Lakurawa sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Kebbi
Published: 11th, March 2025 GMT
Mayaƙan Lakurawa sun kashe mutum 13 a wani harin ramuwar gayya da suka kai yankin Birnin Debe da ke Ƙaramar Hukumar Arewa a Jihar Kebbi.
Wani mazauni mai suna Musa Gado, ya ce maharan wanda suka kai harin a ranar Lahadi, sun kuma ƙone ƙauyuka takwas daga cikin tara da ke yankin.
Tsohon shugaban Philippines ya faɗa komar ’yan sanda Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMetShi ma wani mazaunin yankin, Suleiman Abubakar wanda ya rasa ɗan uwansa ɗaya a dalilin harin, ya ce maharan sun auka wa ƙauyukan ne da yammaci bayan sallar Magariba.
“Abin ba a cewa komai domin mun ga tashin hankali. Sun kashe mutane da dama sun ƙone mana ƙauyuka kuma babu wanda suka ƙyale hatta mata da ƙananan yara.”
Aminiya ta ruwaito cewa, galibin waɗanda suka jikkata a dalilin harin yanzu haka suna samun kulawa a Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Birnin Kebbi.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Sani Aliyu, ya tabbatar da faruwar lamari da cewa tuni an tura ƙarin jami’an tsaro zuwa yankin yayin da gwamnatin ke ci gaba da ɗaukar mataki a kan lamarin.
Harin wanda ake zargin na ramuwar gayya ne na zuwa ne bayan wani farmakin haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da gwamnatin Kebbi, wanda ya yi sanadin mutuwar wani shugaban ’yan ta’addar Lakurawa da ake kira Maigemu.
Majiyoyin leƙen asiri sun tabbatar da cewa an kashe Maigemu a yankin Kuncin Baba da ke Arewacin jihar, bayan fafatawar da aka yi a ranar Alhamis ta makon jiya.
Da take martani, rundunar ’yan sandan jihar, ta ce mayaƙan Lakurawa ne suka kai harin a yankunan Birnin Debi, Dogon Daji, Danmarke, Yar Goru, Tambo, Garin Nagoro da kuma Garin Rugga da ke Arewacin jihar.
Rundunar ta ce mayaƙan ɗauke da muggan makamai sun kai hari a waɗannan yankunan da ke iyaka da Jamhuriyyar Nijar, inda suka kashe aƙalla mutum 11 yayin da wasu biyu suka jikkata.
Wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar ta ce maharan sun koma ƙone wasu gida ƙurmus a ƙauyukan da abin ya shafa.
Ana iya tuna cewa, a watan jiya na Fabarairu ne wasu ’yan ta’addan suka kashe wani mutum tare da jikkatar wasu shida a yayin harin da aka kai ƙauyen Gulman da ke Ƙaramar Hukumar Argungu ta Jihar Kebbi.
Kazalika, mayaƙan ake ɗora wa alhakin kashe wasu jami’an hukumar shige da fice biyu da wani farar hula ɗaya a Ƙaramar Hukumar Kangiwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi Lakurawa Ƙaramar Hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.
Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,
Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.
Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu
Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hadafitattun da za ta fuskanci kakar bana.
Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.
Raunin ‘yanwasa da ke jinyaRaunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.
Bayan Liberpool na yoyoA kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.
Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara
kakar nan.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA