Leadership News Hausa:
2025-12-01@08:50:17 GMT

Ɗan Uwan Gwamnan Kano Da Malaman NNPP Sun Koma APC

Published: 8th, March 2025 GMT

Ɗan Uwan Gwamnan Kano Da Malaman NNPP Sun Koma APC

Haka nan, wasu manyan jiga-jigan NNPP daga ƙaramar hukumar Gwale, Mahmoud Salisu Gwale da Farouk Ahmed Gwale, su ma sun koma APC.

Sanata Barau ya tabbatarwa da al’ummar Nijeriya cewa kofa a buɗe take ga kowa.

“A matsayina na Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, ina yi wa kowa hidima. Ko da kai ɗan PDP ne, LP, Kwankwasiyya, ko wata jam’iyya, ina tare da kai.

Idan kana son shigowa APC, jam’iyyar jama’a, muna maraba da kai. Ƙara yawa, ƙara daɗi!” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barau Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano

Ana ci gaba da ta ƙaddama kan Naira dubu ɗari bakwai da hamsin da Jami’ar Amurka ta Maryam Abacha  (MAAUN) da ke Jihar Kano ta wajabta wa ɗalibanta da suka kammala karatu biya a matsayin kuɗin bikin yaye ɗalibai.

Jami’ar MAAUN ta sanya wa kowane ɗalibin da ya kammala karatu biyan Naira dubu ɗari bakwai da hamsin a matsayin kuɗin bikin yaye ɗalibai, kafin ta ba shi takardar shaidar kammala karatu da gabatar da bayanansa domin samun damar halartar aikin yi wa ƙasa hidima (NYSC).

Sai dai kuma, Hukumar Karɓar Ƙorafi ta Jihar Kano (PCACC) ta umarci iyayen ɗaliban cewa su dakata da biyan kuɗin har sai ta kammala bincike kan ƙorafin da suka gabatar mata a kan lamarin.

Sanarwar da Shugaban Sashen Ayyuka na PCACC, Salisu Saleh, ya fitar bayan samun ƙorafi daga iyayen ɗaliban, ta umarci hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN da ta jingine shirinta na riƙe takardar kammala karatun ɗaliban ko tura sunayensu domin shirye-shiryen NYSC, saboda rashin biyan kuɗin.

’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno

A gefe guda kuma, hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN ta dage a kan cewa, za ta gudanar da bikin yadda ta riga ta tsara, wanda bai gamsu ba ya tafi kotu.

Mai mallakar Jami’ar MAAUN, Farfesa Abubakar Adamu Gwarzo, ya shaida wa wakilinmu cewa jami’ar za ta gudanar da taron bikin yaye ɗaliban nata kamar yadda ta tsara a cikin wannan wata na Disamba, 2025.

Ya jaddada cewa jami’ar zaman kanta take, don haka tana da ikon sanya kuɗin bikin yaye ɗalibanta.

A cewarsa, kuɗin da MAAUN ta sanya bai kai abin da wata jami’a mai zaman kanta a Jihar ba ta sanya, amma bai ambaci suna ba. Don haka ya kalubalanci Hukumar kan rashin dakatar da biyan kuɗaɗen a ɗaya jami’ar ba.

Ya ce, “Za mu gudanar da bikin a watan Disamba a kamar yadda muka tsara, kuma za mu gayyaci ’yan jarida su ɗauki rahoto.”

Wata wasiƙar ƙorafi a madadin ɗalibai ta nuna damuwa kan yunƙurin tattaunawa da ɗalibai a ɗaiɗaikunsu domin neman ragin kuɗin da jami’ar ta sanya.

Ta bayyana cewa wannan ya saɓa wa abin da aka tsara cewa tattaunawar za ta ƙunshi iyayen ɗalibai da hukumomin jami’ar da kuma wakilan gwamnati.

A yayin da iyaye ke jiran samun tabbacin tsarin da aka yi a hukumance, hukumar gudanarwar Jami’ar MAAUN ta nace cewa babu gudu, babu ja da baya wajen gudanar da taron kamar yadda ta riga ta tsara — duk wanda bai gamsu ba ya tafi kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • N750,000 kuɗin bikin yaye ɗaliban Jami’ar MAAUN ya tayar da ƙura a Kano
  • Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe tsohuwa, sun sace mutum 3 a Kano
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku
  • Barau ya musanta zargin gwamnatin Kano, ya soki gwamna Abba
  • Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Yadda ’yan mata ke kufancewa da kasuwancin fara a Kano
  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali