HausaTv:
2025-06-26@08:34:06 GMT

Iran Da Iraki Sun Nuna Damuwa Kan Tashe-tahen Hankula A Siriya

Published: 8th, March 2025 GMT

Kasashen Iran da kuma Iraki sun nuna damuwa kan tashe tashen hankulan dake faruwa a Siriya.

A wata sanarwa da ta fita ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana matukar damuwarta kan yadda tashe-tashen hankulan da ke yaduwa a fadin kasar ta Siriya, tana mai gargadin cewa, wannan yanayi mara kyau zai share fagen rashin zaman lafiya a yankin da kuma kara tunzura Isra’ila.

Kakakin ma’aikatar Esmail Baghai ya bayyana cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran na nuna damuwa kan rashin tsaro, tashe-tashen hankula, zubar da jini da cutar da al’ummar Siriya da basu ji basu gani ba.

Ita ma ma’aikatar harkokin wajen kasar Iraki ta bayyana matukar damuwarta kan halin da ake ciki a makwabciyarta Syria, tana mai jaddada cewa karuwar tashe-tashen hankula a kasar Larabawar ka iya yin tasiri sosai ga tsaro da zaman lafiyar yankin.

A cikin wata sanarwa da ta fitar a Asabar din nan, ma’aikatar ta jaddada bukatar “kare fararen hula daga bala’in rikici.”tare da yin kira da a ba da fifiko wajen tattauna hanyoyin warware matsalar ta cikin lumana.

Sanarwar ta zo ne a daidai lokacin da wasu majiyoyi na cikin gida suka bayar da rahoton cewa, an gwabza kazamin fada tsakanin bangarorin da ke da alaka da gwamnatin Hayat Tahrir al-Sham (HTC) mai mulki da kuma ‘yan adawa masu biyayya ga tsohuwar gwamnatin, kusa da asibitin al-Watani da ke birnin As-Suwayda a kudu maso yammacin kasar Syria.

Kungiyar kare hakkin dan adam ta Syrian Observatory for Human Rights (SOHR) mai hedkwata a birnin Landan ta bayar da rahoto a jiya Juma’a cewa akalla mutane 237 ne aka kashe a yankin gabar tekun Syria tun bayan barkewar sabon tashin hankali a ranar Alhamis.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Eze ya gode wa waɗanda suka kafa ADA saboda ƙoƙarinsu na ceton Nijeriya daga hannun shugabannin da ba sa bin tsarin dimokuraɗiyya.

Ya ce sun nuna ƙwazo da ƙaunar ƙasa.

Ya ce, “Kun nuna bajinta da kishin ƙasa ta hanyar ƙoƙarin ƙwato mulki daga hannun shugabannin da suka haddasa rikice-rikice, garkuwa da mutane, talauci, yunwa da kunya ga ƙasar nan.”

Eze ya kuma yi addu’ar cewa Allah Ya taimaka musu su samu nasarar ceto Nijeriya daga hannun shugabanni marasa ƙwarewa da tausayi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa
  • Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO
  • PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta
  • Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
  • Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
  • Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
  • Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
  • Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran
  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
  • Amurka ta roƙi China ta sa baki kada Iran ta rufe mashigar tekun Hormuz