Leadership News Hausa:
2025-12-14@13:23:40 GMT

Ɗan Uwan Gwamnan Kano Da Malaman NNPP Sun Koma APC

Published: 8th, March 2025 GMT

Ɗan Uwan Gwamnan Kano Da Malaman NNPP Sun Koma APC

Haka nan, wasu manyan jiga-jigan NNPP daga ƙaramar hukumar Gwale, Mahmoud Salisu Gwale da Farouk Ahmed Gwale, su ma sun koma APC.

Sanata Barau ya tabbatarwa da al’ummar Nijeriya cewa kofa a buɗe take ga kowa.

“A matsayina na Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, ina yi wa kowa hidima. Ko da kai ɗan PDP ne, LP, Kwankwasiyya, ko wata jam’iyya, ina tare da kai.

Idan kana son shigowa APC, jam’iyyar jama’a, muna maraba da kai. Ƙara yawa, ƙara daɗi!” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barau Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta

Gwamnatin Jihar Kano, ta haramta kafa Hukumar Hisbah mai zaman kanta tana, wadda tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje, yake ƙoƙarin kafawa.

Gwamnatin ta ce kafa hukumar ya saɓa da doka, kuma zai iya zama barazana ga zaman lafiya a jihar.

Zan yi amfani da Salah a wasan Liverpool da Brighton — Arn Slot Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago

A cikin wata takarda da Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya sanya hannu a ranar 8 ga watan Disamba, 2025, gwamnatin ta ce ta gano an fara ɗaukar mutane aiki a hukumar ba tare da neman izini ba.

Gwamnatin ta ce hakan ya saɓa wa Dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.

Da yake zantawa da ’yan jarida, Kwamishinan YaɗaLabarai da Harkokin Cikin Gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya ce Hukumar Hisbah ce kaɗai doka ta amince da ita wajen gudanar da ayyuka a jihar.

Ya ce kafa wata ƙungiya ko hukuma ta daban ba bisa ƙa’ida ba na iya kawo cikas ga zaman lafiya.

Umarnin ya bayyana cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ikon ɗaukar mutane aiki, tara su, horas da su ko tura su domin kafa wata hukumar Hisbah mai zaman kanta a jihar.

Gwamna Abba, ya kuma ayyana ayyukan hukumar a matsayin haramtattu, tare da gargaɗin cewa duk wanda ya yi amfani da kayan Hisbah, alamominta ko ikonta ba tare da izini ba zai fuskanci hukunci.

Gwamnan, ya umarci jami’an tsaro, ciki har da ’Yan Sanda, DSS, NSCDC, da sauran hukumomin tsaro, da su binciki waɗanda suka kafa sabuwar hukumar.

Gwamnatin ta kuma gargaɗi jama’a cewa duk wanda ya shiga, ya goyi baya ko ya haɗa kai da sabuwar hukumar, zai fuskanci hukunci.

An shawarci waɗanda aka ɗauka aiki su fice daga hukumar nan take tare da komawa ofishin Hisbah, ko Ƙaramar Hukuma.

Umarnin ya kuma tanadi hukunci ga waɗanda suka saɓa wa dokar, ciki har da gurfanar da su a gaban kotu bisa laifin gudanar da taro ba bisa ƙa’ida ba, kwaikwayon hukumomin gwamnati, da kafa rundunar tsaro ba tare da neman izini ba.

Wannan umarni ya fara aiki nan take, kuma za a yaɗa shi a kafofin watsa labarun Gwamnatin Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Gwamnatin Kano ta haramta kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Annabi SAW Ya Zarce Duk Sauran Annabawa Yawan Mu’uzijoji
  • ‘Sojojin Najeriya da na Ivory Coast 200 sun shiga domin tsaftace Jamhuriyar Benin’
  • Jam’iyyar PDP ta tabbatar da mutuwar mataimakin Gwamnan Bayelsa
  • Katsina Ta Amince Da Bayar Da Alawus Na Naira 30,000 Duk Wata Ga Malaman Karkara
  • Manchester United ta shiga zawarcin Sergio Ramos