Aƙalla mutane 26 ne suka riga mu gida sakamakon ɓarkewar cutar Sanƙarau a wasu ƙananan hukumomi huɗu na Jihar Kebbi.
Da yake zantawa da manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar, Kwamishinan Lafiya, Yanusa Ismail, ya bayyana cewa an samu adadin mutane 248 da ake zargin sun kamu da cutar, inda daga cikin samfura 11 da aka gwada a ɗakin gwaje-gwaje, an tabbatar da cewa uku daga ciki kalau suke.
A cewar kwamishinan, ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Gwandu, Aleiro, da Jega, inda aka samu asarar rayuka 15 a Gwandu, shida a Jega, huɗu a Aleiro, ɗaya kuma a Argungu.
Ya ce an buɗe sansanonin keɓe waɗanda suka kamu, yayin da gwamnatin jihar ta soma ɗaukar matakan daƙile cutar ciki har da neman alluran rigakafin.
Kwamishinan ya gargaɗi jama’a game da shan magunguna da kansu, inda ya ce mutane su gaggauta zuwa asibiti mafi kusa domin yin gwaji a duk lokacin da ba su da lafiya don tabbatar da halin da suke ciki.
“Ya kamata mutane su guji yin barci a cikin ɗaki mai cunkoso. Su riƙa wanke hannayensu akai-akai bayan sun shiga bayan gida.
“Ya kamata su daina ziyartar sansanonin da aka keɓe marasa lafiyar kuma su tabbatar sun wanke ’ya’yan itatuwa da sauran kayan abinci kafin su ci don guje wa kamuwa da cutar Sanƙarau,” in ji shi.
Kwamishinan ya ce Gwamna Nasir Idris ya bayar da naira miliyan 30 domin siyan magunguna da sauran kayayyaki domin ɗaukar matakan daƙile cutar.
Sanƙarau wata cuta dai da ke janyo kumburi a wani rukuni na ƙwaƙwalwa ta kuma karya garkuwar ƙashin baya.
Alamomin cutar sun haɗa da sanƙarewar wuya, zazzaɓi mai zafi, rashin son haske, ruɗewa, ciwon kai da amai.
A bayan nan ne hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki uku zuwa huɗu.
Cikin jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa har da Kebbi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi Jihar Sakkwato Sanƙarau
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
Daga Usman Muhammad Zaria
Shugaban kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bukaci ma’aikatar kananan hukumomi ta jihar tabbatar da ganin cewa kananan hukumonin jihar 27 sun wallafa cikakken kundin kasafin kudadensu cikin zangon farko na sabuwar shekara.
Alhaji Aminu Zakari wanda shi ne wakilin mazabar Gwiwa, ya bayyana haka ne lokacin tantance kiyasin kasafin kudin sabuwar shekara na ma’aikatar kananan hukumomi.
Ya kuma yi kira ga ma’aikatar da ta duba batun rashin biyan albashi ga wasu daga cikin nadaddun kansiloli, kasancewar yanzu haka akwai nadaddun kansiloli 21 da ba sa samun albashin su.
Ya kara da cewar, kwamitin ya samu koke kan tsallake albashin wasu ma’aikatan kananan hukumomi sakamakon aikin tantance ma’aikata na IPPS ta yadda wasu ma’aikatan sun yi ritaya ba tare sun karbi albashin da aka tsallake su ba.
A nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar kananan hikumomin Jihar, Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa, ya bada tabbacin yin duk abinda ya kamata domin magance wadannan batutuwa.
Ya ce ma’aikatar ta yi kiyasin kashe naira miliyan dubu 13 domin gudanar da manyan ayyuka da harkokin yau da kullum a shekarar 2026.
Hannun Giwa, ya kuma bayyana cewar daga cikin manyan ayyuka akwai gyaran ofisoshin shiyya na jami’an duba kananan hukumomi guda 7.
Yana mai cewar za’a kuma kammala aikin ginin sabbin ofisoshi dake kananan hukumomin Babura da Kafin Hausa.
Kazalika, Kwamishinan ya ce za’a sayi motocin aiki da babura ga jami’an duba kananan hukimomi da mataimakansu, tare da kudaden gudanarwa domin ziyarar aiki a lungu da sakon kananan hukumomin jihar 27.