Mutum 7,000 Suka Mutu A Rikicin Gabashin Kwango Tun Daga Watan Janairu
Published: 25th, February 2025 GMT
Fiye da mutane 7,000 da yawancinsu fararen hula ne aka kashe a yankin gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango tun daga watan Janairu, in ji Firaminista Judith Suminwa Tuluka a ranar Litinin.
Mambobin kungiyar M23 da ke samun goyon bayan kasar Rwanda sun kwace iko da yankunan gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo masu arzikin ma’adinai da suka hada da manyan biranen Goma da Bukavu da ke gabashin kasar.
Firayim Minista Judith Suminwa Tuluka ta yi gargadin cewa, halin da ake ciki na tsaro a gabashin DRC ya kai matsayi mai daukar hankali, yayin da take jawabi ga kwamitin kare hakkin bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya a Geneva.
Ta ce mutanen da suka mutu sun hada da “fiye da gawarwaki 2,500 da aka binne ba a san ko su waye ba” kuma gawarwakin mutane 1,500 na nan a dakin ajiye gawa.
A cewar rahotannin Majalisar Dinkin Duniya, ‘yan kungiyar M23 dauke da makamai, wadanda ke samun goyon bayan sojojin Rwanda kimanin 4,000, suyka abkawa yankunan, lamarin da ya tilastawa dubban mutane tserewa daga yankin.
A baya-bayan nan ne dakarun M23 suka karbe iko da Bukavu, babban birnin lardin Kivu ta Kudu, bayan da suka kwace Goma, babban birnin lardin Kivu ta Arewa.
Firayim Ministan Kongo ya ce an kashe fiye da mutane 3,000 a Goma kadai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.
M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.
Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.
Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”
Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.
Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.
Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.