A yau Asabar ne aka gudanar da zama na biyu na taro na uku, na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC, a babban dakin taron jama’a dake birnin Beijing. Zaman da babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kuma shugaban kasar, kana shugaban kwamitin kolin soja Xi Jinping ya halarta.

Albarkacin kasancewar yau ranar bikin mata ta kasa da kasa, a madadin tawagar shugabannin taron, zaman ya mika fatan alheri ga mata daga dukkan kabilu, da dukkan bangarorin kasar Sin, da mata na dukkan kasashen duniya.

Bugu da kari, rahoton ayyukan zaunannen kwamitin NPC ya nuna cewa, ana shirin bitar dokoki 34 a shekarar nan ta 2025, wadanda suka hada da samar da wata doka, don inganta hadin kai da ci gaban al’ummar kasar. Ban da hakan, zaunannen kwamitin NPC, zai kuma karfafa binciken kafa dokoki masu nasaba da fasahohin AI, da tattalin arzikin dijital da sauransu.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’

Ministan Harkokin Waje na Jamhuriyar Benin, Olushegun Adjadi Bakari, ya ce kimanin sojoji 200 daga Najeriya da Ivory Coast yanzu haka na cikin kasar shi a matsayin wani ɓangare na aikin tsaro don tallafa wa gwamnati.

Ƙaramar ƙasa ta Yammacin Afirka ta girgiza da yunƙurin juyin mulkin da bai yi nasara ba a ranar Lahadi, wanda ya sa Najeriya, Faransa da Ivory Coast suka tashi tsaye wajen goyon bayan gwamnatin farar hula.

Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa Ɗaliban Jami’ar Unijos 8 sun mutu a hatsarin mota

“A halin yanzu akwai kusan sojoji 200 da suka zo don ba da taimako ga rundunar tsaron Benin a cikin aikin sharewa da tsaftacewa,” in ji Olushegun Adjadi Bakari ga ’yan jarida a taron manema labarai da aka yi a Abuja ranar Alhamis.

Wata majiyar tsaro daga Ivory Coast ta ce Abidjan ta turo sojoji 50 a matsayin ɓangare na wannan aiki, inda ƙungiyar ECOWAS ta bayyana cewa za a haɗa da sojoji daga Ghana da Saliyo.

Najeriya ta ce sojojinta sun isa Benin tun ranar Lahadi. ECOWAS ba ta bayyana adadin sojojin da ake sa ran za su shiga ba.

Bakari ya ce lokacin da rundunar Benin ta nemi taimako, shirin juyin mulkin “ya riga ya yi wargaje.”

Ya ce sojojin Benin masu biyayya sun fatattaki harin farko, amma lamarin na buƙatar kulawa sosai don kauce wa asarar rayukan fararen hula.

“Mun nemi goyon bayan ’yan’uwa ba saboda rundunarmu ba za ta iya ba, amma saboda Shugaban Ƙasa bai so a yi asarar rayuka masu yawa ba.”

Ya ƙara da cewa kai hari kai tsaye zuwa sansanin masu juyin mulkin na iya haifar da zubar da jini mai yawa. “Shi ya sa Shugaba Patrice Talon ya nemi goyon bayan Jamhuriyar Tarayyar Najeriya.

“Rundunar Benin ta yi nasarar fatattakar wannan yunƙurin juyin mulki, amma haɗarin asarar rayuka da dama ya sa aka buƙaci martani na haɗin gwiwa.”

Ana ci gaba da tattaunawa kan ko sojojin tsaro na yankin za su ci gaba da zama na ɗan lokaci, amma Bakari ya ce duk wani mataki “za a ɗauka ne tare da haɗin gwiwar rundunar tsaro ta Benin, wadda ta nuna jarumta.”

Yadda Najeriya ta taimaka wa Benin — Tuggar

A taron ministocin ECOWAS da aka yi a Abuja, Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya ce saurin matakan diflomasiyya, na soja da na leƙen asiri tsakanin Najeriya da Benin ne ya taimaka wajen dakile juyin mulkin.

Tuggar ya ce lamarin ya nuna yadda za a iya kare dimokuraɗiyya idan ƙasashe makwabta suna sadarwa yadda ya kamata.

Ya ce, “Haɗin kai don tabbatar da cewa dimokuraɗiyya ta ci gaba da kasancewa a Benin ya yi nasara, kuma wannan misali ne na abin da ya kamata a yi duk lokacin da dimokuraɗiyya ke fuskantar barazana a yankinmu.”

A halin yanzu, kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa Pascal Tigri, wanda ake zargi da jagorantar juyin mulkin da bai yi nasara va, tare da abokan aikinsa suna buya a Togo.

A ranar Laraba, jami’an gwamnatin Benin suka shaida wa Reuters cewa shugaban juyin mulkin yana gudun hijira a Lome 2, unguwa a babban birnin Togo inda gidan shugaban ƙasar, Faure Gnassingbe yake.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Gwamnatin Jigawa Ta Kara Samar da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Buƙata ta Musamman
  • Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya
  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa
  • Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa
  • Majalisar Dattawa Ta Bawa Tunubu Damar Kai Sojoji Zuwa Kasar Benin
  • Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba