Leadership News Hausa:
2025-06-30@23:26:54 GMT

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Published: 8th, March 2025 GMT

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

5. Damfara da Alkawurra na Bogi: Wasu na bayar da alkawurran aure da ba su da gaskiya don cimma wasu burika nasu.

Yadda Za Ka Kare Kanka

• Ka guji aika hotuna na sirri ko bidiyo ga wanda ba ka sani sosai ba.

• Kar ka yarda da duk wani alkawari da ba ka tabbatar da gaskiyarsa ba.

• Ka duba asalin mutum kafin ka yi amanna dashi da bayanan ka.

• Yi taka-tsantsan da sakwannin da kake fitarwa a yanar gizo.

• Ka daina amfani da intanet wajen yin mu’amala da wanda ba ka da isasshen sani a kansa.

• Idan kana fuskantar barazana, ka sanar da hukuma ko wani da ka yarda da shi.

Labari Domin Karfafa Gwiwa

Maryam ta hadu da wani saurayi a Facebook, wanda ya yi alkawarin aure da ita. Sai dai, daga baya ya bukaci ta aika masa da hotuna na sirri. Maryam ta ki, amma daga baya ta gano cewa wannan mutumin yana cutar da mata da dama ta irin wannan hanya. Ta sanar da ‘yan sanda kuma hakan ya taimaka wajen kama shi. Wannan yana nuna cewa wayar da kai da taka-tsantsan yana da matukar muhimmanci.

Kammalawa

Soyayya a intanet na iya kasancewa da hadari idan ba a yi hankali ba. Mu kasance masu hankali da mutanen da muke hulda da su a yanar gizo. Kada a yarda da duk wanda ba mu san asalin sa ba, kuma mu iyaye sirrinmu.

Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Garkuwa Soyayya

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa Tace Za’a Maida Takunkuman Tattalin Arziki Kan Kasar Iran Idan Taki Yarda Da Yarjeniyar da Trump Yake

Gwamnatin kasar Faransa ta nawa JMI barazana kan cewa idan bata amince da yarjeniyan da Amurka take so ba to za’a sake dawo da takunkuman MDD a kanta.

Kamfanin dillancin labaran tasnim na kasar Iran ya nakalto ministan harkokin wajen kasar Faransa Jean-Noel Barrot yana fadar haka, ya kuma kara da cewa idan Iran ta ki ta rattaba hannu kan yarjeniyar da gwamnatin shugaba Trump yake so kan shirinta na makamashin Nukliya ba, abinda muke buklata kawai shi ne mu aika da wasika kan a dawoda takunkuman tattalin arziki kan kasar Iran, wadanda suka hada da na makamai, kudade, da kuma fasaha wadanda aka dagesu shekaru 10 da suka gabata.

Bayanda Amurka ta fice daga yarjeniyar JCPOA a shekara 2018 kasashen turai Faransa Burtaniya da Jamus suma sun ki su cika alkawulanda suka hau kansu a yarjeniyar donn goyon bayan Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
  • Magidanci ya kashe matarsa da adda a Yobe
  • Lebanon Ta Nuna Damuwarta Da Yiyuwar Yan Ta’adda Daga Siriya Su Kawo Hare-Hare Cikin Kasar
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa
  • Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki
  • 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
  • Faransa Tace Za’a Maida Takunkuman Tattalin Arziki Kan Kasar Iran Idan Taki Yarda Da Yarjeniyar da Trump Yake
  • Aminu Ɗantata: Na roƙi Allah kada Ya ba ni abin da mutane ba za su amfana ba
  • Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’