Ministan harkokin wajen kasar Iran, ya bayyana cewa bai kamata a yi amfani da hakkin dan adam a matsayin abun matsin lamba na siyasa ko tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasashe ba.

Abbas Araghchi, ya bayyana hakan ne a zaman kwamitin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya, inda ya jaddada cewa, daya daga cikin manyan abubuwan da ke kawo cikas ga tabbatar da hakkin dan Adam a duniya shi ne amfani da matakan tilastawa kasashe.

Ya kara da cewa wadannan matakan suna da illa ga fararen hula kuma ba adalci ne ba ga marasa galihu kamar mata, yara, tsofaffi da masu nakasa.

Ministan harkokin wajen kasar Iran Seyyed Abbas Araghchi ya bayyana jin dadinsa a wannan zama inda Ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na daya daga cikin kasashen da suka assasa Majalisar Dinkin Duniya, a ko da yaushe tana mutunta daidaito da adalci a matakin koli. »

Araghchi ya bayyana cewa shekaru da dama da suka gabata al’ummar Iran na fuskantar manyan kalubale kamar takunkumin karya tattalin arziki da kuma ta’addanci, wadanda suka yi illa ga hakkokinsu na zamantakewa da tattalin arziki, To sai dai kuma a cewarsa duk da wadannan kalubale, Iran ta samu ci gaba mai ma’ana A tsarin Musulunci da mutuncin bil’adama, da inganta fannonin ilimi da kiwon lafiya da ‘yancin mata da ci gaban masana’antu da tattalin arziki.

Muna bukatar a gaggauta soke duk wani takunkumi, saboda ba wai kawai take hakkin bil’adama na al’ummar Iran ba ne, har ma da haifar da wahala ga miliyoyin mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede

“Iyakar kasa ba wai kawai yanki ne na tsaro ba. Yanki ne na al’adu; yanki ne na tarihi; haka nan ma yanki ne na tattalin arziki. Kula da shige da fice na da matukar amfani ga ci gabanmu. Wajibi ne Nijeriya ta zuba jari a kan kula da nau’in mutanen da take tacewa wajen shiga kasa da kuma irin mutanen da muke tacewa wajen fita daga kasa.

“Dole ne mu yi nazarin nau’in ayyukan da bakin-haure ke yi da kuma yadda suke shafar tattalin arzikinmu. Muna bukatar tsame mutanen da ke kawo cikas ga ci gabanmu”, in ji Babandede.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki October 31, 2025 Labarai Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida October 31, 2025 Labarai Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai