Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Published: 8th, March 2025 GMT
5. Damfara da Alkawurra na Bogi: Wasu na bayar da alkawurran aure da ba su da gaskiya don cimma wasu burika nasu.
Yadda Za Ka Kare Kanka
• Ka guji aika hotuna na sirri ko bidiyo ga wanda ba ka sani sosai ba.
• Kar ka yarda da duk wani alkawari da ba ka tabbatar da gaskiyarsa ba.
• Ka duba asalin mutum kafin ka yi amanna dashi da bayanan ka.
• Yi taka-tsantsan da sakwannin da kake fitarwa a yanar gizo.
• Ka daina amfani da intanet wajen yin mu’amala da wanda ba ka da isasshen sani a kansa.
• Idan kana fuskantar barazana, ka sanar da hukuma ko wani da ka yarda da shi.
Labari Domin Karfafa Gwiwa
Maryam ta hadu da wani saurayi a Facebook, wanda ya yi alkawarin aure da ita. Sai dai, daga baya ya bukaci ta aika masa da hotuna na sirri. Maryam ta ki, amma daga baya ta gano cewa wannan mutumin yana cutar da mata da dama ta irin wannan hanya. Ta sanar da ‘yan sanda kuma hakan ya taimaka wajen kama shi. Wannan yana nuna cewa wayar da kai da taka-tsantsan yana da matukar muhimmanci.
Kammalawa
Soyayya a intanet na iya kasancewa da hadari idan ba a yi hankali ba. Mu kasance masu hankali da mutanen da muke hulda da su a yanar gizo. Kada a yarda da duk wanda ba mu san asalin sa ba, kuma mu iyaye sirrinmu.
Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
Wani abin fashewa da ake zargin bam ne ya kashe aƙalla mutum 26, ciki har da mata da yara a kan hanyar Rann zuwa Gamboru Ngala da ke Jihar Borno.
Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Litinin a lokacin da motoci suka tayar da bama-baman da aka ɗana a gefen hanyar, da ya rutsa da maza 16 da mata huɗu da ƙananan yara guda shida.
Ta yi wa saurayinta ƙaryar shekarunta 27 maimakon 47 An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalMajiyoyi, ciki har da wani babba soja, sun tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu da harin na baya bayan da safiyar ranar Talata.
Sun bayyana cewa waɗanda lamarin ya rutsa da su suna kan hanyarsu ta tafiya Gamboru Ngala ne daga Rann lokacin da suka isa inda ‘yan ta’addan Boko Haram suka ɗana bam ɗin.
Bayanai sun ce baya ga mutum 26 da suka mutu, ƙarin mutum uku sun ji munanan raunuka.
“Mun tura wasu masu ba da agajin gaggawa inda lamarin ya auku domin kwashe mutane tare da tabbatar da tsaron sauran fararen-hula a wurin,” kamar yadda wata majiyar sojin da ba ta yarda a bayyana sunanta ba ta shaida wa Anadolu.
Ali Abass, wani ganau wanda ke tafiya a kan hanyar a lokacin da lamarin ya auku, ya ce sojojin da ‘yan sa-kai sun kai waɗanda suka jikkata wani asibiti. Ya ƙara da cewa ɗaya daga cikin ‘yan’uwansa na cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Harin yana zuwa ne yayin da hare-hare ke ƙara ƙaruwa a yankin Tafkin Chadi, inda ‘yan ta’addan Boko Haram ke ƙara ƙaddamar da hare-haren bama-bamai da kwanton-ɓauna kan motocin fararen-hula da na sojoji.
An ba da rahoton hare-hare irin wannan a ranakun 21 ga watan Maris da 12 ga watan Afrilu. Kawo safiyar ranar Talata dai, jami’an tsaro a Borno ba su fitar da wata sanarwa a hukumance game da lamarin ba.