UNRWA ta bukaci Isra’ila da ta bari a shigar da kayan agaji a Gaza
Published: 11th, March 2025 GMT
UNRWA ta yi kira ga Isra’ila da ta kawo karshen hana shigar da kayan agaji a zirin Gaza domin dakile bazuwar yunwa da wahala a yankin.
“Mun riga mun ga alamun farko na karin farashi a kasuwa,” in ji Kwamishinan UNRWA Philippe Lazzarini yayin taron manema labarai a wannan Litinin, ya kara da cewa yayin da lokaci yake kara kurewa, tasirin haramcin yana karuwa a Gaza.
Lazzarini ya kara da cewa “akwai hadarin komawa ga yanayin da muka fuskanta watannin da suka gabata, game da kara yaduwar yunwa a tsakanin mutanen zirin Gaza sakamakon matakan da Isra’ila take dauka.
“Isra’ila” ta sanar da dakatar da isar da kayayyakin jin kai zuwa Gaza a ranar 2 ga Maris, tare da yin barazanar kara matsin lamba kan Hamas, yayin da bangaren ‘yan gwagwarmayar Falasdinu ya ki amincewa da shawarar Amurka na tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta farko, maimakon shiga mataki na biyu kamar yadda yarjejeniyar tanada tun daga farko.
A wani mataki na baya-bayan nan na kara matsa lamba kan al’ummar zirin Gaza, Ministan Makamashi na Isra’ila Eli Cohen ya sanar da cewa, ya rattaba hannu kan wata doka ta katse wutar lantarki a yankin Gaza daga ranar 9 ga Maris, yana mai jaddada cewa “Isra’ila za ta yi amfani da dukkan kayan aikinta wajen dawo da mutanen da aka yi garkuwa da su, da kuma tabbatar da kawo karshen samuwar Hamas a cikin Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana
Aƙalla mutum 12 sun mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata a wani turmutsutsu da ya faru yayin jarabawar ɗaukar aikin soja a Filin Wasa na El-Wak da ke Accra, babban birnin ƙasar Ghana.
Lamarin ya faru ne da safiyar Laraba, yayin da ɗaruruwan matasa masu neman aikin suka kutsa cikin filin wasan ba tare da bin tsarin shiga da aka tanada ba.
An gano motar da aka sace a Gidan Gwamnatin Kano Gasar Kofin Duniya ta 2026 ita ce ta ƙarshe da zan buga — RonaldoRundunar Tsaron Ghana (GAF) ta ce mutum shida ne suka mutu a farko, amma rahotanni daga asibitin sojoji sun tabbatar da cewar adadin mamatan ya ƙaru zuwa mutum 12.
Wasu mutum 22 sun jikkata, ciki har da biyar da ke cikin mawuyacin hali, kamar yadda jami’ar asibitin sojojin ƙasar ta tabbatar.
Ministan Tsaro, Dokta Cassiel Ato Forson, ya ce an dakatar da ɗaukar na wani ɗan lokaci tare da kafa kwamiti domin binciken musabbabin lamarin, wanda ta bayyana a matsayin abin takaici.
Shugaban ƙasar, John Mahama, ya kai ziyarar jaje ga iyalan waɗanda suka mutu da kuma marasa lafiya, inda ya bayyana cewa gwamnati za ta ɗauki matakan tabbatar da cewa irin wannan lamari ba zai sake faruwa ba.
Rundunar Tsaron Ghana ta miƙa sakon ta’aziyya ga iyalan da abin ya shafa tare da tabbatar da cewa ana ci gaba da kula da waɗanda suka jikkata a asibitin sojoji.