Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Published: 8th, March 2025 GMT
5. Damfara da Alkawurra na Bogi: Wasu na bayar da alkawurran aure da ba su da gaskiya don cimma wasu burika nasu.
Yadda Za Ka Kare Kanka
• Ka guji aika hotuna na sirri ko bidiyo ga wanda ba ka sani sosai ba.
• Kar ka yarda da duk wani alkawari da ba ka tabbatar da gaskiyarsa ba.
• Ka duba asalin mutum kafin ka yi amanna dashi da bayanan ka.
• Yi taka-tsantsan da sakwannin da kake fitarwa a yanar gizo.
• Ka daina amfani da intanet wajen yin mu’amala da wanda ba ka da isasshen sani a kansa.
• Idan kana fuskantar barazana, ka sanar da hukuma ko wani da ka yarda da shi.
Labari Domin Karfafa Gwiwa
Maryam ta hadu da wani saurayi a Facebook, wanda ya yi alkawarin aure da ita. Sai dai, daga baya ya bukaci ta aika masa da hotuna na sirri. Maryam ta ki, amma daga baya ta gano cewa wannan mutumin yana cutar da mata da dama ta irin wannan hanya. Ta sanar da ‘yan sanda kuma hakan ya taimaka wajen kama shi. Wannan yana nuna cewa wayar da kai da taka-tsantsan yana da matukar muhimmanci.
Kammalawa
Soyayya a intanet na iya kasancewa da hadari idan ba a yi hankali ba. Mu kasance masu hankali da mutanen da muke hulda da su a yanar gizo. Kada a yarda da duk wanda ba mu san asalin sa ba, kuma mu iyaye sirrinmu.
Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume
Sanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ce Najeriya na iya ajiye biliyoyin naira a duk shekara idan aka rungumi tsarin majalisa ta wucin gadi.
Yayin da yake magana a gidan talabijin na Channels ranar Alhamis, Ndume ya ce kuɗin da ake kashewa wajen kula da Majalisar Dokoki a tsarin zama kodayaushe ba zai dore ba, musamman a wannan lokaci da ƙasar ke fama da matsalolin kuɗi da tsaro.
An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra“Kudin gudanar da gwamnati ya yi yawa sosai. Idan ’yan majalisa suka zauna na wucin gadi, gwamnati za ta ajiye biliyoyi,” in ji shi.
Ya ce za a iya sauya akalar kuɗin zuwa bangaren tsaro da sauran muhimman abubuwan ƙasa.
Ndume ya danganta tsadar gudanar da gwamnati da manyan ƙalubale da ke hana ƙasar yin nasara wajen yaki da rashin tsaro.
Ya ce Najeriya ba za ta iya jure ɓarnar kashe kuɗi ba a yayin da ake fuskantar ta’addanci a Arewa maso Gabas, ’yan bindiga a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya, garkuwa da mutane, da kuma ƙaruwar laifuka.
A wani bangare na fafutukar rage kashe kuɗi, sanatan ya soki ci gaba da kasancewar ’yan sanda da ke tare da sanataci da sauran manyan mutane duk da umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na janye jami’an tsaro daga irin wannan aiki.
Aminiya ta rawaito cewa Shugaban Ƙasa ya umarci Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, da ya janye jami’an daga aikin kare manyan mutane ya kuma tura su zuwa fagen yaki da ta’addanci da samar da tsaro.
“Amma har yanzu, ’yan siyasa na tare da ’yan sanda,” in ji Ndume, yana kira ga Babban Sufeton da ya tabbatar da cikakken bin umarnin na shugaban ƙasa.
Ya bayyana cewa tura ’yan sanda daga aikin kare manyan mutane zuwa aikin al’umma da na fagen yaki zai ƙara inganta tsaron ƙasa fiye da ɗaure su ga mutum ɗaya.
Ndume ya ce tsarin tsaron ƙasa ya yi ƙunci kuma yana bukatar “haɗa hannaye wajen yin aiki,” yana mai jaddada cewa dubban jami’an suna makale wajen rakiyar ’yan siyasa da masu tasiri waɗanda za su iya rayuwa ba tare da irin wannan rakiyar ba.