Leadership News Hausa:
2025-03-28@09:10:01 GMT

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Published: 8th, March 2025 GMT

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

5. Damfara da Alkawurra na Bogi: Wasu na bayar da alkawurran aure da ba su da gaskiya don cimma wasu burika nasu.

Yadda Za Ka Kare Kanka

• Ka guji aika hotuna na sirri ko bidiyo ga wanda ba ka sani sosai ba.

• Kar ka yarda da duk wani alkawari da ba ka tabbatar da gaskiyarsa ba.

• Ka duba asalin mutum kafin ka yi amanna dashi da bayanan ka.

• Yi taka-tsantsan da sakwannin da kake fitarwa a yanar gizo.

• Ka daina amfani da intanet wajen yin mu’amala da wanda ba ka da isasshen sani a kansa.

• Idan kana fuskantar barazana, ka sanar da hukuma ko wani da ka yarda da shi.

Labari Domin Karfafa Gwiwa

Maryam ta hadu da wani saurayi a Facebook, wanda ya yi alkawarin aure da ita. Sai dai, daga baya ya bukaci ta aika masa da hotuna na sirri. Maryam ta ki, amma daga baya ta gano cewa wannan mutumin yana cutar da mata da dama ta irin wannan hanya. Ta sanar da ‘yan sanda kuma hakan ya taimaka wajen kama shi. Wannan yana nuna cewa wayar da kai da taka-tsantsan yana da matukar muhimmanci.

Kammalawa

Soyayya a intanet na iya kasancewa da hadari idan ba a yi hankali ba. Mu kasance masu hankali da mutanen da muke hulda da su a yanar gizo. Kada a yarda da duk wanda ba mu san asalin sa ba, kuma mu iyaye sirrinmu.

Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Garkuwa Soyayya

এছাড়াও পড়ুন:

Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya

A Jamhuriyar Nijar, an daga martabar Abdourahmane Tiani madugun juyin mulkin sojin kasar daga mukamin Birgediya Janar zuwa Janar, mukamin soji mafi girma a kasar.

An ba Abdourahmane Tiani wannan mukamin ne bayan tabbatar masa da mukamin shugaban rikon kwarya na kasar a bikin da aka gudanar a jiya Laraba a Yamai babban birrin kasar.

Kafin hakan kuma Janar Abdourahamane Tiani, ya sa hannu kan dokar tsarin mulki na wucin gadi, mai taken “Tsarin farfado da Nijar”.

Bisa wannan doka, Tiani zai jagoranci kasar tsawon shekaru 5 tun daga ranar kaddamar da dokar, yayin da ainihin wa’adinta zai danganta da halin tsaro, da bukatun farfadowar kasar, da kuma ajandar kawancen kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso.

Hukumomin wucin gadin sun kunshi shugaban jamhuriyar Nijar, da kwamiti mai kula da harkokin tsaron kasar, da gwamnati da kwamitin sulhu, da hukumar sa ido kan harkar jin kai da sauransu. 

Wata dokar kuma da shugaban rikon kwaryar ya sanya wa hannu a jiya ita ce ta rusa dukkanin jam’iyyun siyasa a duk fadin kasar.

An amince da wannan sabon tsarin mulki ne bisa kudurorin da aka tattara, a yayin taron farfado da kasa da aka gudanar a tsakanin ranakun 15 zuwa 19 ga watan da ya gabata a birnin Yamai, fadar mulkin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [20]
  • Majalisa ta buƙaci a rage kuɗin data don sauƙaƙa wa ’yan Najeriya 
  • Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]
  •  Nigeria: An  Kashe Sojoji Da DAma A Wani Hari Da Aka Kai Wa Sansanonin Soja Biyu Hari A Jihar Borno
  • Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4
  • Boko Haram Ta Kashe Sojoji A Wani Sabon Hari A Borno
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]
  • Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI