan mutane na iya zama magana kawai —Shehu Sani
Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Kwamred Shehu Sani, ya ce umarnin Shugaba Tinubu na janye ’yan sanda daga gadin manyan mutane zai iya zama magana kawai babu aiki.
A daidai wannan lokaci na ƙara yawaitar rashin tsaro, Shugaba Tinubu ya ce yana sa ido sosai kan al’amuran tsaro a faɗin ƙasa tare da jajircewa wajen kare ’yan Najeriya.
A wani taro da ya yi da hukumomin tsaro a ranar Lahadi, Shugaban Ƙasa ya bayar da umarnin cewa a janye ’yan sanda da ke gadin manyan mutane.
A cewar mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, daga yanzu rundunar ’yan sanda za ta mayar da jami’anta kan ayyukan tsaro na asali.
Yau Atiku zai karɓi katin zama ɗan a Jama’iyyar ADC Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwanaUmarnin ya kuma bayyana cewa duk wani babban mutum da ke buƙatar tsaro zai nemi jami’an hukumar tsaron fararen kaya (NSCDC).
Sai dai a martaninsa a shafinsa na X, Sanata Sani ya nuna damuwa cewa wannan umarni na iya zama magana kawai ba tare da cikakken aiwatarwa ba.
Ya rubuta cewa: “Janye ’Yan Sanda daga manyan mutane ra’ayi ne mai kyau da kuma kyakkyawan tsari duba da gaggawar buƙatun tsaron ƙasa, amma zai iya farawa kuma ya ƙare a matsayin magana kawai.”
Najeriya ta sake fuskantar tashin hankali, ciki har da hare-haren Boko Haram a Borno da kuma farmakin ’yan bindiga a jihohin Kebbi, Neja, Kwara da Borno da Bauchi.