HausaTv:
2025-03-18@01:19:40 GMT

UNRWA ta bukaci Isra’ila da ta bari a shigar da kayan agaji a Gaza

Published: 11th, March 2025 GMT

UNRWA ta yi kira ga Isra’ila da ta kawo karshen hana shigar da kayan agaji a zirin Gaza domin dakile bazuwar yunwa da wahala a yankin.

“Mun riga mun ga alamun farko na karin farashi a kasuwa,” in ji Kwamishinan UNRWA Philippe Lazzarini yayin taron manema labarai a wannan Litinin, ya kara da cewa yayin da lokaci yake kara kurewa, tasirin haramcin yana karuwa a Gaza.

Lazzarini ya kara da cewa “akwai hadarin komawa ga yanayin da muka fuskanta watannin da suka gabata, game da kara yaduwar yunwa a tsakanin mutanen  zirin Gaza sakamakon matakan da Isra’ila take dauka.

“Isra’ila” ta sanar da dakatar da isar da kayayyakin jin kai zuwa Gaza a ranar 2 ga Maris, tare da yin barazanar kara matsin lamba kan Hamas, yayin da bangaren ‘yan gwagwarmayar  Falasdinu ya ki amincewa da shawarar Amurka na tsawaita yarjejeniyar tsagaita bude wuta ta farko, maimakon shiga mataki na biyu kamar yadda yarjejeniyar tanada tun daga farko.

A wani mataki na baya-bayan nan na kara matsa lamba kan al’ummar zirin Gaza, Ministan Makamashi na Isra’ila Eli Cohen ya sanar da cewa, ya rattaba hannu kan wata doka ta katse wutar lantarki a yankin Gaza daga ranar 9 ga Maris, yana mai jaddada cewa “Isra’ila za ta yi amfani da dukkan kayan aikinta wajen  dawo da mutanen da aka yi garkuwa da su, da kuma tabbatar da kawo karshen samuwar Hamas a cikin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi

Kwamandan dakarun kare juyin musulunci na Iran manjo  janar Salami wanda ya gabatar da jawabi a wurin tunawa da shahid Mahadi Bakiri a garin Tabriz ya bayyana cewa;; Babu yadda za ayi jamhuriyar musulunci ta Iran ta bude tattaunawa da Amurka a karkashin barazana, yana mai kara da cewa; yin gwawarmaya da jajurcewa a gaban masu girman kai da daga hanci, yana daga cikin muhimman koyarwar alkur’ani mai girma da kuma tsarin musulunci.

Manjo janar Salami ya kara da cewa; ta hanyar tsayin daka da dunkulewar al’umma wuri daya, za a kai ga samun nasara.

Haka nan ya kara da cewa; A tsawon shekaru 46 da su ka gabata, al’ummar Iran ta kasance a cikin fadaka wajen fuskantar duk wata barazana.

Bugu da kari kwamandan dakarun kare juyin juya halin musuluncin na Iran ya kuma ce; Makiyan jamhuriyar musulunci ta Iran masu kekashewar zukata ne, ba su aiki da mandiki, kuma ba su aiki da duk wata halayya ta ‘yan ta ‘yan adamtaka,abu daya tilo da su ka yi imani da shi, shi ne amfani da karfi.

Har ila yau, kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya yi ishara da halayyar HKI da Amurka a yakin Gaza, Lebanon, Syria, Yemen, Iraki da Afghanistan; yana mai kara da cewa; sun tabbatar da cewa, su masu karya alkawali ne, don haka batun tattaunawa da  wadannan makiyan  kuskure ne

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD ta bukaci masu ruwa da tsaki a Yemen da su kai zuciya nesa
  • Sojojin Sudan sun sanar da samun gagarumin ci gaba a tsakiyar Khartoum
  • Adadin Shahidan Falasdinawa A Gaza Ya Karu Da 14 A Jiya Lahadi Saboda Hare-Haren Sojojin HKI
  • Darajar Kasuwar Kayan Aikin Likitancin Kasar Sin Ta Kai Yuan Triliyan 1.35
  • Wasu sarakunan gargajiya na ta’ammali da ƙwayoyi — Obasanjo
  • Yadda za a girka ‘Kamoniya’
  • Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza
  • Salami: Makiyan Iran Ba Su San Wani Abu Ba Sai Karfi
  • Harin da Isra’ila ta kai ya kashe Falasdinawa 9 a arewacin Gaza
  • Faɗuwar farashin kayan abinci a watan azumi ta shammace mu – ‘Yan kasuwa