MDD, ta la’anci Isra’ila kan katse wutar lantarki a Gaza
Published: 11th, March 2025 GMT
Majalisar Dinkin Duniya, ta yi tir da matakin Isra’ila na kate wutar lantarki a Gaza, tana mai matukar gargadi game da ilan da hakan zai janyo wa Zirin.
Matakin da Isra’ila ta dauka na katse wutar lantarki a zirin Gaza da aka yi wa kawanya zai hana yankin Falasdinawa samun “ruwa mai tsafta,” in ji wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman kan yankunan Falasdinawa da aka mamaye.
Francesca Albanese ta fada a ranar Litinin cewa shawarar da Isra’ila ta dauka na yanke wuta a Gaza na nufin tsaida hanyoyin samar da ruwa a zirin.
Albanese ta kuma yi Allah wadai da rashin daukar mataki kan hakan daga kasashen duniya.
A ranar Lahadin da ta gabata ne, kafofin yada labaran Isra’ila suka mabato cewa ministan makamashi da ababen more rayuwa na gwamnatin Isra’ila Eli Cohen ya umarci Kamfanin Lantarki na Isra’ila da ya katse wutar lantarki zuwa Gaza “nan take.”
Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza tun a ranar 7 ga Oktoba, 2023 bayan harin ba zata na kungiyar Hamas, kuma tun lokacin ta kashe Falasdinawa sama da 48,400, baya ga lalata duk wasu cibiyoyi masu mahimmanci na Zirin kama daga asibitoci, sansanonin ‘yan gudun hijira, makarantu gidajen jama’a da dai saurensu tare da goyan bayan Amurka, lamarin da gwamnatocin kasashen duniya dama suka danganta da yunkurin share wata al’umma daga doron kasa.
Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta fitar a bara da sammacin kame firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, da tsohon ministan tsaron kasar Yoav Galant, bisa zarginsu da aikata laifukan yaki a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Harin Isra’ila ya kashe mutum 3 a kudancin Lebanon
Sojojin Isra’ila sun kashe akalla mutane uku a kudancin Lebanon a lokacin wasu hare-haren sama daban-daban bayan sun yi barazanar sake ci gaba da kai muggan hare-hare kan kasar.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar lafiya ta Lebanon ta fitar ta ce wani “harin makiya ” a yankin Yater, a kudancin kasar, ya kashe mutum daya tare da raunata wani.
A wani bangare kuma, wani harin Isra’ilar da aka kai kan wata mota shi ma ya kashe wani mutum a tsakanin garuruwan Safad al-Batikh da Barashit.
A lokaci guda kuma, an kashe wani memba na majalisar birnin Jouaya, Tyre, bayan wani hari da Isra’ila ta kai kan garin.
Ministan yakin Isra’ila, Israel Katz, a karshen watan da ya gabata, ya yi gargadin cewa Tel Aviv ta shirya kaddamar da sabon yaki kan Lebanon idan kungiyar Hezbollah ba ta mika makamanta ba kafin karshen shekarar nan ta 2025.
Lebanon ta samu sakon gargadin daga bangarorin kasashen Larabawa da na kasa da kasa cewa Isra’ila na shirin kaddamar da wani babban hari kan kasar, in ji Ministan Harkokin Waje Youssef Raggi a ranar Juma’a.
M. Raggi ya ce Beirut na kara karfafa huldarta da kasashen yankin don “kare Lebanon daga duk wani hari.”
Babban sakataren kungiyar Hezbollah, Sheikh Naim Qassem, a wani jawabi da ya yi kwanan nan, ya yi alkawarin cewa kungiyar ba za ta taba ajiye makamanta ba, yana mai sukar shirin gwamnatin kasar wanda y ace Amurka da Isra’ila ne ke amfani da batun don matsa lamba kan kungiyar ta kwance damarar makamai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Firaministan Ostiraliya ya goyi bayan tsauraran dokokin mallakar bindiga bayan harin Sydney December 15, 2025 Burtaniya: Masu Kin Baki Da Musulmi Suna Kai Masu Hare-Hare December 14, 2025 Iran Ta Bukaci Mutanen Yemen Su Daina Kashe Juna December 14, 2025 Iran Tayi Tir Da Hare-Haren Sydney Na Kasar Austaralia December 14, 2025 Sudan: Makaman ‘Drones’ Sun Kashe Ma’aikatan MDD 6 A Kadugli Na Kurdufan Ta Kudu December 14, 2025 Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD) December 14, 2025 َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja December 14, 2025 Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha December 14, 2025 Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan. December 14, 2025 Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai December 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci