A yau Asabar ne aka gudanar da zama na biyu na taro na uku, na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC, a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing. Zaman da babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kasar, kana shugaban kwamitin kolin soja Xi Jinping ya halarta.

Albarkacin kasancewar yau ranar bikin mata ta kasa da kasa, a madadin tawagar shugabannin taron, zaman ya mika fatan alheri ga mata daga dukkan kabilu, da dukkan bangarorin kasar Sin, da mata na dukkan kasashen duniya.

Bugu da kari, rahoton ayyukan zaunannen kwamitin NPC ya nuna cewa, ana shirin bitar dokoki 34 a shekarar nan ta 2025, wadanda suka hada da samar da wata doka, don inganta hadin kai da ci gaban al’ummar kasar. Ban da hakan, zaunannen kwamitin NPC, zai kuma karfafa binciken kafa dokoki masu nasaba da fasahohin AI, da tattalin arzikin dijital da sauransu.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno

Dakarun Sojin Rundunar Operation Haɗin Kai, sun kashe ’yan ta’adda biyu a wani samame da suka kai yankin Shettimari da ke Ƙaramar Hukumar Konduga, a Jihar Borno.

Majiyoyi sun shaida cewa rundunar ta kai harin ne ƙarƙashin Operation Desert Sanity V da safiyar ranar Alhamis.

Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai

Wata majiyar soji ta ce, “Sojojin sun tare mayaƙan a kusa da inda suka ke shirin kai hari a yankin da misalin ƙarfe 1:20 na dare.”

Ya ƙara da cewa, “Sojojin sun yi nasarar daƙile ’yan ta’addan nan take, inda suka kashe biyu daga cikinsu yayin da wasu suka tsere.”

Bugu da ƙari, majiyar ta ce daga baya an gano wasu bama-bamai guda biyu da kuma wani gidan harsashi guda ɗaya mai ɗauke da harsasai 23 masu ɗangon 7.62mm x 39mm da ’yan ta’addan suka watsar yayin tserewa.

Majiyar ta ƙara da cewa, “Babu wanda ya mutu a cikin sojojin, sai dai daga baya tawagar sojojin sun ci gaba da aikinsu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Karatun Baya Dangane Da Tarihi Shi Ne Abun Da Ya Kamaci Japan
  • ’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno
  • Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Iran Zata Dauki Bakoncin Taro Dangane Da Kasar Afganistan Da Tsaron Yankin
  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa