HausaTv:
2025-10-13@18:09:51 GMT

Mutum 7,000 Suka Mutu A Rikicin Gabashin Kwango Tun Daga Watan Janairu

Published: 25th, February 2025 GMT

Fiye da mutane 7,000 da yawancinsu fararen hula ne aka kashe a yankin gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango tun daga watan Janairu, in ji Firaminista Judith Suminwa Tuluka a ranar Litinin.

Mambobin kungiyar M23 da ke samun goyon bayan kasar Rwanda sun kwace iko da yankunan gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo masu arzikin ma’adinai da suka hada da manyan biranen Goma da Bukavu da ke gabashin kasar.

Firayim Minista Judith Suminwa Tuluka ta yi gargadin cewa, halin da ake ciki na tsaro a gabashin DRC ya kai matsayi mai daukar hankali, yayin da take jawabi ga kwamitin kare hakkin bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya a Geneva.

Ta ce mutanen da suka mutu sun hada da “fiye da gawarwaki 2,500 da aka binne ba a san ko su waye ba” kuma gawarwakin mutane 1,500 na nan a dakin ajiye gawa.

A cewar rahotannin Majalisar Dinkin Duniya, ‘yan kungiyar M23 dauke da makamai, wadanda ke samun goyon bayan sojojin Rwanda kimanin 4,000, suyka abkawa yankunan, lamarin da ya tilastawa dubban mutane tserewa daga yankin.

A baya-bayan nan ne dakarun M23 suka karbe iko da Bukavu, babban birnin lardin Kivu ta Kudu, bayan da suka kwace Goma, babban birnin lardin Kivu ta Arewa.

Firayim Ministan Kongo ya ce an kashe fiye da mutane 3,000 a Goma kadai.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

A cewar NEMA, mutane 135,764 ne suka rasa matsugunansu, yayin da 115 aka bayyana bacewarsu, yayin da wasu 826 suka samu raunuka sakamakon ambaliyar. Bugu da kari, gidaje 47,708 sun lalace, yayin da gonaki 62,653 suka lalace a fadin jihohin da abin ya shafa.

 

Hukumar ta kara da cewa, daga cikin wadanda abin ya shafa sun hada da yara 188,118, mata 125,307, maza 77,423, tsofaffi 18,866, da kuma nakasassu 2,418.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako October 13, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Isa Birnin Rome Don  Halartar Taron Tsaro Na Aqaba October 12, 2025 Manyan Labarai An Sauya Kwamishinan Ƴansandan Abuja Saboda Rashin Tsaro October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • An Wallafa Ra’ayoyin Shugaba Xi Kan Batutuwan Da Suka Shafi Mata Da Yara Cikin Karin Harsunan Waje
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Matasa 2 Sun Mutu Bayan Nutsewa A Rafi A Kano