Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Published: 8th, March 2025 GMT
5. Damfara da Alkawurra na Bogi: Wasu na bayar da alkawurran aure da ba su da gaskiya don cimma wasu burika nasu.
Yadda Za Ka Kare Kanka
• Ka guji aika hotuna na sirri ko bidiyo ga wanda ba ka sani sosai ba.
• Kar ka yarda da duk wani alkawari da ba ka tabbatar da gaskiyarsa ba.
• Ka duba asalin mutum kafin ka yi amanna dashi da bayanan ka.
• Yi taka-tsantsan da sakwannin da kake fitarwa a yanar gizo.
• Ka daina amfani da intanet wajen yin mu’amala da wanda ba ka da isasshen sani a kansa.
• Idan kana fuskantar barazana, ka sanar da hukuma ko wani da ka yarda da shi.
Labari Domin Karfafa Gwiwa
Maryam ta hadu da wani saurayi a Facebook, wanda ya yi alkawarin aure da ita. Sai dai, daga baya ya bukaci ta aika masa da hotuna na sirri. Maryam ta ki, amma daga baya ta gano cewa wannan mutumin yana cutar da mata da dama ta irin wannan hanya. Ta sanar da ‘yan sanda kuma hakan ya taimaka wajen kama shi. Wannan yana nuna cewa wayar da kai da taka-tsantsan yana da matukar muhimmanci.
Kammalawa
Soyayya a intanet na iya kasancewa da hadari idan ba a yi hankali ba. Mu kasance masu hankali da mutanen da muke hulda da su a yanar gizo. Kada a yarda da duk wanda ba mu san asalin sa ba, kuma mu iyaye sirrinmu.
Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
A yayin da ake tsaka da bikin Ranar Dimokradiyya a Najeriya, al’ummar jihar Gombe sun wayi gari da sabuwar dokar takaita zirga-zirgar babura daga ƙarfe 7:00 na yamma zuwa ƙarfe 6:00 na safe a duk faɗin jihar.
Sanarwar da ta fito ne daga hannun Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta jihar, DSP Buhari Abdullahi, ranar Alhamis, a madadin kwamishinan ’yan sandan jihar Bello Yahaya.
Sanarwar ta ce an kafa dokar ne don rage ayyukan ta’addanci a fadin jihar.
Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a FilatoKafa dokar na zuwa ne kwana uku bayan wasu matasa da ba a tantance su wane ne ba suka kashe wani magidanci mai suna Ahmad Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe, a daren Lahadi.
Sanarwar ta ƙara da cewa duk wanda aka kama ya karya dokar zai fuskanci hukunci mai tsauri, ciki har da gurfanar da shi a gaban kotu.
Kazalika, sanarwar ta ce dokar ta haramta ɗaukar mutum fiye da ɗaya a kan babur domin rage matsalar rashin tsaro a jihar.
“Dokar hana hawa babur da goyon biyu ta fara aiki ne daga yau, Alhamis, ranar bikin Dimokradiyya, har sai wani lokaci da ba a kayyade ba,” in ji Kakakin ’yan sandan.
Rundunar ’yan sandan ta ce an ɗauki wannan mataki ne don magance matsalar bata-gari na ‘’yan kalare’ da sauran ayyukan ta’addanci.
A lokacin da wakilinmu ya kai ziyara kwaryar birnin Gombe, filin wasa na Pantami ya kasance a rufe ba tare da alamar wani biki ba.
Sai dai ya gane wa idanunsa cewa an jibge jami’an tsaro a sassa daban-daban, ciki har da ’yan sanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da kuma ’yan banga.
Wannan sabuwar doka ta ja hankalin mutane da dama a jihar, musamman mazauna yankunan da aka fi samun matsalar tsaro.
Sai dai wasu na gani za ta kara jefa jihar cikin kuncin talauci sakamakon rufe shaguna da kasuwanni da wuri saboda rashin abun hawa wanda dama can baburan aka fi hawa saboda tsadar rayuwa.