Leadership News Hausa:
2025-11-25@01:52:10 GMT

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

Published: 8th, March 2025 GMT

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

5. Damfara da Alkawurra na Bogi: Wasu na bayar da alkawurran aure da ba su da gaskiya don cimma wasu burika nasu.

Yadda Za Ka Kare Kanka

• Ka guji aika hotuna na sirri ko bidiyo ga wanda ba ka sani sosai ba.

• Kar ka yarda da duk wani alkawari da ba ka tabbatar da gaskiyarsa ba.

• Ka duba asalin mutum kafin ka yi amanna dashi da bayanan ka.

• Yi taka-tsantsan da sakwannin da kake fitarwa a yanar gizo.

• Ka daina amfani da intanet wajen yin mu’amala da wanda ba ka da isasshen sani a kansa.

• Idan kana fuskantar barazana, ka sanar da hukuma ko wani da ka yarda da shi.

Labari Domin Karfafa Gwiwa

Maryam ta hadu da wani saurayi a Facebook, wanda ya yi alkawarin aure da ita. Sai dai, daga baya ya bukaci ta aika masa da hotuna na sirri. Maryam ta ki, amma daga baya ta gano cewa wannan mutumin yana cutar da mata da dama ta irin wannan hanya. Ta sanar da ‘yan sanda kuma hakan ya taimaka wajen kama shi. Wannan yana nuna cewa wayar da kai da taka-tsantsan yana da matukar muhimmanci.

Kammalawa

Soyayya a intanet na iya kasancewa da hadari idan ba a yi hankali ba. Mu kasance masu hankali da mutanen da muke hulda da su a yanar gizo. Kada a yarda da duk wanda ba mu san asalin sa ba, kuma mu iyaye sirrinmu.

Ku ci gaba da bibiyar wannan shafi don samun karin bayani kan yadda za a kare kai daga hatsarin intanet!

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Garkuwa Soyayya

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Janye ‘Yan Sanda Daga Tsaron Manyan Mutane, Ya Amince Da Daukar Sabbin 30,000

Shugaban kasan Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin janye jami’an ƴansanda dake gadi ko rakiyar manyan mutane domin mayar da su aikin tsaro.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar ya fitar Mr Bayo Onanuga, da yammacin wannan Lahadi, ya ce daga yanzu za’a rika tura jami’an ƴansanda ne gudanar da ayyukan ƙasa.

Tinubu ya bayar da umarnin ne yayin ganawar da ya yi da shugabannin tsaron ƙasar da suka haɗa da rundunar sojin sama, da na ƙasa da na ruwa da Darakta Janar na ma’aikatar tsaro ta DSS da kuma Sufeto Janar na ƴansanda Kayode Egbetokun.

Sanarwar ta ce, daga yanzu duk mutumin da ke son jami’an tsaro su yi gadinsa to ya nemi jami’an tsaron Nigeria Security and Civil Defence Corps.

Shugaban ƙasa ya ɗauki wannan mataki ne la’akari da cewa sassan Najeriya da dama, musamman a yankunan karkara ana fuskantar ƙarancin jami’ai ofisohin ƴansanda, lamarin da ke sanya wahalar sauye nauyin kare al’umma da aka ɗaura musu.

Tuni Shugaba Tinubu ya amince da ɗaukar ƙarin jami’an ƴan sanda 30,000, yayin da gwamnatin tarayya ta sanar da wani shirin haɗin gwiwa da jihohi don haɓaka cibiyoyin horar da  ƴan sanda a duk faɗin ƙasar.

Daga BELLO WAKILI 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi
  • Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool
  • Ɗaya daga cikin ’yan matan da ISWAP ta sace a Borno ta tsere
  • Yara 50 Da Aka Sace A Najeriya Sun Tsere Daga Hannun Barayin Daji
  • Umarnin janye ’yan sanda daga faɗin manyan mutane na iya zama magana kawai —Shehu Sani
  • Tinubu Ya Janye ‘Yan Sanda Daga Tsaron Manyan Mutane, Ya Amince Da Daukar Sabbin 30,000
  • Tinubu ya dakatar da ’yan sanda daga tsaron manyan mutane a Najeriya
  • ’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161
  • Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF