Leadership News Hausa:
2025-12-11@20:00:51 GMT

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Published: 8th, March 2025 GMT

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

5. Damfara da Alkawurra na Bogi: Wasu na bayar da alkawurran aure da ba su da gaskiya don cimma wasu burika nasu.

Yadda Za Ka Kare Kanka

• Ka guji aika hotuna na sirri ko bidiyo ga wanda ba ka sani sosai ba.

• Kar ka yarda da duk wani alkawari da ba ka tabbatar da gaskiyarsa ba.

• Ka duba asalin mutum kafin ka yi amanna dashi da bayanan ka.

• Yi taka-tsantsan da sakwannin da kake fitarwa a yanar gizo.

• Ka daina amfani da intanet wajen yin mu’amala da wanda ba ka da isasshen sani a kansa.

• Idan kana fuskantar barazana, ka sanar da hukuma ko wani da ka yarda da shi.

Labari Domin Karfafa Gwiwa

Maryam ta hadu da wani saurayi a Facebook, wanda ya yi alkawarin aure da ita. Sai dai, daga baya ya bukaci ta aika masa da hotuna na sirri. Maryam ta ki, amma daga baya ta gano cewa wannan mutumin yana cutar da mata da dama ta irin wannan hanya. Ta sanar da ‘yan sanda kuma hakan ya taimaka wajen kama shi. Wannan yana nuna cewa wayar da kai da taka-tsantsan yana da matukar muhimmanci.

Kammalawa

Soyayya a intanet na iya kasancewa da hadari idan ba a yi hankali ba. Mu kasance masu hankali da mutanen da muke hulda da su a yanar gizo. Kada a yarda da duk wanda ba mu san asalin sa ba, kuma mu iyaye sirrinmu.

Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Garkuwa Soyayya

এছাড়াও পড়ুন:

An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya

Aƙalla ’yan Najeriya 32 ne aka koro su daga Indiya kan zargin su da hannu a kasuwancin miyagun ƙwayoyi.

A ƙarshen watan da ya gabata, ’yan sandan Delhi da na Telangana, sun kama ’yan Najeriya 50 biyo bayan samamen da suma kai wa wata ƙungiyar safarar miyagun ƙwayoyi mai alaƙa da ƙasashen waje.

Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC

Ana zargin mutanen da rarraba ƙwayoyi a birane da dama a Indiya, inda suke amfani da kamfanonin bayar da kaya don ɓoye ƙwayoyin da suke safara.

An gano mutanen suna da alaƙa da wani ɗan Najeriya mai suna “Nick,” wanda ake nema ruwa a jallo, kuma ana zargin yana jagorantar wannan ƙungiyar daga Najeriya.

Wasu majoyi sun bayyana cewa yana da abokan aiki aƙalla 100 a Delhi.

Masu bincike sun ce ƙungiyar tana da waɗanda ke aiki a ƙarƙashinta sama da 3,000 a Indiya kuma tana aika manyan kuɗaɗe zuwa Najeriya.

Daga cikin waɗanda aka kama, an koro ’yan Najeriya 32, yayin da wasu bakwai ke fuskantar tuhumar shari’a.

Hukumomi a ƙasar sun ana ci gaba da ce bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babbar Kasuwar Fim Ta Sin Babbar Damar Nollywood Ce
  • An koro ’yan Najeriya 32 kan kasuwancin miyagun ƙwayoyi a Indiya
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky
  • An kama wani mutum a Abuja yana ƙoƙarin kai harsasai ga ’yan bindiga a Zamfara
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Matsalar rashin tsaro ce ta sa na yi waqar “Arewa”-SKD Arewa
  • ‘Yan Bindiga 18 Sun Muta a Wata Arangama da Rundunar Operation Fansan Yamma