Aminiya:
2025-03-18@00:37:14 GMT

Sanƙarau ta kashe mutum 26 a Kebbi

Published: 11th, March 2025 GMT

Aƙalla mutane 26 ne suka riga mu gida sakamakon ɓarkewar cutar Sanƙarau a wasu ƙananan hukumomi huɗu na Jihar Kebbi.

Da yake zantawa da manema labarai a Birnin Kebbi, babban birnin jihar, Kwamishinan Lafiya, Yanusa Ismail, ya bayyana cewa an samu adadin mutane 248 da ake zargin sun kamu da cutar, inda daga cikin samfura 11 da aka gwada a ɗakin gwaje-gwaje, an tabbatar da cewa uku daga ciki kalau suke.

Ana fargabar ɓarkewar Sanƙarau a Sakkwato Lakurawa sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Kebbi

A cewar kwamishinan, ƙananan hukumomin da abin ya shafa sun haɗa da Gwandu, Aleiro, da Jega, inda aka samu asarar rayuka 15 a Gwandu, shida a Jega, huɗu a Aleiro, ɗaya kuma a Argungu.

Ya ce an buɗe sansanonin keɓe waɗanda suka kamu, yayin da gwamnatin jihar ta soma ɗaukar matakan daƙile cutar ciki har da neman alluran rigakafin.

Kwamishinan ya gargaɗi jama’a game da shan magunguna da kansu, inda ya ce mutane su gaggauta zuwa asibiti mafi kusa domin yin gwaji a duk lokacin da ba su da lafiya don tabbatar da halin da suke ciki.

“Ya kamata mutane su guji yin barci a cikin ɗaki mai cunkoso. Su riƙa wanke hannayensu akai-akai bayan sun shiga bayan gida.

“Ya kamata su daina ziyartar sansanonin da aka keɓe marasa lafiyar kuma su tabbatar sun wanke ’ya’yan itatuwa da sauran kayan abinci kafin su ci don guje wa kamuwa da cutar Sanƙarau,” in ji shi.

Kwamishinan ya ce Gwamna Nasir Idris ya bayar da naira miliyan 30 domin siyan magunguna da sauran kayayyaki domin ɗaukar matakan daƙile cutar.

Sanƙarau wata cuta dai da ke janyo kumburi a wani rukuni na ƙwaƙwalwa ta kuma karya garkuwar ƙashin baya.

Alamomin cutar sun haɗa da sanƙarewar wuya, zazzaɓi mai zafi, rashin son haske, ruɗewa, ciwon kai da amai.

A bayan nan ne hukumar kula da yanayi ta Nijeriya NiMet ta yi gargaɗin cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin ƙasar na tsawon kwanaki uku zuwa huɗu.

Cikin jihohin da aka yi hasashen za su fuskanci ƙaruwar yanayi na zafin rana sun haɗa har da Kebbi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi Jihar Sakkwato Sanƙarau

এছাড়াও পড়ুন:

Harin da Isra’ila ta kai ya kashe Falasdinawa 9 a arewacin Gaza

Rahotannin dake fitowa daga Falasdinu na cewa wani hari da Isra’ila ta kai a arewacin zirin Gaza ya kashe akalla Falasdinawa tara, ciki har da ‘yan jarida uku a cikin gida, in ji ma’aikatan lafiya.

An kai harin ta sama a wata mota a garin Beit Lahiya da ke arewacin zirin yau Asabar.

A cewar likitocin, mutane da dama sun samu munanan raunuka, tare da jikkata a ciki da wajen motar.

“An kai shahidai tara zuwa asibiti, da suka hada da ‘yan jarida da dama da ma’aikata daga kungiyar agaji ta Al-Khair, sakamakon harin da aka kai wa motar da wani jirgi mara matuki a garin Beit Lahia, tare da luguden wuta a yankin,” in ji kakakin hukumar tsaron farar hula Mahmoud Bassal.

Shaidu da sauran ‘yan jarida sun ce mutanen da ke cikin motar na wata kungiyar agaji ve a garin, kuma Sun samu rakiyar ‘yan jarida da masu daukar hoto lokacin da harin ya same su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [9]
  • Ba Don Tarbiyantar Da Mutane Nake Yin Fim Ba -Amina Shehu Lulu
  • An sanya dokar hana fita bayan kashe sabuwar amarya a Jigawa
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina
  • Fiye Da Mutane 20 Ne Su Ka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren  Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
  • Harin da Isra’ila ta kai ya kashe Falasdinawa 9 a arewacin Gaza
  • Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  •  Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
  • Zargi: ’Yan sanda sun musanta sace tsohon Kwamishinan El-Rufai
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [7]