Aminiya:
2025-05-01@00:53:50 GMT

Lakurawa sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Kebbi

Published: 11th, March 2025 GMT

Mayaƙan Lakurawa sun kashe mutum 13 a wani harin ramuwar gayya da suka kai yankin Birnin Debe da ke Ƙaramar Hukumar Arewa a Jihar Kebbi.

Wani mazauni mai suna Musa Gado, ya ce maharan wanda suka kai harin a ranar Lahadi, sun kuma ƙone ƙauyuka takwas daga cikin tara da ke yankin.

Tsohon shugaban Philippines ya faɗa komar ’yan sanda Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMet

Shi ma wani mazaunin yankin, Suleiman Abubakar wanda ya rasa ɗan uwansa ɗaya a dalilin harin, ya ce maharan sun auka wa ƙauyukan ne da yammaci bayan sallar Magariba.

“Abin ba a cewa komai domin mun ga tashin hankali. Sun kashe mutane da dama sun ƙone mana ƙauyuka kuma babu wanda suka ƙyale hatta mata da ƙananan yara.”

Aminiya ta ruwaito cewa, galibin waɗanda suka jikkata a dalilin harin yanzu haka suna samun kulawa a Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Birnin Kebbi.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Sani Aliyu, ya tabbatar da faruwar lamari da cewa tuni an tura ƙarin jami’an tsaro zuwa yankin yayin da gwamnatin ke ci gaba da ɗaukar mataki a kan lamarin.

Harin wanda ake zargin na ramuwar gayya ne na zuwa ne bayan wani farmakin haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da gwamnatin Kebbi, wanda ya yi sanadin mutuwar wani shugaban ’yan ta’addar Lakurawa da ake kira Maigemu.

Majiyoyin leƙen asiri sun tabbatar da cewa an kashe Maigemu a yankin Kuncin Baba da ke Arewacin jihar, bayan fafatawar da aka yi a ranar Alhamis ta makon jiya.

Da take martani, rundunar ’yan sandan jihar, ta ce mayaƙan Lakurawa ne suka kai harin a yankunan Birnin Debi, Dogon Daji, Danmarke, Yar Goru, Tambo, Garin Nagoro da kuma Garin Rugga da ke Arewacin jihar.

Rundunar ta ce mayaƙan ɗauke da muggan makamai sun kai hari a waɗannan yankunan da ke iyaka da Jamhuriyyar Nijar, inda suka kashe aƙalla mutum 11 yayin da wasu biyu suka jikkata.

Wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar ta ce maharan sun koma ƙone wasu gida ƙurmus a ƙauyukan da abin ya shafa.

Ana iya tuna cewa, a watan jiya na Fabarairu ne wasu ’yan ta’addan suka kashe wani mutum tare da jikkatar wasu shida a yayin harin da aka kai ƙauyen Gulman da ke Ƙaramar Hukumar Argungu ta Jihar Kebbi.

Kazalika, mayaƙan ake ɗora wa alhakin kashe wasu jami’an hukumar shige da fice biyu da wani farar hula ɗaya a Ƙaramar Hukumar Kangiwa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi Lakurawa Ƙaramar Hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta gano ma’aikatanta 240 da ke ƙarɓar albashi sau biyu a duk wata, da wasu 217 da ke amfani da lambar tantance asusun banki (BVN) guda ɗaya.

Wani mai magana da yawun gwamnati, Dakta Sulaiman Wali Sani, ya gaya wa manema labarai a ranar Lahadi cewa an gano wannan badaƙalar ce a yayin da ake tantance tsarin biyan albashin gwamnati.

Dr. Sani ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin biyan ma’aikata daidai kuma akan lokaci, kuma gano waɗannan matsalolin wani ɓangare ne na gyara al’amura.

Ya ce sun duba bayanan ma’aikata ta hanyar amfani da hotunan yatsa a matakin jiha da ƙananan hukumomi.

“Tsohuwar hanyar biyan mutane tana da matsaloli. Mun gano ma’aikata 240 suna karɓar albashi sau biyu kuma mutane 217 suna amfani da BVN ɗaya, wanda zai iya nufin akwai ma’aikatan bogi ko kuma mutane suna amfani da BVN na wani,” in ji Dakta Sani.

Ya kuma ce ma’aikata 1,335 ba su zo don a tantance su ba a tsawon fiye da watanni shida, wanda ya sa suke tunanin ko waɗannan mutanen da gaske suna aiki da gwamnati.

Alhaji Umar Idi, wanda ya duba biyan kuɗin ƙananan hukumomi, ya ce sun gano sunaye 247 da babu tabbaci a kansu. Waɗannan sun haɗa da mutanen da suka yi ritaya, waɗanda suka mutu, ko kuma waɗanda aka ci gaba da biyan su ba tare da izini ba bayan lokacin barinsu aiki.

“Daga cikin waɗannan ma’aikata 247, takwas ne kawai suka zo don tabbatar da cewa har yanzu suna aiki. Za a goge sauran sunaye 239, wanda zai rage wa gwamnati asarar naira miliyan 27 a duk wata,” in ji shi, yana mai cewa za a mayar da kuɗaɗen da aka samu ga asusun gwamnati.

Dakta Sani ya ce gwamnati ba ta ƙoƙarin hukunta kowa ba, kawai dai tana gyara tsarin ne don ma’aikata na gaske da ’yan fansho su ci gaba da karɓar haƙƙoƙinsu ba tare da wata matsala ko yanka ba bisa ƙa’ida ba.

“Tun lokacin da Gwamna Abba ya fara aiki, ya tabbatar da cewa ana biyan ma’aikatan gwamnati da ’yan fansho a kan lokaci, ba tare da ɓoyayyun cire-cire da aka riƙa yi a baya ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa yanzu da suke tsaftace tsarin biyan kuɗi, ma’aikata su yi tsammanin samun biyan kuɗi mafi inganci a gaba.

Gwamnati ta ce za ta ci gaba da magana da duk masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa an magance duk matsalolin kuma jama’a sun sake amincewa da ayyukan gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano